MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   85 / 144

252K to 255K   out of 431K words

da fara,a da alaman daga barci ta tashi lokacin gaishe ta muka fara tana murmushi ta zauna tare da fadin kun shigo.
Eh inji maryam tana kara gaida matar nima na gaida da ta tace jiya ai nayi mantuwa ban tabayi sunayen ku ba har kuka tafi.
Maryam ta gabatar mata da sunan ta sannan ni na biyo baya tace duk sunayen ku sunane masu dadi ko a addinance ana alfahari da wanan sunan.
Tace amarya zance ko khadija nayi murmushi tace da fatan aikin mu ya fara tun jiya dai cikin kunya nace gaskiya bai fara ba don maigidan bayanan yayi tafiya.
Ok lailai ashe akwai taro kuwa don ya kamata ki haddace lokacin dawowan mijin ki gida kafin nan da rabin awa ya zamanto lalai kina a cikin shiri bawai yazo ya samay ki a ya mutse ba har ya fahinci halin ki ne hakan.
Ya kamata ya samay ki a cikin kwalliya kina zaune falo kina dakon zuwa sa yana shigowa zaki mike a cikin naki irin sallon kina masa sannu da zuwa tare da karban jakkan hannun sa ko leda ko wani abu dai daya shigo dashi gidan a hannun sa kina mai sannu da zuwa da sauran maganganun jan hankali a gare ki.
Nayi mantuwa ban fada maki ba ya kamata ace shi yana waje gurin aiki ke kina gida akalla zaki kirashi cikin ko wani a wa daya kiji lafiyan shi da sauran su.
Har lokacin da zai dawo gidan wanan yana kara kawo shakuwa sosai tsakanin mata da miji don Allah ki kula khadija nace in sha Allahu anty.
Ina fatan dai kina hakan kaina na noke tare da fadin anty ni ba wani shakuwa na soyayya mukayi da maigidan ba sanan kuma yanzu bamu fi wata uku da aure ba dashi.
Maryam tace a cikin na hudu kuke fa yanzu khadija hararan ta nayi Anty Salbiya tace amma ko kin ban mamaki don duk macen da tai jami,a ai ya kamata tasan wanan koda kadan ne.
Aure wata kusan hudu khadija amma baki maida komai serious ba haka a hakan har zaki saci zuciyar mijin naki ina kina da kishiya ko ?
Maryam tace kwarai kuwa kuma buzuwa ce yar Niger ce ta asali don ko hausa bata ji sosai har yanzu Antyn tace ashe irin mu ce sai dai muna da banbanci sosai dasu yanayin mune kawai shigen iri daya dasu don su ma haka suke kamar larabawa ke din ma ai zubin ki baza a ce yar kasan nan bace idan an ganki don kin fi kama da yan kasar Ethopian sosai.
Nakan fada mata amma sai ta dauka zolaya ne nake mata No ba wasa gaskiya nima farko jiya da kuka shigo ban dauka ke hausa bace sai dai da yake ko a cikin hausawan mafi akasarin su ai kyawawa ne kula ne dai da basuyi da kansu yadda ya dace suyi.
Sai kiga mace haihuwa biyu ko uku sun jemay sun fita hayacin su kamar mai shekaru da yawa.
Naga kamar lokaci tafiyan ku yayi ina fatan yau zaki fara daga cikin abinda na koyar dake koda kadan ne don Allah nace in Allah ya yarda anty.
Sosai ta kara yi min yan nasihohi wanda hakan ba karamin tasiri yayi a zuciyana ba don a cikin hikima ta dinga fadakar dani abinda ya dace.
Mukai mata sallama zamu tafi ta dan tako muna har zuwa waje tana fadin gobe insha Allahu zan fadakar dake akan kishiya ko yadda zaki zauna da ita acikin salama don kin san yanzu anbar kinshin fili sai na boye.
Maryam ta amsa da wai banda wanan kishiyar na khadija mai kishin hauka anty bakiga ba fa yadda suke abinsu kirikiri ranan mun dawo daga unguwa kirikiri magani da wani abu muka samu yabe yabe a kofan shiga part din nan dai ta bata labarin abinda ya faru a gidan ranan.
Na dora da fada masu abinda na tono a karkashin gadon AA duk a ranan ko maryam sai a lokacin take ji tana yaba zurfin ciki irin nawa.
Ajiyan zuciya Anty Salbiya ta sauke tace to Allah ya kyauta anan kuma na dora da fada masu urin mafakin da nayi ranan akan Nafisa din wanda abin yake cina har yanzun a zuciyana.
Tace gaskiya sai kin dage da addua tare da yawaita irin su sadaka kyautata da sauran don kin san irin wanan abin ya taimakawa mutum ta ida bai zata ba.
A sanyaye na furta ina yi anty tace da hannun ki kike badaw ko sakawa kike ai maki dai nace cikin murmushi sakawa nake ai min tace shine matsalan mu ai.
Baki san adduan mutum da bakin sa yafi saurin kamawa ba haka kuma abinda kika bayar da hannun ki yafi saurin karbuwa a wurin biyan bukata.
Sauraren ta mukeyi a cikin fahintar abinda take fada muna din, maryan tace anty ai inda mutum zai samu irin wa yan nan mabukatan ne anan har ya basu shine ai.
Kai ta girgiza tana fadin baku dai nema ba maryam amma idan kuka je irin su madala ko maraba nan ma a cikin gwagwalada akwaisu.
Ba wai sai mu saki ba irin masu karamin karfi din nan duk zaku iya basu don ko suna bukata Allah yasan a inda yan amin suke.
Mun rabu da ita cikin farin ciki da kauna muka bar gidan ta wurin anty muka biya nan mukai sallah la,asar mukaci abinci sai dana dan huta na dauko waya na nakira shi.
Kamar kiran zai katse aka dauka da sallama na karba mai yace cikin wani murya a kasalan ce Deedar ya akayi ne ajiyan zuciya na sauke ta yadda har yajini nace dashi ba komai.
Nadai kiraka ne in ji lafiyan ka yace realy nace may ye kuma na mamaki don na kira ka yanzun kuma ?
Ai dole inyi mamaki yau ni Abdulsamad Deedar zata kira kodai kin yi kewan kayan ki ne tsakanin jiya da yau ?
A hasale nace ban sani ba na kashe wayan yana ta kiran layin nawa inaji naki dauka maryam da muka fito take fadin .
Wai wake ta kiranki ne haka kike rejecting din call haka nace kyale shi don Allah shi ai dama ba ai mashi abin kirki yafi son kowa ya zauna kamar yadda matan shi suke ko yaushe.
Ba zaki zauna ba kuwa da sannu zaki gyara komai koda ace ko basu koya ba ke zakici gaba da dasa mai naki akidar a zuciyar shi.
Tun hanya muka rabu yau ban koma school ba na kira driver na fada mai ba sai yazo ba na samu an rage min hanya na dawo gida.
Ina shiga gidan massage din shi na shigo min yana fada min yana saman hanya yanzu an jima kadan zasu iso insha Allahu.
Su nafisa na samu a falo na wuce ba tare dana gaida su ba suma kamar yadda basu min sannu da shigowa ba na wuce hanyar part dina kai tsaye na bude na shiga.
Sai da na canza kaya na fada kitchen tare da tunanen abinda zan girka mai yaci idan ya dawo din ruwa na dora na dauko garin alkama na fara tankadewa.
Na gama na gyara kayan miya fresh na wanke na ciro nama na yanka tare da dorawa akan wuta.
Allah da ikon sa har na karasa aiki basu shigo ba part din har na gyara komai yadda ya dace wanka nayi na shirya sai naji kawai in fara aiwatar da huduban mutane mana yau.
Iya gwargwado dai nasha nasihan zamatakewar rayuwa da fadakar wa ya kamata ni ma in fara amfani dashi hakana in kawar da duk wani nauyi da kunya a tare dani.
Turaren da Anty Salbiya ta bani na shafa na shirya a cikin wasu atamfa mai launin jan watau red colour da dan fari fari a cikin sa.
Skirts and blulawars ne dinkin shi sai dan kwalin dana daura na kawo shi gaba kadan na kara kallon kaina a mirrrow na fito tsab.
Har zan fita daga falon na koma na dauko chewagun mint na bare na saka a baki na direct falon gidan na nufa inda su nafisa suke zaune da tawagan ta a can barin hago inda dakin ta yake.
Wurin dayan set din na nufa tun fitowa na kowan su ya sako min ido caaa suna kallon ikon Allah don wanan shine karo na farko da na taba fitowa falon gidan na zauna tun shigowana gidan.
Zama nayi na dauki kafa na daya na dora saman daya ina taunan chewing gun din a hankali yana bada dan sauti mai kara .
Hankalina yana a wayan dake hannu na ina dakilar wayan ba tare da na kula kowa dake falon ba a lokacin su kuma basu daina kallona suna mamaki ba da tunanen abinda ya kawo nin falon a wanan lokacin.
Yar wurin Nafisa Ihisan ne tayo wurina da gudun ta ta fada min a jiki na dan zabura ina shafa kanta muryan Nafisa naji cikin wani irin kara tana fadin .
Ke, ke , ke kada ki fara ki taba min yarinyar ki kama mata kurwa na fada maki idan kina so ke ma sai ki dage ki haifi naki a gidan.
Ban kula ta ba kuma ban sake yarinyar ba muna magana da yare taiwa Samiha magana tazo ta dauko mata yar ta a wurina.
Samiha ta taso zukwai zukwai taja hannun yarinya ta figeta ta wuce da ita inda suke zaune uwar tace tauraruwa mai wutsiya ganin ki ba alheri ba.
Kin kulla ta nayi don kada ta rushe min plain din kada ya shigo ya samay mu muna fada ko minti biyar ba,ayi ba sai naji dirin motocin shi sun iso gidan.
Ba wanda ya kula daga cikin su da dawowan shi tun a cikin cotton na hango shi tafe ya sagale rigar shi ta sama a kafadan shi.
Mikewa nayi tsam daga inda nake na tare shi bayan ya karasa shigowa daga ciki din a lokacin na mike na nufe shi.
Aiko idanuwan su caa a kaina kamar su cinye ni danya a lokacin hugging nakai mashi tare da sunbatan shi ina mashi sannu da zuwa.
Sai ya rugumoni sosai zuwa jikin shi tare da fadin Miss you deedar wanan kyau da kika sha haka fa nace is for you ya kara kai min kiss shima a tsakiyan kaina.
Mutuwar eacin gadi tayi da kyat ta iya tataro courage din ta tace yau kuma wani karuwanci ne haka a fili ?
Komai dai jarabar mutun dole ya bari har ranan girkin shi yayi jakka shi na zuwa aiki driver ya shigo dashi na karba daga hannun driver din.
Na wuce gaba yana biye dani a bayan shi part din shi na nufa har lokacin banda Nafisan ba wanda ya iya wani kwakwaran motsi daga cikin su.
Ganin na doshi hanyar part din ta mike tsaye tare da fadin malama kya bari sai girkin ki kiyi wanan sallon karuwancin kauyen ko ?
Murmushi nayi ban tsaya ta kanta ba na haye sama abina na barsu a nan tace a hasale dashi.
Samad amma kana kallon takalar yarinyar nan shishigin ta yayi yawa a gidan nan girkin ma yanzu kokari kwacewa take nufin yi a gare ni ko may ?
Da mamaki ya kalle ta yace kamar ya zata ci girkin ki ina yau itace dani kuma time din karban ta yayi har ya shuda yana magana yana kallon agogon hannun shi.
May kaku nufi da maganar ka ina jiya baka kwana gida ba don haka ni ya kamata in karbe ka a yau ai.
Wai Nafisa ke wata irin mace ce da baki da lissafi a rayuwan ki ban fa son irin wanan rikicin kin ji na fada maki.
Amma ai kasan haka muka saba yi a baya dakai idan ka dawo daga tafiyan yanzun ne zaka canza muna tsarin ko may ?
Yace da kika ce ba yanzu ita taga tana iya bar maki nata waccen da kike magana wanan ko tasan right din ta.
Hannayen ta ta taba tare da fadin yau ko zanga yadda za a dulmuye ni ina ji ina gani tsuki yaja ya nufi saman abinshi ya barta nan.
A dakin ruwan wanka nake kokarin hada mashi a ban daki naji shigowan shi dakin ko da na fito yana tsaye a tsakar dakin yana kokarin sasauta nicktie din wuyan zai kwance.
Na fito daga ban daki takowa nayi inda yake na rike mai hannu karban cire mai tie din nayi ina kokarin cirewa sai kallon mamaki yake min yana wani lumshe ido
Ban san shigowan ta dakin ba sai ji nayi an bangaje ni ta baya da karfi sai da na fada saman jikin shi ya tallabe ni da hannun sa.
Tare da fadin kina hauka ne wai Nafisa may ya shigo dake dakin nan wanan lokaci haka ko kishi haukane wai ?
Mace baki son zaman lafiya ko yaushe sai dai ayi fitina shine gurin ki kin sani sarai ba lokacin ki bane yanzu don may zaki tayar wa mutane da hankali haka wai , ?
Zan nuna maku haukan da kake yawan kira min ne azzalumai kawai kuna ganin zaku juyani ne a gidan nan ne komai yadda muka saba idan ka dawo haka za a ba wanda ya isa ya canza min tsari na.
Hannuna na daga ina kokarin karasa cire mai tie din ta daga hannu zata kai min duka ne ko mari ya rike hannun ta da sauri tare da fadin.
Dukan ta zakiyi komay nace barta kin ci albarkancin cikin nan dake jikin ki da yau kin gane baki da wayo da nanuna maki tawa kalar haukan kin gani.
Don ni ban tsayawa fadan baki haka kanki zaki tsunta a waje eh lalai ba laifin ki bane wuri kika samu.
Gashi yanzu kirkiri a gabana kuna son ku dulmuye min hakki na macuta mayaudara ba irin Nafisa ake cuta a zauna lafiya ba.
Ciki kuma da kike maganar sa kokarina ne ya bani shi don ni ba juya bace mai ci takai masai kullun zufana ne kike gani don haka kada bakin bakin ki ya kara tofa zance akan cikin jikina.
Jan hannun ta yayi zuwa waje yana fadin ki koma kasa idan na sauko sai muyi magana amma ba nan ba a cikin hakkin wata.
Samad ni kake kora a dakin ka kan wanan kwailar karuwan yarinyar da ka dauko mai kama da matan titi.
Nafisa yace cikin wani irin tsawa ba ita dake gaban shi ba har ni sai da na kadu daga inda nake ina kallon su ya daga hannun kamar zai make ta sai kuma ya sauke yaja hannun ta zuwa wajw tana turjewa.
Sai zagi take zuba min na cin mutunci da tozarci na fallasa irin na tantiran kishiyoyi din nan suka fice daga dakin ajiyan zuciya na sauke ina binsu da kallo.
Abinda ya fara zuwa min a rai shine ashe wanan akidar ke nan sukewa Fati dole ne Fati ta kasa zama a gidan don wanan irin dabancin na Nafisa kishi da buzuwa sai basira da hankali sai kuma an daure.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Wanan novel fitar dashi cin amana ne karanta shi ba tare da biya ba rike hakkin wani ne akan ki don Allah yan uwa musulmai mu kula da hakkin wani akan mu.
Ki tuna wanan online novel ne kika saya ba booklet don haka ka,idar shi ki karanta ki barshi nan kiyi tunanen wanan maganan yar uwa dubara ya saura ga mai tsoron Allah.
Dakin ya dawo rai bace ya shiga wanka bayan shigar shi wankan, sauka nayi zuwa kasa na kammala duk wani abinda zanyi na rufe part dina na nufo wurin shi a cikin wasu rigar barci masu daukan hankali sosai.
A D/table na samay shi zaune ya fito daga wankan tunda na nufo gurin ya mayar da hankalin shi gare ni ga waya yana yi a hannun sa.
Kulolin na bude na fara zuba mai tuwon da miyar kubewa sai kamshi kaya yaji da sanadarin miya ke tashi.
Ke ba zaki ci bane ya na jan plate din zuwa gaban shi ya dago yana tambaya na ban jin cin komai yanzu don naci abinci around four dazun a koshe nake sosai.
Na lura baki damu da abincin ba sai yan kayan zaki da sauran tarkace kamar sha zumami dan murmusawan dole nayi don abinda ya fadi din.
Sai kuma naci gaba da tunanen da nakeyi a raina ina tausar zuciya akan abinda nake gani anayi akai na, ko yaushe a gidan.
Na zauna a gaban shi yana cin abincin a hankali ido na kura mai zaka ce hankalina yana gurin shi ne a lokacin a yadda muke zaune.
Kula yayi da zurfin tunanen da shiga wanda ba tunanen komai bane sai na rayuwan matar gidan da muke zaune tare, kullun a cikin fitina babu ranan sulhu ko shiryawa a gare mu.
Muryan shi naji tare da dan kada hannayen shi daidai fuskana, na dago kai ina murmushi tare da fadin ina jira ka

85 / 144

Chapters