Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   24 / 144

69K to 72K   out of 431K words

kalar nake ya bude min motar tare da miko min ledojin dake bayan motar ina karba na fice ina fadin mugu kawai da karfi.
Girgiza kan shi yayi ya tayar da motar ya tafi sai da ya fara tafiyane tunanen Nafisa ya zo mashi a rai yana tunanen ko ina taje dazun ya dawo bai samay ta a gida ba.
Ya iso gidan ya shiga a falo ya samu su Hadiye zaine suna hira suna ciye ciye gaishe suke da dawowa yace Nafisa ta dawo sukace bata dawo ba ya shige ya barsu a gurin zaune.
Ya shiga ran shi a bace ya dubi lokaci yaga tara da wani abu na dare goma saura kadan wanka ya shiga yana tunanen Nafisa a ranshi har ya fito ya kwanta shiru ba Nafisa.
Ni na fado mashi a rai jarababu irin ku murmushi ya danyi yana rufe idon shi kamshin turen oud dina yake tunowa daya shaka.
Ya lumshe idon shi tare da gyara kwanciyar shi yana lumshe ido yaji dadin kasancewa mu a tare yau hiran da nake mai na buzaye ne ya dawo mashi a rai.
Ba abinda na raga daga halin da yasan Nafisa dashi zai iya cewa kila wani ya fada min kadan daga cikin halinta daya fahinta.
Sai dai abinda ya tuno inda nace suna barin mazan su a gida su zo duniya su auri wani mijin na daban sunayi suna zuwa ziyarar mazan nasu.
May wanan maganan yake nufi kodai shiyasa Nafisa take yawan ziyaran gida akai akai bai sani ba da sauri ya kawar da wanan zancen kada zargi abinda bashi ba yashiga zuciyar shi.
To wai ma ina Nafisa taje ne uban may tafitayi da tun safe har wanan lokacin bai ta dawo ba yaja tsuki yace zan gwada ma Nafisa matsayin ta na mace a gidan nan.
Goma, sha daya shabiyu saura ya mike zubur hankali a tashe ya mike yana zura riga a jikin shi ya sauko zuwa kasa komai na falon a kashe yake .
Su hadiye sun shige dakunan kwanan su kayan da sukaci abinci gurin babu kowa a wurin tsuki yaja ya fita waje ya nufi gurin maigadi yana tambayan shi ko yaushe nafisa tafita a gidan.
Maigadi yace rabon shi da ita tun shekarajiya da kawar ta tazo suka fita komawa yayi ciki yana tunanen tun shekaran jiya da kenan Nafisa dama bata gidan tun lokacin da shima yayi tafiya ko may ?
Kamar zai tayar dasu hadiye ya tambaye su sai kuma ya fasa ya koma ya kwanta suna barin mazan su a gida su je wani guri su kara aure suna yi suna ziyarar su.
Abinda ya fado mashi a rai ke nan karfe daya agogon da ya kalla ya nuna mai da sauri ya mike zaune biyu saura na dare yaji ana buga gidan maigadi ya bude kofa motar ta shigo sai ganin nafisa yayi ta fito daga motar ta dan tsaya suna magana da ta cikin motan.
Ta shigo gidan a gajiye take kafafuwan ta har sun dan kunbura saboda zaman motan da tayi mai tsawo dakin su hadiye ta fara zuwa.
Ta samu suna barcin su hankali kwance ta ta da ita a cikin magagin barci tace kin dawo da yare tace na dawo bata gane komai a guta ba ta juya zata shige tace Alhaji ma ya dawo dazu da safe.
Dam taji gaban ta ya fadi da sauri ta fita zuwa dakinta ta kayan sihirin da ta dawo take kokari boyewa a wardrobe din ta sai taga an kuna wutan dakin ta.
A fusace ta juyo sai ganin Abdulsamad tayi tsaye yana kallon ta da sauri ta kara gare shi sai yayi saurin juyawa ya fice daga dakin .
Boye kayan ta karasa yi ta rufa mai baya ta murda kofan dakin a rufe taji shi gam ta juya zuwa dakin ta ciki da fargaba da tsoro a ranta.
Washe gari ta samay alokacin ya gama shiri zai fita yana daura agogo a hannun shi yana gani ta ya daure fuska tankar bai taba dariya ba a rayuwan shi.
Rudewa tayi tama rasa may ta fada mashi can dai tace Samad kayi hakkuri na san ban kyauta ba na fita ba da sani ka ba.
Jakar laptop din shi ya dauka zai wuce ta zube kasa gaban shi tana fadi ka yafe min gurin buki naje shine naka wanan lokacin ban dawo ba.
Nasan nayi laifi fita in dade baka nan amma kayi hakkuri haka ba zai sake faruwa ba insha Allahu.
Yace don gani saunar na miji ki fita gida na kwana da kwanaki yanzu kizo kice inyi hakkuri haka kai tsaye bayan kin gama yawon gantalin ki a can.
Kin kwaso kafan ki kin dawo min gida ki koma inda kika fito zai fi maki sauki na baki minti awa daya ki fice a gidan nan da kowa naki.
Samad kayi hakkuri ka yafe min ba zan sake ba yace rufa min baki munafuka wace bata san ciwon kan ta da darajan aure.
Ya sure jakkar shi ya fice a dakin da kyat ta iya mikewa tsaye daidai lokacin ya dawo yana fadin fita min daga daki zan rufe abina ne .
Ta bishi da kallon mamaki a kofan tana tsaye ya rufo dakin shi karo na farko a gidan abin ya mata zafi saidai cikin ranta tana fadin yi abin ka a hannu na zaka dawo kwanan nan.
Ya fice ta bishi da kallo tare da juyawa ta wuce zuwa dakin ta tana mai jin haushin shi.


Kutayani da addua yan uwa


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Washegari da safe ban tashi da wuri ba don fashin sallah da nakeyi sai da naji motsin daddy ya dawo na fito don in gaida su har lokacin a cikin damuwa nake.
Daddy yana zaune a cikin dan karamin falon mu ga abin karyawa a gaban shi mama tana gefen shi ta motsa mashi kunun da ta aje mai a gaban shi sai kamshi kosai ke tashi a falon.
Daga kofa na tsuguna ina gaida su daddy yace a a baby na shigo mana daga ciki na tashi na karasa shigowa cikin falo har lokacin na kasa sakin jiki dasu kamar kullun.
Daddy yace ya karatu nace daddy Alhamdullah yace babu matsalan komai ko nace daddy ba matsalan komai na fada tare da sunkuyar da kaina kasa.
Ina kokarin mai da hawayen da ya ke shirin silalowa a idona nace daddy sai dai wanan mutumin da ya hado ni da kayan nan wallahi ban san ya sakasu a mota ba sai da muka zo nan taimakon shi nayi shine ya saka min da haka.
Ido duk kan su suka tsura min da nake masu bayanin daddy yana kallona yana yaba hankalina don yasan ba zan boye masu komai dake faruwa ba.
Saboda karya ba halina bane kai tsaye nake fadin gaskiya ga mutum yace dakata khadija kin mashi alheri kin shirya shi da iyayyen shi.
Shi kuma yaji dadin hakan ya saka maki da alheri ko kamar yadda yace na gyada kai nace hakane daddy.
Mama tace ina kika hadu dashi haka khadija nace mama a wurin da aka tura mu aiki ne na hadu dashi ya samu matsala da iyayyen shi da yan uwanshi.
Shine na basu shawara ya nemi shiri da yan uwanshi da mahaifar shi ta hanyar aikata masu alheri daya jaraba hakan sai suka shirya dashi.
Shine yazo yace zai saka min da alheri akan abinda nayi mashi tace khadija shine ya kashe maki wanan uban kudin daga taimako kawai irin haka ?
Nace mama wallahi ni ban san haka zai min ba daga ta Hussai yace ma mama kin san ni ya kamata in dauki zafi akan maganan nan fiye da kowa.
Amma sanin halin ya ta danayi yasa na yarda da bayanin mutumin nan tunda ya rantse min da bata roke shi ba kuma ba da wani manufa yayi mata haka ba.
Yai min bayanin da hankalina ya sa na yarda dashi da ita sai dai yanzu ba yadda muka iya tunda kayan nan sun riga sun shigo gidan nan.
Kiga ba komawa zasu yi ba tunda dai ba rokon shi tayi ba sai dai khadija a gaskiya nayi mamaki da wanan abin don ba karamin kudi ya kashe ba ga kayan abincin nan.
Da sauri nace daddy ba kayan abinci bane kawai har da na sakawa da kudi sune a cikin wanan akwatin da ga gani jiya.
Ido maman mu ta fitar waje tace khadija anya ba dan yankan kai bane kika hadu dashi kada fa watarana ya gama zolayar ki da abinduniya mu nemiki mu rasa.
Dariya maganan ta yaso bani sai na dake nace mama ba dan yankar kai bane don nasan kowa nasa na kuma san matar shi.
Share kawai duk wanan tunanen nayi shi a daren jiya har nafila sai da nayi akai banga wani abin cuta ba daga gare shi sai tarin alheri da na hango ga wanan alamarin.
Shiyasa kika ga ban wani damu ba da hakan sai da ita din ta kula da kanta da mutuncin ta da irin tarbiyar da mukai mata zan sake yin yau na gani don ni kaina abin ya daure min kai sosai.
Mikewa nayi na dauko kudin da kayan na turo zuwa dakin nan na fara fitarwa ina masu bayani yadda kayan suke nima mamakin yawan kayan nake yi a cikin macewa jiki.
Daddy yace aje kayan zamuyi sai na nemi yar uwarki a waya naji shawaranta akai da yadda za ayi da kayan.
Zan dage da rokon Allah don ina jiba jikina kamar akwai alheri ga haduwan khadija da wanan mutumin sai dai mu bar ma Allah sanin shi.
Koda yakira ya Amina yayi mata bayanin abinda na dawo dashi wanan karon tare da fadin ta sake binkice na tsakani na da wanan mutumin don a gono gaskiyar maganan.
Ta kira ni lokacin ina kwance mara na yana damu na da ciwo na dauki wayan ina gaida ita bata tsaya amsawa ba sai cewa tayi Deeda make faruwa ne daddy ya kirani yana fada min wani magana da safen nan.
Shiru nayi sai da ta kara maimaita maganan ta nace cikin kuka wallahi ya Amina ba halina da kuka sani da na canza yanzu.
Nima ban san da kayan nan ba sai da muka shigo garin nan na gani nan dai na koro mata bayanin komai don ba zan iya boye mata ba ita.
Tace khadija kina nufin dama Abdulsamad ne ya yi maki wanan alherin ban sani ba khadija baki jin tsoron buzuwa ta san wanan labarin ta yi maki illar nace ya Amina yaya zanyi ni ban roke shi ba shiya bani.
Tace dama khadija kece kika saka yayi wanan alherin da yayiwa iyayyen shi ashe dama duk kece sanadi ni ba komai nake ji wa ba sai buzuwan matar nan tashi wallahi.
Takira daddy tayi mai bayanin komai yace shi zancen buzuwan matar shi bai damay su ba tunda ta sheda ba mugu bane.
Nema ne idan naga zan iya sai in yi dashi wanan ba komai bane Allah yasan abinda ya hada a tsakanin mu ya kawo hakan sai dai mu saka ido a kan yar mu don har yanzu khadija yarinyar ce karama.
Ya Amina tace gaskiya ne daddy zan shigo kafin ta koma dayardan Allah anan suka rufe maganan tare da taya ni addua ga wanan lamari tunda daddy yace abarwa Allah sanin shi a tsakanin mu.
Maryam ta kirani nake mata bayanin abinda ya faru dani maimakon ta tayani jimamay sai naji tana min dariyan shakiyancin da ta saba min tace shike nan ya nuna maki wayon manya ya gabatar da kan shi ke nan gare su.
Nace wai ke maryam don Allah may yasa kike irin haka ne sai a na maganan gaskiya sai ki dauko wani zance daban tace shike nan yanzu mubar zancen a haka dai.
Nace zai fi sauki muka dauko maganan karatu bayan mun gama wayan ne barci ya dauke ni a wurin wanda nasan barcin da ban samu bane a daren jiya.
Nan dai na kwashi barci na sosai a ranan sai wani lokaci na tashi don mama taki sake min fuska yasa ban son fita a tsakar gidan sam.
Wayana yayi kara na dauka Dan Baiwa nagani a rubuce wani haushin shine ya kamani a raina nayi banza da wayan nashi bandaga ba har kiran ya katse.
Ya sake kirana da kyat na iya daga wayan don har yanzu ina fama da ciwon mara dake cina jin murya na da yayi yasa shi saurin fadin.
May ya samay ki baki da lafiya ne may ke damun ki ne khadija haka yadda naga ya rude ne nace banda lafiya ne .
Tun yaushe nace tunda safe daddy na gida naji ya tambaya nace yana waje turo min da layin shi may zakayi da layin shi nace dashi.
Ban number shi nace maki ya fada a dake nace ban san number shi OK zan kira a bani number yar ki in karba a gurin ta yace da sauri nace a a din Allah ni dai kada ka kirata naji sauki.
Dole na bashi layin daddy din don naga yana niyar kashe wayan bayan na bashine ya kashe wayan bai fi minti goma ba sai ga daddy ya shigo gidan yana fadin ina khadijan take ne wai ashe bata da lafiya bamu sani ba.
Sai da wanan yaron ya kirani yanzu yake fada min khadija bata da lafiya a kaita asibiti wai zai turo da kudi kamar shine ya haife ta.
Mama tace ni tunda jiya da ta dawo na ganta kwance ban san may ke damun ta ba, har dakina daddy ya shigo ya samay ni kwance sai dai ba barci nake yi ba.
Zama yayi saman tsohowar kujeran dake falon yana fuskanta na yaga yar raman da nayi yace baby na may ke damun ki ne yanzu wanan mutumin ya kirani wai baki da lafiya.
Sai dai ban san ida ma yasamo lambata ba ya kira nace niyace in bashi na tura mai yanzu amma ban san kiranka zai yi bz ai daddy yace zai turo da kudi wai kije asibiti nace ya barshi bayan kudin da ya turo muna zai kara dawainiya kuma.
Daddy yayi murmushi yace kin san may yace dani na girgiza kai cewa yayi wai dawainiyar ki yanzu akan shi yake.
Nace daddy kada ka yarda da maganan shi wallahi ni ba komai a tsakanin mu yace naji sai dai yadda yake ya nuna min da fuskan gaskiya yazo maki don bai bar abin a tsakanin ku ba ku biyu ya sakomu mu iyayyen ki a ciki bai boye muna ba.
Yanzun dai yace a tura mashi da account number da zai turo kudi kije asibiti nace daddy nifa ba komai a tsakanin sai mutunci kawai yace yaji.
Sai ga daddy ya shigo zuwa sha biyu yana fadin ya turo dubu hamsin in tafi asibiti nace nasha magani naji sauki daddy dama ciwon mara ne kawai ke damu na.
Yanzu yaya kike son ayi da kudin da ya turo maki kasa kasa da murya nace kayi amfani dashi kawai daddy.
Sai yamma ya kira yana tambaya ko naje asibitin nace eh yace sun baki magani nace eh nasha har naji sauki sosai yace ashe period kike yi kike wanan raki haka ?
Shiru nayi banyi magana ba yace duk wata haka yake maki nace ban sani ba yace kan ki ga Yusuf ku gaisa.
Kunya naji sosai jin har da Yusuf yasan ina period yanzu muka gaisa yayi min yaya jiki nace da sauki yace ki sha magani kin ji sauki ko nace eh yayana .
Sai shiru ya biyo nace Yusuf batare da fadin yayan da na saba kiran shi dashi ba yayi makin jin hakan daga bakina sai ya dake yace yaya akayi yar mama ?
Nace kayiwa mutumin nan fada mijin buzuwa akan abinda yayi min bai kyauta min ba don may yake son saka iyayyena su zarge ni.
Yace zargi kuma khadija akan may nace yanzu haka tunda na dawo mama sai fushi take yi dani akan abin da ya saka a motar da naje gida dashi.
Saboda shi take fushi dake nace wallahi ni na rasa may zanyi akai suna ganin kamar ban kama kaina bane a Abuja ina hurda da mazan banza ne a can.
Sai daddy ne kawai daya fahinci komai da taimakon ya Amina na samu ya dan sausauta min bai fishi dani muryan shi naji yana fadin why mama zata yi fushi dake akan dan abinda na tura masu.
Mama bata yarda da tarbiyan da sukai maki bane ko may in haka ne kuwa zan shigo da kaina in mata magana da zata fahince ni ita ma.
Ban saka ba haka ka hadani dasu dazun daga na fada ma banda lafiya ka fadawa daddy yazo yana yi min fada balle maman mu da ta hau dani.
Ba matsalan ki bane nasan abinda zance da ita idan nazo nayi saurin fadin bansaka ba dai ka barni da ita zamu shirya wataran.
Bayan na kashe wayan na mike na shiga wanka na

24 / 144

Chapters