MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   78 / 144

231K to 234K   out of 431K words

zan ji halin da take ciki in gaida ita kafin nan na yanke a raina ya kamata in fara neman shawaran maryam ance wanda ya riga kwana yana rigaka tashi inji hausawa.
Don haka maryan zata fi ni sanin dacewa inje ko in bari sai ta dawo gida mu gaisa da haka naci gaba da daukan darasins a class.
Sai a zahar muka fito daga lectures a masalaci kamar kullun muka hadu na rigata zuwa har na kusa idar da sallah sai ga maryam din ta iso na gama na dade ina addua kafin in bar gurin zuwa waje na zauna ina gyara jikina sai ga maryam din ta fito.
Muryan ta naji a bayana tana fadin amarsu ta ango yau lafiya kike kuwa tun dazu nake tsaye ina kallon ki kina tunane ko anyi halin naku ne agidan.
Ajiyan zuciya na sauke ina shafa weat lips a bakina tare da fadin Allah dai ya kyauta maryam amma fasawa za, ayi tunda Allah ya kawoni gidan matsala.
Dafani tayi tana kaiwa zaune tare da fadin AA ya dawo ke nan daga tafiyan ko ?
Tana mai tsura min ido taji amsa nace cikin yar murya karama ke dai ya dawo jiya maryam kuma har munyi halin namu.
Nan dai na koro mata da abinda ya faru a daren jiya din tsakanin mu da Nafisa da wanda ya faru da ita din zuwa safe har zuwa na school.
Ikon Allah wai ko khadi matar nan tana sallah kuwa nace waya sanar mata tunda ba part din mu daya ba nace balle ma nasan tanayi tunda nasan shi ba kyaleta zaiyi ba.
Sai dai ibadan ragaggene na sani ba cika shi akeyi yadda ya dace ayi ba Allah dai ya kyauta kawai kedai maryam tace amin.
Nace ni yanzu shawaran ki nake nema shin in tafi asibitin ne idan tana can har yanzu ko in bari sai idan ta dawo gida in gaida ita don kin san ita bahaguwar mace ce maryam ba ai mata daidai kin sani.
Shi AA din ya kiraki ne da sukaje asibitin nace bai kirani ba nice dai ma na kirashi ina tambayan jikin nata a guriin shi.
Tace matsalan maza ke nan wallahi ai kamata yayi kafin ma su fita ya sanar dake amma yasa kafa kamar baisan akwaiki a gidan ba akala da suka isa komai yayi daidai ai sai ya kiraki yai maki bayanin halin da ake ciki ko.
Nace ni wanan bai damay ni ba don sun fi kusa shiyasa kike ganin duk irin fitinan da zasuyi bai zurfi a cikin sa dan kai zasu bari a cikin idan ka shiga.
Yanzu zasuyi masifa kamar su kashe junan su amma minti goma yayi yawa ki samu sun shirya don may zan tsaya ina wahal da kaina akan su nidai hakkina na tsare kawai don kada wullakanci da raini yai min yawa.
Tace kin kyauta ma kanki wallahi don irin auren jaraban nan idan kana gidan da akeyin shi wallahi sai su daure maka kai don ga abin haushe na faruwa saidai kai kaji musu haushin kawai su basu damu ba.
Ni yanzu shawaran da zan baki shine ki fara bincikawa idan tana asibitin sai muje can mu gaida ita ai ba don ta zaki ba don Allah ne da shi kuma AA din.
Sanan kuma hakan wani makami ne a gurin ki don gaba koda magana ya taso dai kina da abinda zaki fada masu wanda ita ba zata iya maki shi ba.
Na nisa tare da fadin gaskiya maryam ba zan iya kiran AA ba tunda shi baiyi tunanen ya kirani ba insan halin da ake ciki.
Tace kada ki kirashi nima ban goyi bayan ki kirashi ba ai maza suke gyarawa kuma suke bata gidan su idan sun tashi.
Barin kira Yusuf muji halin da suke ciki kiin ga sai mu san abin yi ko kai kawai na gyada mata ina matse jikina da hannaye na wuri daya ina tunaane tare da takurewa a ida nake.
Kira uku ya dauki waya tare da fadin maryam kuna tare da kanwa tace khadija tace eh muna tare itace ma ta sa in kiraka muji halin da mutanen gidan su suke ciki a asibitin.
Yace eh suna can har yanzu don likita ya bata gado na kwanaki har aga halin da cikin zai yi tukun maryam tace dama muna son jin ida suke ne sai taje ta gaida su.
Yace yanzu kuna free ne ko sai anjima inzo in kaiku tace bamu gama ba amma zaka iya zuwa muje ai ba matsala kada yamma yayi.
Yace kujirani ganinan zuwa insha Allahu tace sai kazo Allah ya tsare take care ta kashe wayan tana kallona tare da fadin ke kinji bama zancen dawowa gida bane fa.
Don an kwantar da itane acan sai anga yadda hali zaiyi idona na lumshe ina tunane rayuwa na sake budewa nace oh mata suna ganin abu akan ciki kamar ba ita bace lafiya jiya fa.
Tace ikon Allah ko mutuwa akace maki tayi yanzu ai ba abin mamaki bane don ikon Allah yafi danan nace kwarai kuwa maryam.
Tace aini abinda nake ji zata zauna ta iya yin bedrest din nan a asibiti wanan matar da take kamar shanshani wurin yawon tsiya.
Zata iya mana idan ya kama tayi dole don lafiyan ta sai dai idan cikin bai damay ta bane mun dan dauki lokaci a gurin kafin Yusuf yazo.
Da ya iso wayan maryam din ya kira yana sheda muna zuwan shi muka samay shi a gurin da yai muna kwatance din.
Baya na shiga maryam a gaba ta zauna dashi sai da ya fara tuki nake gaida shi ya amsa da yaya gida jiya mun iso ban samu shigowa cikin ba ina sauri.
Nace kun dawo lafiya ya mutanen gida yace suna gaida ku Fati tace ai maki godiya sosai sun gode nace kai sai kace wani abu na basu mai yawa.
Yace kin yi kokari sosai khadija ai baki san wani abu ba wallahi macen kwarai ke kula yaranta har tayi masu alheri irin haka.
Ina ta samu haka a baya banda ma idan mijin zai yi idan har Nafisa ta sani hanawa takeyi ko ta amshe kudin da sunan zata saya masu abin sai labarin ga.
Maryam tace wallahi wanan abokin naka yana bukatan gyara a rayuwan shi wallahi ta yaya kana tare da mutum abu ya samay ka bazaka iya fada mai ba.
Yace maganan da muka gama dashi kenan kuka kirani wai cewa yayi ai khadija ta sani kuma ta wuce school bada izzinin shi ba.
Murmushi nayi nace ni ina na kara ganin shi ma yayana tun fa da aka buga kofa ya fita ban sake ganin shi ba har yanzu.
Zan zauna ne akan lalurar wata in bar nawa yace na fada mashi ai da yake fada nace kai ka kirata kai mata bayani halin da kuke ciki shine yai min shiru.
Ki dai kara hakkuri kanwata wata rana sai labari insha Allah irin wa yan nan matan ba abokan zams bane wallahi.
Yanzu a asibiti sai da suka kwashi rikici sosai da ita wai ita bazata zauna ba har tsawon wani lokaci da kyat likitan tayi mata bayanin halin da take ciki kafin ta yarda ta kwanta din.
Allah dai ya bata lafiya nace idan tayi hakkuri kwana nawa ne in ta samu lafiyan ta ba sai ta dawo gida ba duk da an san zaman asibiti ba dadi wallahi.
Yusuf yace lafiyan ta yafi komai fa khadija ita wata irin mace ce da bata da ganewa ne mace har da kanta takewa kyata haka.
Nidai shiru nayi suna ta maganan su a hanya wurin masu fruits ya tsaya ya fita sai gashi da ledojin fruits an biyoshi dasu zuwa wurin mota yace zaku shiga mata dashi kada kuje hannu sake.
Godiya mukai mai yana zama nace ummmhmm ni nasan ko kallon wanan ba zatayi ba zatace wani abu muka saka mata aciki don ko yanzu ba fita zanyi ba a gurin ta.
Kada ki damu da wanan don ko baki fada ba sai ta fada idan kuma baki kai badin ma fada zatayi don halinta ne haka.
Mun isa asibitin motar AA mukai tozali dashi a haraban wurin aje motocin muka fito Yusuf na gaba muna biye dashi a baya shi ya dauki ledan tsaraban kayan dubiyar da ya saya muna din.
Lokacin ganin mara lafiya ne a lokacin ga yan uwanta da kawayen ta harda ma wa yanda ban sani ba a gurin.
Suna hango mu kamar ba asibiti ba idanuwan su ya dawo gare mu caaa sai kuskus ake yi a gurin bani ba ko maryam bata tsaya binta nasu ba muka shige dakin da take kwance a ciki.
Ita kadai ce a cikin dakin ba,a hadata da kowa a dakin ba komai akwai a dakin na jin dadin rayuwan dan adam aciki.
Yana zaune bakin gadon da take kwance ga su madam a gefen zaune ya rike mata hannu suna magana muka shiga dakin.
Yusuf ne ya aje kayan yana gaida ita da jiki muka karaso wurin sai dakin yai tsit a lokacin suna kallon mu.
A bakin gadon muka tsaya muna mata ya jiki bata amsa muna ba sai shi dake zaune ke fadin baki jisu bane ?
Ta wani dako kai tana fadin najisu mana ba tazo ta gani da idon ta ba ban mutu ba yadda taso in halaka.
Murmushi nayi tare da fadin Allah dai ya baki lafiya ya tsare gaba mu duba lafiyan ki ne ya kawo mu ba wanan ba.
Allah ya sauwa ka nace tare da fadin mu tafi ma maryam muka juya mun fara tafiya naji muryan ta a cikin hausan ta dake da surki tana fadin ku zo ku dauki kayan tsiyar ku, ku tafi da sherin ku baku ganni cikin mugun hali ba.
Madam ne tace haba matar Samad wanan wani irin haline ai kya bari ki koma gida duk abinda kike ji kuyi shi a can amma ba anan ba.
Duk wanda yazo gaida kai koda na munafunci ne ai yayi kokari tunda tsabgan gaban shi ya bari yazo ko.
Mudai mun fita daga cikin mu ba wanda yai magana har muka kai bakin mota muka tsaya jiran yusuf ya fito mu tafi.
Ashe a ciki sun kwasa da Yusuf din a kan mu da yaji zagin yai yawa yace mata irin hakane kike jawa kan ki matsala may zata saka maki a cikin ayaba da lemo ko kankana yanzun fa suka sa na tsaya hanya suka saye shi.
Tace koshi an fada mashi yarda tayi dashi idan akwai wanda zai kashe ta farko ai shine don ta dade da sanin haka .
AA ne ya mike tare da jan tsuki ya yiwa Yusuf magana su fita daga dakin tace kai kuma ina zaka ko binta zakayi ne ?
Yace idan na bita laifi ne yasa kai suka fito sun samay mu a tsaye ba mai magana a cikin mu kowa da kalar tunanen da yake yi.
Bayan fitan mu madam ne ta ja tsuki tare da fadin Nafisa ina ganin tafiyan mu ba zaizo daidai da ke ba gaskiya.
Yanzu wa ya saura irin wanan kishin da kike haka koma may ye kin ga yanzun tafiki gaskiya ga mijin ku don tazo dubaki a gaban shi kin mata rashin mutunci kuma.
Yanzu abinda kikai din nan yayi daidai ke nan har karamar yarinya tazo tafiki wayau ta nuna maki hillan mata da kissa.
An san akwai zafi tunda a sanadin ta haka ya samay ki sai ki barin har kiga lafiyan ki tukun na sai kin koma gida ki nuna mata halin ki.
Tace madam ke ma kin san ba zan iya ba wallahi uban wa tazo nema a gurina in ba zuwa tayi tagani ko zan mutu ko ina cikin wani hali ?
Dadai kin koyi boye wani hali a gaban miji don ranan fadin magana tace ba wani ranan fadar magana in ba bayan wanan yar iskan nayi da mijina ba.
Ledan kayan fruit madam ta jawo ta fara budewa tana fadin mukan bari muci tunda bada sunan mu akai aikin ba komai ba zai samay mu ba.
Nan suka far ma kayan da ci kamar jira suke itako wani irin bakin ciki take ji a ranta na bin bayan mu da yayi.
Sai lokacin yake gaisawa da maryam ta amsa tana tambayan shi ya mai jikin yace da sauki ni dai ko kallon shi banyi ba ina kallon wani wurin.
School din zaku koma ko gida maryam tace ni dai zan koma itakan gida zata yanzu ai yamma yayi ko mun koma ba wani dadewa zamuyi ba a tashi.
Barin sauke ku yace nace da sauri da ka tsaya kada kuma kayi laifi yaya Yusuf sai ya sauke mu Yusuf ne yace lalai kan don abu kadan yanzu laifine ga mai ciki.
Tsaye yayi sororo yana kallona ina magana ga mamakina nayi zaton zai yi magana amma sai ya kyale Yusuf din ya tafi damu har muka kai gidan ba sa baki a hiran su ba.
Wanda duk hiran akan Nafisa ne suke yin shi muka kawo nayi wa Yusuf godiya na bude na fita ban san ya sukayi ba naji muryan maryam tana kirana na tsaya tare da juyowa.
Ganin tana magana yasa na koma wurin motar inji mai zata fada min sai naji Yusuf na fadin kanwata don Allah kada ki sa komai a ranki halin Nafisa dai yanzu ba bakon abu bane a wurin ki.
Na dan yi dariyar yake ina fadin ba komai wallahi nagode yace ke dai kici gaba da addua don Allah shine kawai mafita ga wanan shu,umar abokiyar zaman taki.
Murmushi na sakeyi ina fadin ba komai na gode nayi masu sai anjima na wuce ciki zuciya na cike da damuwa ina isa na shiga babu kowa a gidan sai mutum daya da yara a gidan.
Ihsan na ganina ta sheko da gudu ta rungumay ni wanan matar dake gida da suke kira da gambo tazo da sauri tana kokarin daukan yarinyar taki zuwa yar Nafisa babba tayi mata yare naga ta bar ta dani.
Dakina muka nufa da ita tana min yare na bude muka shiga kayan zaki na bata irin na yara ta fita da gudu zuwa waje murmushi nayi na tube don in watsa ruwa a jikina.
Sai da na fito nayi sallah na koma na zauna na gyara jikina a gaban mirrow kitchen na shiga don nemawa kaina abinda zanci may dan karfi don yanzu ina ci abinci sosai gashi tun safe ban ci wani abu a cikina har na fara galabaita.
Lafiyayyen nodles na hada wanda yaji kayan hadi don ya cika min ciki na na debo nazo falo zama sai ga Ihsan ta dawo dakin wurina.
Tayi nayi mata tace zataci na dibar mata waje ta nufa dashi na zauna na fara cin wanda na zuba ma kaina.
Yar wurin Nafisa ne ta shigo sai ranan ta fara gaidani a gidan tana tambayana idan abincin da na dafa ya rage in diba mata yunwa take ji.
Kallon ta nayi kamar zanyi magana sai dai na mike na shiga kitchen din na juyo mata wanda ya saura gaba daya.
Ta karba batare da furta komai ba ta fita bayan na gama ne na fito don gyara part din msigidan na samay su zaune dukan su harda mai tsaron su a gidan suna ci.
Na shiga dakin yana a yadda na barshi da safe sai kayan barcin da ya cire a saman gado ko tsaban rudewa yasa yau ya barshi a wurin ban sani ba.
Wanko ban dakin na fara yi inda na dawo dakin na gyara mai komai tsab na rufo kofan kamar yadda na samay shi na dawo part dina.
Har akai magariba banji ya shigo gidan ba har tara na dare barci ya fara dauka na tashi nayi na kule part din na don na dauka a asibitin zai kwana ke nan.
Sai sha daya da wani abu ya dawo gidan bayan sun gama tsiya da Nafisa daga kwancen amma bata barshi ba don cewa tayi bata yarda ya kwana a gidan ba don ranan girkita ne.
Kada yaje wurina don baiga idon ta ba da alkwari da komai ta barshi ya tafi gida shi dai sai lalabata yakeyi kada cikin jikin ta ya samo matsala dai.
Koda ya shigo gidan ba kowa a falon sai dai wuta a kunne yake har lokacin kallon kofan part dina yayi ya ganshi shima rufe.
Kofan gidan ya rufo ya nufi part din shi don ya watsa ruwa Allah ya taimake shi yayi duka sallah a cikin jamm,i wanka ya rage mai sai dan abinda zaici.
Ya fito yana saye da bathrobe ya tsaya gaban mirrow dakin har ya gama shiryawa cikin pjarm din shi ya sauko zuwa part dina ya murda hardles din yaji kofan a rufe kara murdawa yayi sosai ya ji a key kofan yake .
Gashi yana gudun buga kofan yan uwan Nafisa su jishi sukai mata labarin sun ji shi yana bugun kofa na dole ya juya ya koma part din shi

78 / 144

Chapters