Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   113 / 144

336K to 339K   out of 431K words

ya dauke ni ban sani ba ta fito ta barni don in samu barcin.
Washe gari tunda na tashi nake baki masu shigo taro na don an kai masu tsaraban da nazo dashi suna tambayan yaushe zan koma sai ace masu gobe.
Duk wanan bai sa zancen mafalkin da nayi da madam da yanyala ya fita raina ba da wata mace da ban sani ba mama ta lura da damuwan da nake ciki sai da muka kebe nake fada mata abinda na gani a cikin mafalkin nawa.
Da farko dai ana taro ne a dakina sai gasu sun shigo fuskan madam ya canza ta karbi wata yarinya ta barin wurin yarinyar ta koma wani kala kamar abin tsoro.
Yanyala kuma ganin ta nayi tare da nafisa suna bina da gudu ina kama yara sai ga AA yazo ya tare mu sai suka juya da sauri..
Ajiyan zuciya mama ta sauke tace ke nan akwai wani fitina a boye da zai taso nan gaba ki yabada lambar wayan shi mu kirashi mu fada mai abinda kika gani din.
Nace nima zan so na samu lambar inje dashi don ko wani abu ka taso mun a can sai in kirashi in mai bayani.
Mama ta kirashi sun gaisa yace a bani waya bayan dan wasan jika da kaka da muka taba dashi ya fara tamnayana ko nayi mafalkin nace eh tare da mashi bayanin komai dala,dala ya sauke ajiyan zuciya tare da fadin ikon Allah.
To Allah ya kyauta ya tsare ya kare kuma mafalkin farko yana nufin suna da mugun manufa akan abida zaki haifa nan gaba sai kiyi taka tsatsan da su sosai lokacin haihuwar naki don akwai wani sheri da suka kula.
Sai nabiyu dake da zurian dkine suke bi da sherri wanan daya tare ku shine zai taimaka maki a nan gaba akan sherin nasu.
Yaushe ne tafiyan ku nace gobe yace da wuri haka nace kwanakin da akan bake nan inyi yace ba damuwa tunda bada safe kwarai zaku tafi ba ai nace eh malam.
Yace to goben zan ba yarda abu akawo maki kafin ku wuce sai ki kirani a waya zan maki bayanin komai Allah ya kara tsarewa nace amin nagode muka kashe wayan.
Shikan daddy ba abinda ya damay shi sai harkan shi yake dani da mamane muke kashewa muke binnewa mu kadai ba tare da yasan komai ba sai kuma ya Amina da wayanta ke kai yana kawowa akan mu.
Sai da mukai waya da tsohon na danji sanyi a raina yadda ya kwantar min da hankali sai shirin ake min yayin da nake jin raina ba dadi na komawan nawa.
Don bansan kuma damay zasu tare ni kuma don yanzu tsoron su nake ji sosai abin yayi yawa sosai kullun babu sasauci ga alamarin nafisa din.
Abuja tun ranan da muka bar gidan ta fita ta bar yaran sun kadai a gidan har mijin ya dawo basu dawo ba ashe sunje wani kauyen kefi ne dare yai masu acan.
Ranan yai mata masifs sosai yakuma sa mata kulle ance mai kishiya bata mutuwar Allah ni da ban gari amma laifina Nafisa ta gani.
Wai na kai AA wurin tsafi an tsafe shi tun kan in dawo gidan dole ta mike don tasan ina can gida ina sabon shiri a kan ta da mijin ta.
Da rarashi da komai taciyo kanshi ya yarda yanyala ta dawo ita kadai ta zauna dasu don kula da yara nan suka hade sukai ta binne binnen su a gidan yadda suke so.
Saboda sakon da za a kawo min muka dan bata lokaci gashi sai kira yake muna ina bamu taso ba har yanzu muna may a minna har wanan lokacin.
Banbi ta nasa ba sai dana karbi sakona muka kama hanyar Abuja uku da wani abu muka shigo garin da shirina na dunfari kofan ina adduoi a bakina banji fargaban komai ba na shiga gidan ba kowa a falo sai tv dake aiki shi kadai.
Part dina na bude ana samun kayan da akai min tsaraba daga gida ciki Ihisan ce ta fito taga laraba ta shigo da wasu kaya ta sake ihun ganin mu shiya hankaltar da iyayyen suka san mun dawo.
Dakin ta nufo tana jikina tana zuba surutu sai ga Yanyala ta shigo tana kiranta nayi mamaki kwarai da gani yanyala ta dawo gidan sai dai ban tankata ba taja yar suka fita.
Mikewa nayi zuwa uwar dakina na fara tube kayan jikina sai ga Laraba ta leko tana fadin uwar dakina maza a barsu kawai kinga matar nan ashe sun dawo gidan nan kuma.
Nace mayu ne basu da zuciya wace Suraj yaiwa koran wullakanci irin haka ko kofan gidan nan in nine ai ba zan kara kallo ba.
Tace kin san su da bakin nacin tsiya ai in sun samu guri kamar gidan gado suka samu ta fita na mede baki ina fadin shi dai ya sani mina fuki.
Kansu zai kare shida ya dauko jaraba gidan shi ya sani ana wani labewa ga asiri yanzun dai ban kara yarda da cin kashin kowa daga cikin su.
Wanka nayi nayi sallah ban fito ba sai da nayi la,asar nafito falo bambarana na diba naci mai isata na saka saura a cikin fridge.
Biyar daidai ya shigo part din mu da mama suka fara gaisawa yana tambagan ta ya hanya da mutanen gida.
Ya juyo inda nake dan cin sauran bambaran dana rage yana fadin kun iso ashe nace eh yaya mutanen gida sunce suna gaishe ka sun gode.
Bai yi magana ba sai kallo na dayake yi sai kuma ya tuntsure da dariya yace haka kika je masu da katon cikin nan kowa na kallon ki dashi.
Nace ai sin san ba laifina bane don bada shi nazo nan ba da farko yana kallon abinda nake ci tare da fadin maye wanan haka kuma kike ci nace cimar mu ne na yan Niger.
Ko zakaci ne in dibama na tambaye shi ina kallon shi tare da fadin ga doya can daddy yasa muzo ma dashi nace ya barshi muna dashi yace a, a.
Yace nako gode ai doyan ku daban take da namu na nan tana sakwara mai kyau sosai akace nace in diba ma bambaran ne ya bata fuska tare da fadin ci abinki na gode.
Ya fita naso ranan in huta amna hakan bai samu ba sai da ya saka ni in mashi sakwara da miyar egushi yace yana so dole muka daka mai shi.
Zan kai mai abinci na hadu da nafisa tana saukowa saman harara ne ya raba mu yadda naga ranta a bace nasan sunyi tsiyane ta fito.
Shima a haka na samay shi ban kula ba ban kuma tambaya ba shine naji yana tambayana da cewa idan mace ta dawo tafiya kafin yamma ba ita bace da girki sai idan yamma yayine lokacin amsan girki ya wuce ta iso bazatai girki ba.
Nace eh haka naga anayi sai lokacin na fahinci may sukewa rigima nakuma fahinci dalilin shi na matsa muna mu taso da wurin da yake yi tun muna minna.
Nace idan girkin take son yi ka barta mana tayi ba shike nan ba nasan dai ina gidan zuwan ta gida sau biyu kuma bantaba cewa zan karbi girki a ranan da ta dawo ba.
Don haka na kulle a raina nasan abinda zan mata nan gaba idan tayi tafiya ai abin ba tsoro bane don taga ina daga mata kafa ne ta dauka duk asiri ne ke cina.
Ranan wani munafukin soyyaya gwada min in da na dabe komai a raina nima na gwada mai nayi missing din shi.
Washe gari ban fito ba har goma muna dakin muna barci wanan abin shi ya bakanta wa Nafisa rai sosai don tana falo tun bakwai tana dakon fitowan nawa.
Bayan na fito ne na samay su zaune a falon na shige ina jin tana buga wani uban tsuki nace sai dai shi kan yanzu.
Dakin ta nufa ta samay shi ya fito wanka gadon ta kalla na gyara shi fes kamar bamu kwanta ba tace dan dadin abu kazan mace.
Anje gida an tsuma anzo maka dashi ka rude harda kaiwa karfe goma da mace cikin daki baka fito ba may kake nufi da hakan ko tafi kowa dadi ne wai.
Yace baki ganewa ke wanan sirina ne kuma nakai karfe goma din kema kije ki tsuma naki idan kina son in sha daya dake.
Yana magana yana nuna mata lokaci da hannun tace Samad ni kake fada ma haka akan wanan yar duniyar matar taka yace na fada maki ke may ye na shigowa ki mun wanan maganan haka.
Ko ke ba a kwana dake ne wani yahanaki kai wanan lokacin ne a dakin nan kullun ke ke nan amaki ba daidai ba cikin korafi.
Na dauki hakkin kine na kai mata ko ita ta saka ido akan abinda mukeyi dake ne a gidan nan barin fada maki nagaji da wanan halin naki wallahi.
May na rage ki dashi na rayuwa akan wanan yarinyar ne a gidan nan kina da abinda bata dashi tayi hakuri dani ta zauna dani duk da tasan ina tauye ta din akanki.
Ko finta kikayi a gurinanr wai tace tana gyada kai lalai Samad shike nan an kaika wurin dodon Nufawa sun asirice ka tunda har ka iya fada min wanan magana ko duk zaki kazane yasaka sake wanan santin.
Yace ashe kin gane nasha dasin da ban taba shan irin sa ba jiya kuma ki bace min da gani dakin nan kafin ranki ya baci sororo tayi tana kallon shi yau.
Don tana da tabbacin aikin da taimay ba zai iya taba daga ido ya musaya mata maganan ta ba sai gashi jiya jiya da dawowa na gida taga sauyi mai yawa a tatare dashi din.
Bata iya kara magana ba juyawa tayi tafita a hasale shikuma yaci gaba da shirin sa hankali kwance tana zuwa daki ta rarumi waya tare da danna wa madam kira.
Tana dauka tace ayyah madam na shiga uku wanan yarinyar ibilishiya ce ta gama min da miji kin san wai sai yanzu suka fito tun jiya da suka shiga barci nayi mai magana baki ji irin santin kaza da Samad ke min ba yau.
Madam tace waya aikeki wayasa ki ki masa magana Nafisa nafa fara gajiya da wanan halin naki kema kin san idan mace tayi dan tafiya bata gida namiji dokin ta yake yi kamar tayi tafiyan shekara ne.
Tace madam abin ne da ban haushi wallahi yun jiya fa sai yanzun suka sako kasa ji irin kudin da muka kai kefin nan fa duk akan shegiya ta dawo mai makon inga sauyi sai bacin rai.
A bangare na na shirya mai abin karyawa wanan duk yana daga ciki huduban dana samu wurin mama Tani harda dadewa ban fito badanayi daga gurin shi din.
Sai da ya gama shiri ya sauko ganin ban kawo mai abin karyawan ba yasa ya biyo part dina nan na zaunar dashi muka karya ina jan shi da dan hira ya bata lokacin shi a gurina.
Yana fitowa ta wani kafe shi da ido sai gani na fito dakin dauke da case din shi a hannuna tare muka jera zuwa waje sai da motar shi ya bar gurin na juya na shiga ciki.
Barci nayi sosai sai bayan sallah na fito falon gidan na zauna tare da kuna tv bayan nasa laraba ta gyara min falon don wurin kamar tunda mukai tafiya ba a gyara shi ba.
Suna daya gefen zaune nace Samira ta miko min remote na canza canal nakai muna mbc 2 muna kallon fin can na rage sautin tv na danna kiran layin shi ya dauka.
Hira mukayi sosai dashi duk hankalin ta na gurin mu tana ji kamar ta taso ta shake ni a furin takeji a ranta.
Da gangan nayi mata haka karshe kasa zama tayi a falon ta shige ciki tare da kiran yaran ta suka barmu a gurin bamu tashi ba sai yamma muka shige part dina .

ZAINAB IDRIS MAKAWA
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Ni kaina canzawan da nayi a gidan cikin dan kwana biyun danayi da dawowa yana buurgeni don a sannu ina samun kulawa daga maigidan ta yadda ban zata ba.
Ashe gaskiyar maryam da take fada min ciki bai saka rage komai gun miji sai dai ma ya kara maku farin ciki .
Don ni a wautana na dauka cikin da nayi saurin samu ba zai barni inyi yadda raina zai so ba ko samun kulawan maigidan a kaina ashe abin ba haka yake ba sai yanzu da nayi amfani da nasihar mama tani dake fadin indan baan dadage ba zasu daga min nono a cikin wasa.
Ba miji kulawa yana kawo shakuwa da yarda a tsakanin ku sai yanzu na kara yarda da wanan maganan don na gani a kaina.
San kulawan da nake nuna mai da yawan manne mai idan muna tare yasa na fara zama kamar wata abokiyar shawaran sa.
Koda ban je gurin shi ba shi da kansa zai zo part dina mu dade muna hira dashi wanda haka nasha kama su da Nafisa suna fitin akan hakan.
Duk da har yanzu bawai power ta ya kare a gidan bane akwai dan shakkunta a tare dashi ban damuwa da hakan kokarin kafa kaina nake a gare shi.
Yanzu ma na dawo daga rakiyar shine zai tafi office nan muka wuce su a falo zaune kamar kullun idan ina da girki hakan take miin wanda nasan ba zaman banza take a gurin ba zaman saka idone akan mu.
Ina shigowa tace karuwanciin banza indai na miji ne can muka fito muma talkaman ya tsunke baan yarda na kyale ta ba najuyo nace ashe takalman naku dama tsoho ne kuka saka harda ya tsunke din.
May kike nufi da maganar ki nace amsar maganar kice na baki ai dama tsohon gindn kika kawo mai wanda mazan buzaye suka gama dashi ashe shiyasa kikai saurin daukewa.
Wa, iyazu billah nan naga tijara iyayyena sun sha zagi ranan a haukace ta tashi kamar zata dukeni sai tazo kusa dani kuma komay take tunawa sai ta dan ja baya.
Nace kiyi naki kibar na Allah wanan kan an hade mutu ka raba takalmin kaza ba abinda zai sashi tsunkewa da kike tunane yanzu muka fara wasa dake a gidan nan.
Idan kin fada min biyar sai na fada maki goma don haka shege ka fasa dani dake na shige dakina ma barta tana masifa.
Karshe na fito wanka sai ga kiran shi ya shigo min yana tambayana wai may kuma ya hada mu da Nafisa ne bayan fitar shi yanzun ta kirashi tana tashin hankali.
Murmushi nayi nace yaya kadai san halin matar ka magana ta fada min na bata amsa shine ya zama tashin hankali nina fita batun ta ai tunda na bata amsa ai.
Deedar bakya dai ji baki fita zancen ta wai nace ai na fita nikan tunda ban tsaya kulata ba yadan gama babatin shi ya kashe wayan na kali wayan nace Waire inji yarbawa.
Da yake ba abincin rana yake dawowa ci ba don haka na samu issashe barci na dakyau da rana sai bayan sallah la,asar na fito falo da laraba muka zauna.
Babu kowa a falon sai baby ita kadai a kwance falon tana tsala kuka kamar in share yarinya na dai daure nace laraba ta dauko min ita.
Allah sarki yarinyar tana kara girma kanta ma yana kara wani yin gingiringin dashi ga wani dan molo dayayi a gaba idan ka kalle ta sau daya bakaa son ka kara kallon ta karo na biyu.
Na duba tayi kashi da amai nace laraba ta duba yanyala ta bata yarinyar ta duba babu kowa a part din yana a rufe gashi tana kuka da alama abinci take so a bata.
Dole laraba ce nasa ta wanke mata kashin ta kawo min ita shiru shiru basu dawo ba nan kira AA ya shigo min muna waya yana jin kukan yarinyar.
Yace sadiya ce a gurin ki nace eh yanzu na fito falo na samay ta ita kadai a kwance tana kuka mun duba part din babu kowa da alama ma yunwa take ji.
Tayi kashi an wanke mata sai dai ba abincin ta a kusa yace gashi nan zuwa yanzu AA yana kokarin kula da yarinyar sosai don yafi uwar kula da ita gaskiya in dai yana gida zai dauke ta su tafi part din shi.
Amma uwar da wuya kaga ta dauki sadiya a jikin ta ba a dade baa sai gashi ya shigo dauke da madaran da ake mata amfani yana zaune aka bata tasha sai barci ya dauke ta.
Ajiyan zuciya ya sauke tare da kada kai yace wanan wani irin rashin imani ne haka ga Nafisa na lura sam bata son yarinyar nan tunda aka haife ta hakan nan.
Take kyamkyamin ta sai wani maganan banza wai an hurhura mata yarta ne donn likita yace mata namiji zata haifa sai gashi ra haifi mace macen wai musaka acewar ta.
Laraba dake gyarawa yarinyar kwanciya tace da Allah take jayaiya ke nan kuma irin yaran nan in suyi lafiya ai su ke zama wani abu wata rana.
Ya mike yana

113 / 144

Chapters