dalilin rufe kitchen da tsore din gidan da akayi wa mutanen gidan.
Hajiya nan fa gida na ne ina da daman da zan rufe ko ina nake son don Abdul bai bar abinci da Fati a gidan nan ba tunda bai cata dawo ba ta dowo don haka sai ta jira idan ya dawo ya bata abinci ita da diyan ta suci.
Karya kike yi munafukar Allah kuma baki isa ba wallahi muryan Suraj ne da batayi tsamani ba ya fado dakin yana zazzare mata ido a cikin hasala yake magana yana huci.
Tare da daka mata tsayawa yana fadin ban makulin nan tun ban balbalaki yanzu a wurin nan in kuma sa sojoji suzo su kwashe ki sukaiki barikin mu su daure har ranan da miji ku ya dawo inji shiku idan shiya ai horo da yunwa haka.
Kallo da tayi wa Suraj raga fuskan nan nashi ba imani a cikin sa zai iya aikata abinda yace a kanta tsoran ta Allah tsoran ta soja da sauri ta mike ta shige dakin ta yabi ta da harara.
Yadawo da fuskan shi kan yar ta dake cin abincin da tayo masu take away a hanyan dawowanta gida ya watsa ma yarinyar harara da sauri ta noke kanta kasa ta kasa cin abincin da tun shigowan su dacin abincin ta take yi bata ko gaida su ba.
Da sauri tafito daga dakin dauke da key din a hannun ta tana mika mashi cikin ladabi ya fisge a hannun ta har ya fara tafiya su mommy zasu bishi sai kuma ya juyo yana fadin.
Ina ne kitchen din da tsore suke ki taso muje yau za a yi ta ta kare and idan bayan tafiya ko harara naji kin ma yar uwa wallahi yau ba ubanda zai hanani daureki a garin nan jiki na rawa ta bi bayan shi zuwa tsore din yace ta bude da kanta ta bude.
Laraba da mai masu aikin gida namiji da ta dauko dan kabilar su can garin su wanda ya zama kamar CID din ta ga komi a gidan ko tana nan ko bata nan ya kira.
Komai na tsore din aka fito dashi waje aka kasa uku yace Fati ta kwashi kashi biyu ita da diyan ta kashi daya ta dauka nata ne.
Ga abin magana ba halin yi don tsoron soja da ke zuciyan ta tun da zasu shigo Nigeria sojoji suka latsu a hanya take tsoran soja inda duk ta ganshi.
Yana tsaye a rike kunkurun shi da hannayen shi biyu yake tambayan fati akwai wani tsore da kitchen a gidan tace eh akwaishi a part din ta wanan nata ne ita fatin suke amfani dashi in generar.
Kwashi naki kikai part din ki da sauri taja wani kwali da kyat tana fadin kasiye dauko mun sauran ta matsu tabar wiein wanan dan banzan soja mara hankali dake gabanta.
Dama tun zuwan ta gida da ta fara ganin shi aka nuna mashi ita a matsayin sabuwar matar wan shi bai yi murna da ganin ta ba a fili ya nuna hakan kowa ya gani.
Don shi kyamar irin su yake yi bai dauke su wasu cikakkun mutane ba a idon shi, yafi daukan mayaudara aduk inda ya gasu haka yake kallon su a yatsune.
Shine dan uwan shi ja jini ya auro ya kawo ta cikin zurian su take juya mutane yadda ta ga dama a gidan da takaicin ta ya juya tafi bai shiga gidan nasu ba a lokacin mommy tare da anty Amarya suka koma gida bayan sun yiwa Fati nasiha kadan.
Nan suka tafi suka bar Fati da tsoro a zuciyar ta fam sai dai abinda bata sani ba a halin yanzu Nafisa tafita shiga tashin hankali don tsoranta Allah tsoron ta Suraj soja.
Wanda ta hango mugunta zalla cikin kwanyan idon shi abinda ya fadi tasan karamin aikin soja ne yayi shi ya aiwatar da abinda ya fada din dole ga magana nacin ta da zata fadawa Fati a yau sai dai babu halin yin hakan gare ta dole ta kawo ido ta saka mata a gidan tana jiran dawowan mijin nasu wanda zata sa ya ci fuskan Fati din a gidan.
Ai idan sun san wata basu san wata da makirici zataci galaban su gaba daya don ta gane yan uwan mijin da iyayyen shi duk munafukai ne a kanta.
Can gidan su hajiya sun koma kumshe da dariya a cikin su sai da suka shiga mota suka fara dariyan abinda suraj din yayi wa Nafisa .
Yanzu sun gano takon ta Suraj ne zai dinga mata hukunci irin nasu na sojoji na rashin imani sun shiga gida nan suke bada labarin abinda ya wakana a gidan.
Mama taji dadin har cikin ranta ko banza Suraj ya kwantarwa Fati incin ta yau wanda inba shi din ba, ba wanda ya isa yayi haka a zauna lafiya da ita tunda tayi niya.
Maganan mommy ne ya dakatar da ita da taji abinda Nafisan ke fadi a lokacin shigan su gida da take fadin wai babu rabon su Fati da yayan ta ga abinda maigidan ya bari a gidan.
Lalaima wanan matar tantiriya danta ya dauko mata ba kwai ba donge amma har take ikirarin cewa wai ba abincin su a gidan.
Wani zafi na bakin ciki irin wanda iyayye ke ji a gamay da diyan su idan sun yi abu ba daidai a cikin alumma wanda sai uwa ko mahaifi suka san da irin zafin da mama taji a lokacin.
Haka dai ta shige daki a dadafe bakin ciki da takaicin da matan dan nata ke kumsa mata a zuciyar ta yayi yawa kuma dan nata ya sani amma bai iya daukan wani mataki akan hakan.
Wunin ranan haka suka kare shi da maganan Nafisa wanda hakan ba bakon abu bane agurin anyi sau tari da yawa sai dai na yau din ya banbanta da sauri don ta fito ta nuna masu karfin iko da izan da take dashi a cikin kan dan nasu .
Wanda suka haifa suka tarbiyartar da hannun su kuma ya tashi da tarbiya suke saka ran samun farin ciki a wurin shi kamar yadda duk wasu iyayyen ke fata ga diyan su idan su samu
Amma lokaci guda Nasifa ta shiga rayuwan dan nasu wanda ya watsar da duk wani rayuwan farin ciki da suke hasashen samu daga gare shi.
Gashi a yanzu yana a cikin ganiyan samun duniyan shi wanda bai zauna ba tsaye yake wurin neman na kanshi a rayuwan wanda ba komai yakawo hakan ba sai addun mahaifa da yawaita ta sadaka akan diya yake bibiyan shi a yanzu.
Don a baya in zata iya tunawa bata da aiki sai yawai ta sadaka fiye da kowa a gidan in anyi magana sai tace ba neman duniya nake wa kaina nemawa na baya nake madogara.
Ga yawan taimakon na kasa da ita tundai idan ance yaro maraya ne sai mama tasan yadda takai alherin ta ga yaron ko ta saka yayan ta suyi mai alheri daga abinda suke dashi na jikin su mai kyau wanda zai farauta ran yaron da za a ba abin.
Don Allah iyayye mata mu kula kada muyi sakaci da wanan dama akan marayu da muke gani zaki iya dafa kan yaro maraye zai ji dadin hakan da kikai mai har a cikin ranshi.
Bawai duka maraye bane zai bukaci taimako wasa ma da dariya a gare su sadaka ce dan abinda zai farauta masu rai sadaka ne Allah ya bamu ikon yi ga maratun dake a kusa damu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: 🧠MIJIN BUZUWAðŸ§
3ï¸âƒ£
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
NOVEL DIN NAN NA KUDI NE BIYA DARI UKU KO KATIN DARI UKU TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI KIRA TA WANAN LAYIN 09026931792 KO 08036959257 ASHA KARATU LAFIYA YAN UWA.
Tsaye take gaban mirrow tana gyara rigar da ta sa a jikin ta na tampha wanda akai mata dogon riga dashi mai wani launi kamar jikin damisa brown colour.
Dinkin mai dan kwala sai da wuyan rigan V neck akayishi wanda yasa gaban ta ya fito dakyau daga cikin rigar kasan rigan ma an bude shi free yadda zata iya walla kafafuwan ta ba cikin matsuwa ba.
Turare ta dauka ta feshe jikin ta dashi ta juya ta dauko gyalen ta dake saman godo gefe ta fesa mashi turare ta mayar a hand bag din ta dan kwali ta dauko ta dan daki lokaci tana daurawa take fuskanta ya fito tsonen a jikin mudubin.
Duk wanan shirin da take yi ranta ba dadi don bata son zancen zuwa kaduna a zuciyar ta tafi son tayi rayuwan ta a gidan ubanta dake a cikin garin Minna.
Inda gidan su yake a kwangila road asalin su su hausawa ne zamane na kakan ni ya kawo su garin minna har suka zama yan ainihin gari baza kace su bakin gari bane yanzu don kowa nasu anan aka haifeshi.
Daga wajen gidan wanda irin ginan da can bayane na siminti wani murya ya kirata da fadin Khadija kina makara fa a cikin irin hausan mutane Niger shiba kananci kuma ba hausa pure ba do ya dan hade da surkin harshe.
Muryan Khadija ne ke fadin mama shiri nakeyi gani fitowa yanzu da sauri ta karasa shirin ta jawo dan trolley din da ta sa tufafin ta a ciki tare da rataya handbag din ta a kafada ta fito waje.
Kallon ta mama tayi wace zance a wurin ta khadija ta debo kyau da na saba kafin in ga mahaifin ta farar mace ce doguwa yar kabilan gwarin may kunkele dake a cikin minna din.
Kallon yar nata tayi tace kin fi son ko yaushe kiyi tafiyan marance mama nina fison in shiga da yamma yafi ba wanda yasan zuwan ka sai dai a ganka.
Maimakon tayi haraman tafiya sai ta ja kujera roban dake gefenta ta zauna kallon ta uwar tayi tare da fadin yaya haka kuma ?
Banbara nake jira na aika a sayo dashi zan tafi bana son in mising din shine idan naje ke dai yanzu na gane baki son zuwa wurin yar uwan naki tunda kika girma kika fara karatun jamia .
Ta dan ya motsa fuska mai kama da sallo ko yanga wanda ba haka bane kusan yanayin yan garin ne haka suke maganan su da kamar sallo da yanga tace ni nafison in yi hutu na a gida.
Amma ita ya Amina kullun sai tace sai mutum tafi wurin ta hutu yanzu kuma ba da bane ban son ina missing din gida sosai murmushi kawai uwar tayi don tasan halin yar nata.
Ba ajima ba mahaifinta ya shigo gidan yana ganin ta yace a Khadija an fito ke nan eh baba zan tafi hannu yasa ya fara laluban aljihun shi sai ya fito da dubu biyu ya cire guda ya miko mata.
Kai ta girgiza mai tace baba ka barshi kawai kudin da anty ta turo min zai ishe ni na gadone a daidai lokacin yaron da ta aika ya sawo mata banbara ya iso da leda a hannun shi yana mika mata da canjin karike canjin tana bude ledan ta debo banbaran ta mika mai ta mike tana gyara jakkan ta yaron ya taima ya fita mata da kaya ida ta tare Napep zuwa Abdulsalam garej .
Tana isa saura mutum daya ta biya suka shiga suka kama hanyan garin kaduna yamma lis suka shiga gari lokacin kuma akai hadarin marancen nan da Nafisa ta dawo ta samu Napep din da zai kaita unguwar da yar uwar nata ke aure wanda kusan rabin zaman ta a baya a nan tayi shi sai data girma ta koma gida karutun da take yi Abuja yanzu shine silar mayar da rayuwan Khadija gida Niger state.
Tun ranan da khadija tazo kaduna bata fita ba tana daga daki sai falo indan ta fito ko kuma ta shiga kitchen tayi masu girki a gidan.
Yau da yamma ya Amina ne ke kwala mata kira tana zaune tana cin banbara da tayi worming din shi kamar yanzu akayi shi bai kwana ba.
Ya Amina gani ta fito tana fadi cikin ranshin kallon fuskanta don Allah zo ki shiga gidan su mommy ki karbo min sako tace yanzu in tura a karbo min.
Fuska khadija ta ya motsa tace ni ban shiga ba tunda nazo banje na gaidasu ba Amina tace wai khadija may ke damun ki ne haka ?
Ke a rayuwan ki sam baki son shiga jamma a ban san inda kike dauko wanan rayuwa naki ba haka cikin bacin rai ta juya dauko gyalen ta kayan da tazo dasu garin ta kara sakawa a jikin ta.
Yaran anty nata biyu ta, ta kira su rakata gidan da aka aike ta din fitowan su bakin get din gidan yayi dai da zuwan wata mota a guje ta watso masu ruwan dake kwance a wani dan rami saman hanya.
Cikin bacin rai Khadija ta dago kai tana fadin you are very stupeid bakya gani ne kika watso ma mutane ruwa haka.
Horn kawai Nafisa tayi masu ba tare da ta tsaya khadija tabi motar da hararan takaici tana dan kakabe riganta da ruwan ya dan taba a lokacin.
Raina yayi matukar baci haka muka doshi gidan mutane ina mita wani saurayi dake tafe a bayan mu naji yace yar iskan buzuwan nan ne haka take tuki kamar mahaukaciya wallahi.
Dan juyawa nayi na kalli mai maganan nace sannu yace yawa bata dai zuba maku ruwan sosai ba ko nace kadan ya taba mu inayi har lokacin ina kakaban ruwa a jikina.
Gidan muka shiga wanda har lokacin raina a bace yake da buzuwar da naji saurayin nan yace min da sallama muka shiga gidan.
Wanda sai kawuce kofan falon gidan kabi wani dan siririn hanya da zai sadaka da cikin gidan da muka shiga wanda babban gida na ba yau bane farkon shigana gidan don duk zuwa nayi sai anty ta aike da gidan ina shiga akai akai yanzu tunda na girma bani shiga idan nazo sai da wani dalili.
Sallama mukayi inda kofan uwargidan ne fara isa sai na mama daga can ciki sai kuma wasu biyu dake kallon nasu din na mommy dana anty Amarya ke facing din su.
Hajiya ummi da yaranta nake jiyo hayaniyar su daga kofan part din ta na dan matsa daga kofan dakin ina gaida su dakyat aka amsa min ban tsaya ba na wuce.
Lekowa akayi daga dakin ummi don ganin mai gaidasu din da bai shigo ba bata gane ni ba alokacin har nakai kofan mama shiyasa ban son shiga wanan gidan don yawan dake garesu kuma sai kabi kowa kagaida shi dole don hadin kai irin na matan gidan.
Koda baka gaida mutum ba wanda kaje wurin shi zaice dakai ka ko gaida mutanen gidan sanin haka danayi yasa na fara binsu daga daga ina gaida su.
Dakin mama ma a kofa naja na tsaya ina fadin ina kwana mama ta amsa min daga ciki tana fadin waye shigo mana ciki.
Dole na shiga daga cikin dakin tare da kara gaida ita inda nakai gwiwana duka biyu a kasa irin gaisuwan mu na mutanen Niger.
Daga kuryan dakin ta aka fadin muryan wa nake ji kamar khadija Adamu da sauri mai maganan ta fito falon ida nake wani irin ihu ta sake a lokaci daya tare da kwalawa binta kira tana fadin ga khadija Adamu ashe tana garin nan mukayi maganan ta jiya.
Murmushi nayi ina dagowa daga gaida mama da nake nan suka shiritar dani nace anty ta aiko ni wurin mommy.
Bayan nagaida amaryan su ne na wuce zuwa dakin mommy ta tareni da fara anta mun dade tana jana da hira wanda ni ban iya sake jiki dasu muyi hiran sosai saboda mutunci da girma da nake gani a idona.
Sakon ta dauko min na fita mukai sallama dasu nan suka rakoni suna dan taka min in baki mantaba mai karatu na fada maki a nan kaduna nayi rabin rayuwa na.
Kamar abin tsokana wanan motar dai ne na dazun ta dawo a guje ta kara yin facali da ruwa a take nace wanan wani irin iskanci ne wai haka ?
Har motar ta wuce sai ta dawo baya a hankali zuwa gare mu a lokacin zainab ke fadin Nafisa ce fa ta dawo zai tai muna cin mutunci kila taji zagin da khadija tayi ne.
Gab damu ta tsaya tare da sauke glass din motar wata farar mata nagani ciki tare da wata zaune a gefen mai zaman banza.
Tace wace yar iska ce cikin ku take zagina shiru naji sunyi suna soke kai kasa nan san lokacin da nace mata kece dai yar iskan da baki san darajan mutane ba kika gudu da mota haka a wulkance cikin gari kamar yar koyo.
Ke tafadi a zafafe tana kokarin bude kofan motan da sauri naji su Binta da zainab na fadin yi hakkuri anty bata san ke bace .
Cikin zafin rai nace ke wacece da zaki watsa ma mutane ruwa kice kada ayi maki magana wallahi ko diyar shugaban kasa kike sai nayi maki magana .
Karasa fitowa tayi daga motan tana fadin ke yar gidan uban waye a garin nan take raina ya kara baci nace kedin yar gidan uban waye da