MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   125 / 144

372K to 375K   out of 431K words

dan sa ya sake zuwa safe mu gani falon muka fito dukan mu muka zauna.
Ina kallon yadda take murzawa yaron albasa a jikin shi da kyau tace insha Allah zai samu sauki don ciwon yara bai wuce mura da ciwon ciki ba wani lokacin.
Sai da ta gama shafe shi tare da shaka mashi hannun ta a hannci ya shaki gafin albasan sosai ta mayar mai da tufafin a jikin shi ta bashi magani.
Shatu ne ta fito daga dakin da take dauke da Sadiya tana fadin yar nan taki barci hajiya tun dazun nake lalashin ta taki shiru.
Tana kokarin miko min ita na rasa yadda zanyi da raina a loacin karban yar nayi daga hannun ta Altine tace a shafa albasan mata ita ma mu gani ai.
Nace Anty lamarin Sadiya ne akwai wuya kin san ita komai nata dan ka,ida ne jikinta ma har yanzu bai tsaya daidai irin na yara ba.
Tace ban ita nan a shafa mata tafi dan uwanta ne da aka shafa mai ta karbi yarinyar daga hannu na tace laraba ta dako mata wani albasan ta shafa mata.
Shine muka samu yaran sukayi barci bayan an masu na gargajiya a gida ko da gari ya waye laraba tayiwa su yan biyu wanka ta kara shafa masu albasan a jiki dukan su aka goya su.
Ya kira wayana har sau biyu ban samu dagawa ba don ban kusa da wayan a lokacin na shigo na samu miscall din.
Wanka nayi na shirya tsab na fita mai falo din gidan dake a gyara tsab sai kamshi yake saboda gyaran dayake samu yanzu.
Nan suka fito suka samay ni muka zauna gaba dayan mu sai laraba dake girkin rana wanda zamu ci take dan tashi lokaci lokaci.
Hira dasu yana dan rage min damuwan dake raina wani lokacin sai dai hiran tasu ce kamar gugan juna don kowa a hasale yake da dan uwa.
Dan gara laraba da Altine akwai dan shiri a tsakanin su sosai daya da wani abu mukaji dirin motoci a hara ban gidan ban kawo shi bane sai da ya shigo.
Da mamaki muke kallon shi ba wanda ya tsamaci dawowan shi a ranan don mun dauka zai dan jima a can ne sannu mukai mai sai dai duk da yana amsa muna hankalin shi yana gun sadiya dake kwance tana kuka.
Ya nufi wurin yarinyar yana fadin yaya kuka barta tana kuka haka yana kokarin dauko ta zuwa jikin shi.
Altine tace yanzu uwar ta aje ta tayi sallah shine ta fara kuka ashe tayi kashi Shatu taje hada ruwa ta wanke mata ne.
Yace shine za a kyale ta tana kuka haka kuma ba wanda ya dauke ta ya juya inda nake yana fadin shiyasa na dawo don hankali bai kwanta ba kan yarinyar nan.
Yanzu ai sai ka kula da ita tunda ka dawo din don hankalinka ya kwanta ko yace wani irin magana kike fada min haka shiru nayi ban bashi amsa ba ya dan kura min ido zuwa dan wani lokaci sai ya kawar.
Ya aje yarinyar ya fara tafiya yace ina twins ban bashi amsa ba Altine ce tace suna lafiya jiya dai ne Al,amin baiji dadin jikin shi ba.
Yace yaya akayi yanzu yana kallona Altine ce tace mai jiyan dai an bashi magani sai kuma Laraba ta shafa mai magani sai jikin yai sanyi.
Baice zai ga yadon ba ya wuce zuwa sama yayin da ake shigo da kayan shi ciki nidai ina zaune a inda nake imani ya cika ni.
Altine tace lalai tsohon nan nasu bai nemi zaman lafiya da iyalin shi ba irin wanan halin daya dauko yana sa mutum sanyi ga abinda yai niya akan yaran.
Ban samu tofa komai a zancen da takeyi sai sauke ajiyan danayi ina mikewa daga inda nake daki na na shige ina shiga Laraba ta kawo min Al,amin wai jikin shi ya fara zafi.
Maryam na kira ina fada mata tace tunda an fada mai bari muga abinda zaiyi idan bai dauki mataki ba sai mu kai yaron asibiti.
Sai wani lokaci ya fito ya fice daga gidan dama nasa Laraba ta kula min da hakan yana ko fita ta sanar min na kira maryam din tace in shirya mu je asibiti da yaron.
Mun kai yaron asibiti sun duba shi suka rubuta maganin da za a bawa yaron sai da na sayo na dawo gida ina hanya naji ya kirani na dauka.
Kina ina ne nace hanya sai naji ya kashe wayan ba tare da yayi magana ba yana kashe wayan nabi wayan da harara na aje gefe na.
Na dawo gida dauke da yaron a kafada na nashigo gidan hannu daya dauke da ledan maganin da na sayo part dina na shiga don babu kowa a falon babba.
Ban jima da dawowa ba ta shigo dakin yana fadin ina kika fito na shigo na samu kin fita ina kokarin dago yaron dake kuka saman gado nace na kaishi asibiti ne.
Duban yaron yayi ya karaso yana taba yaron yace may ke damun shi ne wani haushin shi nake ji a raina ban iya bashi amsa ba sai kokarin dura ma yaron magani da nake shirin yi.
Wani tsawa ya daka min yana fadin bake nake tambaya ba kinyi shiru dago kai nayi nace ni ba likita bace don haka bansan abinda ke damun shi ba.
Naci gaba da bawa yaron maganin da nakeyi din ba tare da na kula shiba yace ok wani zance kike so ke nan kuma.
Har ya kai kofa nace zancen iyakar ka kace in tafi gidan mu nima tunda ban ba diyan ka kulawa yadda kake so ba ko ?
Juyowa yayi yace shi kike shawa wanan kamahin dama don kawai na tambaya akan sadiya nace bazaka tambaye ni ba ai tunda bani ce kaba kula da ita ba.
Duk abinda zaki fada ki fadi nasan haliku na mata duk halin ku dayane a wurin kishi ko kuma don kawai na tambaya shine abin wani zance can ?
Ya fita sai da nagama dura ma yaron maganin nayi tunane idan banyi da gaske ba akwai abinda ke shirin faruwa akaina da yaran nan.
Don yanzu hankalin shi na gurin yaran Nafisa kawai kamar su kadai ne yara a gidan yanzu dayake jini ya dawo min sai ban daga ba don jin lokacin sallah da yayi.
Ina ciki ina hada abinci a dinnng din shi ya shigo gidan na gama na dauka ya shige ashe yana tsaye yana kallo na.
Ina gamawa na juya zan sauka kasa naji yace ina kuma zaki yanzu nace part dina zan koma sai naga ya matso inda nake yace Deedar may yasa kike son bani matsala ne yanzu ?
Dagowa nayi na kalle shi ido cikin ido nace wani abin na sake ma yanzu kuma, ko da yake kasan duk halin mu daya wurin rashin kirki ai.
Murmshi yayi yace kin canza min gaba daya yanzu na rasa may ke damun zuciyar ki a gidan nan gaba daya kin canza dabiun ki gare ni.
Nace dama haka nake ai ko ka manta ne jawoni yayi zuwa jikin shi yace muje ki bani abinci kamar yadda kika saba bani a baya.
Da ke nan yanzu ka san ina da yaran da nake kulawa ma,ana yarana dana haifa don suna bukatana a kusa dasu.
Saboda yaran ne ba zan samu kulawanki ba yanzu nace koya min akayi hakan yasa na iya don kowa nasa ya sani murmushi yayi yace ki ban abinci dai yanzu don yunwa nake ji .
Table din na nufa na fara zuba mai abincin kamar yadda ya bukata yaja kujera ya zauna yana kallon yadda nake zuba mai abincin.
Nagama zan wuce yace ki zauna in gama mana kamar zanyi magana sai kuma naja na zauna a daya daga kujerun wurin.
Kura ma kofa ido nayi hankalina ya tafi ga tunane yace gaya min mai ye matsalan ki danine yanzu da ya kamata ace na samu jin dadi a wurin ki.
Maimakon in magana sai na fara kuka wiwi nace nagaji da wanan zaman haka nagaji nima ka sauwaka min tun yanzu yafi min alheri da zaman ukubar da nake yi a nan.
Shiru yayi baice komai ba sai abincin shi yaci gaba da ci hankali yana sauraren kukan da nakeyi.
Sai atukar mamaki maganar dana yi yake a zuciyar shi jin baiyi magana ba yasa na mike zan wuce sai lokacin na ji yace ki fada min laifin da nake maki har kika iya furta hakan a gare ni gabana kuma.
Baka san halin da ka jefa rayuwana a cikin gidan ba a yan kwanakin nan saboda fitinar gidan nan bankai lokacin daukan wanan kwaram din a lokacin nan ba.
Kasan girman nauyin da ka dauka ka dora min duk kokarin da nake a gaban kowa kake nuna mani rashin godiyan ka baka damu da damuwana dana yara na ba ina tsoron abinda nake gudu tun farko ya faru dani a gidan nan.
Mutum ya tara yara dashi dasu su koma banza a gurin ka gara tun wuri a rabu don ba zan iya daukan wanan wullakancin ba da kurciyana haka.
Ajiyan zuciya naji ya sauke yace yanzu na fahinci kina nufin ban ganin kokarin ki wurin kyautatawa su Ihisan da sadiya.
May zai sa inga rashin kyautatawan ki gare su bayan uwar da ta haifesu ta tsalka ta barsu iyayyena sun kasa rika min ke da kika zauna min dasu ba tare da gardaman komai ba ince baki kyauta min ba kuma.
Ko kinga na nuna bambaci akan yara nane da kike fadin ba zaki dauki wullakaci ba akan diyan ki kasa magana nayi ban iya furta wani abuba.
Yaci gaba da fadin wace tayi min haka ta yaya zan kuntata maki idan ban gode maki ba kin san yara nan kanana ne suna bukatan kulawa don su manta da uwar su a ran su.
Hawayen dake zubamin nake kokarin gogewa da bayan hannu na ina nazarin magananganun da yake min na dadin baki irin ta maza.
Karshe naji yace kiyi hakuri ke uwace yanzu a gare mu kada ki yarda wani yaga sarewan ki tun yanzu a kan gidan nan har a raina maki wayo kan hakan.
Kada ki dauki abinda nakewa yaran da wani manufa na daban kulawa ne kawai wanda ya dace su samu daga uwar su da basu samu ba yasa nake hakan.
Runtse idanuwa na nayi na sauke ajiyan zuciya ina mikewa zan bar wurin naji yace ki zauna mu gama maganar mu kada ki fita haka a fahunci kinyi kuka anan su dauka wani abin ne ya faru tsakanin mu.
Komawa nayi na zauna inda na tashi banji yai magana ba har wani lokaci na dauko na dan kalleshi naga ya mayar da kanshi a saman masangalin kujera yana tunane.
Jikin shi yai sanyi da maganan da na fada farko yasan kawai na kyaleshi ne da kamay kamay da yake min din amma a gaskiya yasan ko waye dole yaji zafin abinda ya nuna min kan yarana
Bai taba kawowa a ranshi nima yanzu na haihu a gidan kuma rashin ba yarana kulawan da ya daina zai iya haddasa wani a zuciyana ba kan yaran balle yai tunanen da yake bai dace ba a fili har kowa ya fahince shi.
Sai yanzu da nayi wanan maganan yake nazarin wanan abin zai iya jawo matsala sosai a tsakanin mu har abin ya shafi yara a gaba.
Gashi tun yanzu shakuwan da muka fara samu a tsakanin mu ya fara raguwa don yadda nake nuna mai din.
Wasu hawaye ne na bakin ciki naji sun kara zuwa min lokaci guda ina kokarin mayar dasu a idona.
Naji ya sauke ajiyan zuciya yace kukan nan da kike haka yana daga min hankalina idan hakkurin dana baki bai gamshe ki bane ki fada min in akwai wani matsala ne sai in sani.
Na dago na dan kalle shi nace rayuwan gidan nan gaba daya ba tsari a cikin sa nike nan a haka zan zaune a cikin kuncin miji dana kishiyoyi ko ina ba dadi.
Mace bata ganin fuskan miji a farin ciki taji dadi ko miji ya zauna da iyalin shi yaji damuwar matar shi kullun sai a dan kuraren lokaci za a zowa mutum sai nayi shiru.
Murmushi yayi yana fadin ina sauraren shi wanan ne kawai damuwar taki a gidan nan ko da saura don ina son in sani ida nake da gyara in gyara nan gaba kamar yadda kike so.
Don wanan kalamin naki naji shi har cikin raina da kika iya budan baki kina ikirarin ke ba zaki iya zama ki reni yaran ki a gidan nan ba.
Ban taba tunanen jin wanan maganan a gareki ba khadija bana jin dadin ganin ki a cikin takura hakan sai inga ban maki adalci ba ban kuma yiwa iyayyen ki ba suma.
Don Allah ki fada min duk damuwan ki dani a gidan nan a shirye nake da in gyara matukar bai saba ma addini ba a gidan nan.
Khadija abinda baki sani ba shine zama dake ya fadakar dani abubuwa na rayuwana da dama da na rasasu abaya a matsayi na namijin mace fiye da daya a gidana.
Ki yarda dani deedar bazan taba cutar ki ko wani naki ba balle diyan dana haifa da zufana don haka ki fada min komay ye damuwar ki kikuma bani second chance da zamu gyara matsalolin gidan nan da kike ganin tauyewa ne a gare ku.
Ajiyan zuciya na sauke don jin yadda yake kalaman shi a gare ni a cikin tausasawa ina jin zuciya ta tana min sayin radadin da nake ji nasa din da farko.
Tunane nake a raina may zan fada mai kuma wanda yai wanan maganan gare ni haka may yasaura in fada mai wanda shi bai san shi akan iyalin shi.
Kallona yake ban sani ba ganin na zurfafa ga tunane nima ya dan hura min iskan bakin sa na bude idona na sauke a kanshi.
Saurin kawar da fuskana nayi gare shi ina sauke ajiyan zuciya yace ke nake saurare deedar nace a hankali ba komai indai zamu samu kulawan ka a matsayin iyalin ka ya wadatar min ga komai.
In dai wanan ne kawai damuwar ki a gidan nan kisa kin samu dama don karatun kine da lalurar ciki yakawo hakan amma kuma nima fa an rageni a gurare da dama kin kuma sani.
Kallon shi nayi da saurin don jin abinda ya fada din yace yes nima indai wanan ne sai ince ni aka kuntatawa don ba a bani kulawan daya dace sai an fara ai min rowa kuma daga baya.
Murmushin karfin hali nayi nace da wanan bataliyan buzayen na gidan ka kake son a baka kulawa komai mutum ke yi idon su akan shi yake.
Murmushi yayi yana mikewa zuwa inda nake yana fadin yanzu ai bataliyan ki suka rage a gidan nan kadai ko su yaya zakiyi dasu kuma ?
Shiru nayi na dan harare shi yace kinyi shiru bakice komai ba nace wanan ai ba su saka ido irin wa yan cen.
Dukawa yayi daidai inda nake zaune yace wani iri naji har cikin raina kamar mai rada yace kin san may kai kawai na girgiza mai khadija ke kadai ce matar da zan zauna da ita muyi magana ta fahinta har mu fahinci juna a natse babu wani hayaniya a gidan nan.
Kalamin ki na yanzu sun sakani jin kunya kaina da nauyin ki a idona ki gafarce ni deedar nasan ban kyauta maki ba har ga Allah kin fada min yaro baida lafiya ban kula ban duba shi ba ni kaina ban san abinda ya dauke min hankali gayin hakan ba.
Ya kara dukowa gab dani yana fadin kiyi hakkuri ki tayani da addua duk da nasan kina min amma ki kara kwanan duk abinda nake Nafisa sai yaran ta nake gani a idona.
Wani iri naji gabana ya fadi sai dai na dake hakan a cikin raina yace na san kowa cece Nafisa nasan ba zata barni in zauna lafiya wanan tafiyan nasan tana can tana shiri akaina sosai fiye dana farko.
Cikin karfin halina nace mai idan sihiri kake tunanen tanayi shi din ma takeyi don duk wanda ke hada wanin Allah da Allah ya zama mushirki.
Kai may zai hana ka dage kana da sani gwargwado na addini yaya idan ka dage komai zata dauko maka akan ta zai koma.
Maganar gaskiya kana da rauni a gurin tsayawa kayi addinin ka kafi bada karfi a girin neman duniya wanda duk abinda ka samu iyakarshi a nan duniya.
Sai nake ganin harda sakacin ka gurin bata dama tana wasu abubuwan da takeyi a gidan nan kiriri zaka kama ta da laifin da ya shafi haka amma babu wani matakin da ka taba dauka kwakwara a kanta don may kuwa baxata ji dadin ta mai da kaimi ga sherin da takeyi ba tunda ta dauka shine mafita a gare ta.
Ka kafa mata tsauraran matakai ka dage gurin ganin addini ya wanzu a gidan ka dole ko batawa Allah ta rage wasu abubuwan da take yi din.
Ka duba yadda Alhajin ku yake tsaye a gudan sa bai

125 / 144

Chapters