MIJIN BUZUWA complete Hausa Novels.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   98 / 144

291K to 294K   out of 431K words

mussanman ma idan mace tana da ciki.
Yana matukar tausaya mata sosai don acewar shi bakanta wa mace mai ciki yana jawowa yaron dake ciki matsalane.
Har wanan lokacin babu wani dan uwan sa da yazo daga kaduna duba su Nafisa din don Abba yace ba wanda zai sake zuwa harka idan na Nafisa ne gidan shi.
Sai lokacin kumane abin ya bata mata rai take yawan korafin akan haka tana fadin dama nasan ba,a sona da kai tunda gashi har na haihu ko dan aikin gidan ku ba,a turo min ba.
Yakance da ita laifin wa da suke zuwa dubaki kina masu wullakanci su ba zuciya ke gare su ba da zaki dinga koje su suna biye dake.
Dama don ni suke zuwa yanzun kuma sun gaji sun ba kan su lafiya ga irin wullakancin da kike masu din don haka kada kiga laifin su.
A gun maryam na fara jin wai wani sati zasuyi tafiyan su nai mamaki rmtare da tambayan ta ina taji wanan magana haka ?
Tace min a bakin da baya karya taji don har angama shirin tafiyan su yanzu haka lokaci kawai ake jira sai ban dauki maganan da wani muhinmanci ba a raina.
Tunda nasan da gaskiya ne da ya fada min ai sai shirin sallah da aka fara inda yasa in mai list din abubuwan da zamu bukata da wanda zai aika gidan su.
Banyi sanyi a gwiwa ba na zauna nayi list din duk abubuwan da yace din nayi zaton zai rage daga ciki sai banji yayi korafin ko daya ba sai cewa da yayi zai min kari a sama koda bukata hakan ka taso.
Daga haka muka bar zancen sai bayan kwana biyu ne ina zaune naji alent ya shigo min na duba naga irin kudin da ya turo min ga account kirasa nayi ko bani yai niyar turowa kudin ba yace shiya turo idan ya dawo gida zai min bayanin komai.
Bayan ya dawo gidane Yusuf ya zo sunyi buda baki ya wuce mun shiga kwanciya yana zaune yana aiki a laptop di yace dazun kinga kudi ko ?
Nace eh sai dai bansan ko na may ba kudin yace zancen list din da nace ki min shekaranjiya ne sune na turo maki don jibi zamu fita da yarinyar nan zuwa india a dubata.
So kiga banda wani time issashe da zance zan leka kaduna kuma tun da tafiya ya kamani tunda ya fara maganan bance tak ba har ya gama nace Allah bata lafiya na gyara kwanciyana .
Yace baki ce komai ba mana ina magana kinyi shiru nace bayan Allah ya bata lafiyan dana fada kuma may kake son ince kuma ?
Murmushi yayi yace at list ai zakice kudin sunyi ko ba zasu isheku ba har in dawo ko nace zasu isa din ai daga haka bance komai ba yakara cewa babu ko Allah ya dawo damu lafiya ?
Baka so in fadi haka ba ai daka fada min tun farko bawai sai yanzu da tafiya yazo kusa ana gobe zaku tashi.
Kai mata may kuma kike son in fada maki bayan wanan yanzu ba gashi na sanar dake zancen tafiyan ba.
Ban face komai kar kuma ace ina bakin ciki ko kishi akan za a kai yarinya wurin neman magani.
Ida ni mai halice nima da naba da nawa gudun mawar kaita asamo mata lafiya yarinya mai taimin ita yar mala,ilar Allah da ita nima kaina mai maganan ai ban wuce nan ba ga Allah.
Amma ai ya kamata ki muna fatan samun nasara kk dana fada maki yanzu din nace bayan wanda na furta idan bakina kake son ji kan haka bazakaji komai ba ubangiji Allah ya bata lafiya yasa aje a cikin nasaran ubangiji yace amin haka nake son ji tun farko.
Kyale shi nayi na kakaro ma kaina barcin dole kafin ya gama abinda yakeyi din sai nasari na yaji a bayan shi na fara barci.
Bai zauna ba washe gari tun safe da ya fita yana wurin fafitukar tafiyan su laraba ne ke tambayan shi nace kin san zasu fita gobe da yarinyar nan zuwa india nasan yana can yana shirin tafiya ne.
Bamu dade da magana ba ya shigo lokacin har an sha ruwa anyi sallah ko part din mu ya nufo yaran suna rige rigen gaida shi ya amsa ya samu wuri ya zauna anan falon.
Laraba ta gaidashi ya amsa ta tabaye shi ya mai jiki yace da sauki
Gobe in sha Allahu da safe zamu fita zuwa waje da ita da yardan Allah takama addua da fatan samun sa,a.
Ina kallon shi ya dan kalle tare da fadin madam ya gida kuma nace muna lafiya yace ce kun gani sai yanzu matsala aka samu kan pasphot din yarinyar ya dan kawo muna tsaiko.
Nace yanzun an gama komai ko yace insha Allahu yana mikewa tare da fadin to mama nasan da safe koda zan fita baku tashi ba.
Tace hakane ubagiji Allah ya kaiku lafiya yasa ai farar tafiya ya amsa da amin nace Affan kuyi sallama da Abba zaiyi tafiya gobe suka shiga ce mai Abba Allah yakai lafiya ya amsa da amin.
Sai da ya dan jima da tafiya na samay shi a dakin har yayi wanka yana cin abinci nace yau ina yayana yake baizo cin abinci ba.
Yace tare muke yanzu ya wuce gida ya huta don kowan mu ya gaji yau ina hada kayan abinci guri daya yake tambayana ba wani matsala a kara muna kudi ?
Nace ba kudi bane matsala ta ni don haka kabar kudin ka nagama hada kaya na shige nabarshi yana mamakina a gurin.
Sai da ya shigo ya kwanta naji yace ke may matsakar ki ne wai khadija nasan maganan serious ne tunda naji ya ambaci sunana in full nace bada matsalan komai illa a dinga bani hakki na a yadda ya dace ba amai dani wata bican ba cikin ku.
Sai da kuka gama shirya tafiyan ku ne zanji daga shanun talla wanan abin da kake min kai mun adalci ke nan yace shine kawai matalar taki.
Na kyale shi shima shiru yayi haka muka kwanta kowa da abinda ke a zuciyar shi hudu saura ya fara shirin tafiya ina jin sa na kyale shi har ya shirya sai lokacin ya tashe ni inyi sahur da ruwa da nake sha.
Nace zanyi dan ajima kadan kafana naji yaja tare da fadin ni zan tafi Yusuf yana waje suna jirana na bude ido tare da mikewa zaune nace Allah ya kai lafiya yasa aje a sa,a.
Yace amin ya dauki dan case din shi ya rataya bai dauki wasu kaya ba taee dashi ya tako zuwa inda nake yace ki kula da kanki da gida nace insha Allahu.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Tun tafiya shi ban koma barci ba karshe ma na tataro na dawo part dina sai dana dade ina dan kwankwasawa mama laraba ta bude min.
Ina shiga tana fadin masu tafiya sun tafi ke nan eh kawai na bata amsa dashi na shige ciki ban tsaya ba.
Na isa dakina kan gado na kwanta ban koma barci ba don lokacin sallah da ya gabato mamaki ne fal a cikin zuciya na da tunanen a haka zan zauna da wanan mutmin ba wani kima da daraja sai idan na biyan bukatane tsakanin miji da mata kawai.
May yasa zai min haka bayan ina zaman zama na a gidan mu yasa aka zarga mashi aure dani alhalin yasan matar shi ba bari zatayi ya zauna da wata mace ba a rayuwan su.
Duk wani abinda aka ce inyi na jan hankalin miji daidai gwargwado ina kokari yin sa don dai inga na jawo hankalin shi a gare ni.
Sai naga saukin daga wurin shi lokaci daya kuma sai abin ya kara birkicewa a tsakanin mu nace a raina wanan wani irin zamane haka.
Gaskiya sai aka kamar kishiya ta tsoron kishiyar ta ko mijin ta bazata iya mata komai ba idan tana iya shege a kan su da miji kamar yadda nake gani da da ban shigo gidan ba.
Sai nake ganin Fatine kawai ke kyale ta don haka ta samu wuri tana iya shage ban san cewa abin bada nan bane ashe da zaran miji ya goya ma mai iya shege baya dole ke ki zama yar bi a tsakanin su don a zauna lafiya.
Nace a raina ba komai yaje idan ma wanan matar tashi ce da yake rawan kafa a kanta nasan da wuya su kare lafiya a can din.
Ina cin wanan tunane ne agogona ya buka na mike na shiga bandaki na dauro alwala nazo na tayar da sallah.
Ina tsaka da sallah ne laraba tazo dakin ta tayar dani sai ta samu ina sallah ta juya ta fita ta koma falo don tafi zama a nan.
Na idar na dade zaune ina kai kukana ga Allah wanda yawan addua,a na yanzu biyu ne Allah sauke ni lafiya ya ban komay ke cikina mai albarka sai kuma fatan in ci jerabawa na dake gaba na yanzu.
Na dade zaune sai da gari ya haska sosai na tashi na koma saman gado na kwanta barci ya dauke ni wanda na jima inayin sa a dakin.

INDIA
Saun sauka lafiya basu tsaya neman masauki ba asibiti suka nufa direct daga nan airport din already an riga da an masu bucking din likitan da zai duba yarinyar acan.
Haka yasa basu wani sha wahala ba sosai sai dai wanda ba a rasa ba kawai a garin da ba naka ba idan kaje.
Likitan ya duba yarinyar inda ya tabbatar masu zasu iya mata aikin a wuein cibiyar ta yanzu sai na kai din ne zasu dan duba su gani idan zai yuyu ai mata shi yanzu saba da kankantan ta.
Gado aka ba su wanda uwar zata dinga shigowa bayan awa bibiyu tana bata nono tare da duba yar sai bayan kwana uku idan sun gama aune aune zasu yi mata aiki su rufe gurin da yake bude din wanda tun a Nigeria likitoci suka so suyi mata aikin uwar tace bata yarda da hakan ba sai dai suje waje.
Masauki suka nema wanda baida nisa da asibitin don samun saukin zirga zirgan su zuwa duba yar tasu dake cikin halin hau,ila,i yanzu.
Wanka ya fito ya canza kayan jikin shi i zuwa masu sauki da ya saya da saukan su indian don bai dauko wasu tufafin kirki ba da zasu zo don gudun wahala dasu.
Abinci yai masu odo aka kawo masu ga abincin ba wai dandanon shi ya mai bane cusawa kawai yake kada ya zauna da yunwa ga azumi da yayi .
Sai dai zuciyar shi yana cikin damuwa damuwar yarsa dake cikin wani hali sai kuma damuwa akan yadda muka rabu dashi ba a cikin dadin rai ba duk da na yi kokarin nuna mai da babu komai.
In ya tuno yadda ko rakiya ban mashi ba da zai bargidan ina daga gado zaune tankar ba wani guri zai tafi nisa da gida ba.
Ke nan kishi nake akan zuwan su ko fushine haka na duk da yasan da na fadi korafina akan rashin fada min da baiyi ba da wuri sai da tafiya tazo masu gap ya fada min.
Idan kishi nake akan ya kawo yarshi asibiti nayi hakan may yasa ban kishi akan su Affan illar cusa yaran da nake kokarin a gurin shi.
Ya kuma yi tunane zaman Nafisa a asibiti daga part dina yaran nafisa da yan uwanta suke dauko abinci suci ai duk da halin zaman da nakeyi da uwar su din don haka ba akan fita da yarinyar nakewa ba sai dai fushine na ba gaira ba dalili irin namu na mata nake tsira mai.
Don haka yace a ranshi bari yaga iya guduna ba zai kira ba sai idan nice na nema shi ya kwanta yana kokarin share zancen a ranshi.
Yusuf kawai ya kira ya sheda mai isar su sai kuma bayanin da yai mai na abinda likitoci suka ce akan yarinyar.
Yayi mashi fatan samun sauki tare da nasara a guri aiki yace zai kira da safe yaji halin da suke ciki kashe gari sukai sallama ya kashe wayan.
Nafisa dake ta waya kwance a gefen shi sai hira take da madam akan wata da za,a hada ta da ita a india tai mata iso wurin wani bokan indiya .
Shiyasa ma ta nace akan sai sunyi tafiyan don tana ganin kamar a kasan ne sa,an ta yake don yanzu idan tana son mutuwar ta to tana son zamana a gidan AA.
Ko nawa ne zata kashe don ta riko kudi sosai a tare da ita wanda tasan zasu isheta shige da fice a kasan na indiya.
Zancen yar ta ma bai damay ta ba don bata ki yar ta mutu ba ta huta don tana ganin ba wani rayuwa zatayi ba a hakan da take ta manta da Allah ne mai yin komai yadda ya so.

KHADIJA
Ko dana tashi na yi mamakin barcin da nayi ranan don har sha biyu ya gwauta ko sai dai damuwar da na kwanta dashi ya rage a zuciyana don tun barci bai dauke ni ba na yanke wa kaina shawara gara inji da abinda ke gabana in fita batun su can.
Wanka nayi na fito falo na zauna laraba suna cikin daki da yaran ina jiyo hayaniyar su daga inda nake zaune tv na kunna wanda karan tv ya jawo hankalin su gare ni.
Sai gasu sun fito daddy ne sarkin son jiki yana fitowa ya nufo ni na dan rugumay shi a jikina tare da fadin daddy mama an tashi lafiya , ?
Laraba tace daddy ko sarkin rigima wanan tsohon naku akai fitina yanzu wai shi dole sai rigar dan uwan shi zai sa a jikin shi bai son nasa tun dazun rikicin da mukeyi ke nan dasu.
Nace ina jawo yaron jikina kyale mama kaji da Affan idan mun fita zan sawo ma sabbi kasa kai kadai bada Affan ba.
Haka yasa yaji dadi sai ya murmusa ya sake ranshi sosai naga kaman shi da mahaifin su da ya dan murmusa din da da Affan nake ganin suna kama da AA din kawai.
AA ne ya fado min a raina nace ko a wani hali suke ciki yanzu a can Allah dai yasa su dace ai wa yarinyar nan wani abu a can din da sukaje.
Mama ne take fadin yau kan kinsha barci ai zasu tayar dake nace don Allah su barki ki dan runtsa don ana son mai ciki tana samun barci irin haka.
Nace aiko na runtsa din sosai wallahi mama dama ga gajiyan jerabawan da nayi yana bina ban samu hutawa ba wanan zancen haihuwan yazo kuma.
Tace suna can dai ko a wani hali suke ciki yanzu ko kunyi waya da sune kiji ko sun isa nace idan bashi ta kiramu na samu lanban shi tace ba ai waya bai yi a tsakanin mu yanzu.
Tace hakane abin ashe ai dana dauka zai yiyu ki kirasu ki samay su a can da tasu nomban ta nan da suke amfani dashi ai.
Nace sai dole su sa na kasan idan sun kira mun samu layin su da suke amfani dashi can ne zamu samay su.
Tace amfanin bokon ke nan ai dariya nayi nace mama ke ko dan primary din nan bakiyi bane ashe tace wa ya bamu wanan gatan a kauyen mu lokacin mun ai mata basu karatu sosai har zagin masu yi din akeyi a lokacin.
Nace ikon Allah gaskiya da anyi abu wanda diya matane akafi cutawa ga rashin barin aikararun din don su maza ai sunayi ba a faye sa masu ido ba kamar diya mace.
Wayana yai kara na duba hajiya mama na gani nace a fili yau hajiya ce ta kirani kuma wanda dama nice kwana bibiyu nakan kirata mu gaisa.
Na dauki wayan da sallama tare da gaida ita ta karba min da fara,a tare da tambayana yara da mama laraba.
Nace suna lafiya gamu tare ma dasu tace ki gaida mun su nace zasuji insha Allahu.
Dan shiru ne ya biyu baya sai can tace sai kuma nake jin wai mijin naku ashe sunyi tafiya zuwa kasan waje ne kai yarsu asibiti shine bai sanar da kowa ba.
Mamaki naji a raina nace wai may AA yake son ya zamane duk ya rude akan wanan matar tashi yar matsala.
Sai dai a fili cewa nayi mama kila tafiyan a bazata yazo mai don nima sai da tafiyan tazo gap ne na samu labari a wurin shi.
Yanzu khadija abinda yaron nan yake yana kyautawa kan shi dani ke nan sam bai dauke mu da wani muhinmanci ba a rayuwan shi.
Wanan bakar matar tashi tana kokatin sai ta rabashi da kowa nasa ta huta shine farin cikin ta ita.
To idan haka take so sai ta zuba ruwa kasa tasha don ta samu yaje tunda ita ya zaba akan mu sai yaje gata gashi mun bar mata.
Sai dai abinda zance dake shine ki kara hakkuri a zaman ki a cikin su nasan kinayi sai dai ince ki kara din.
Nace mama na gode sai dai don

98 / 144

Chapters