dan barin Nafisa a falo da nayi nasan kuma zata biyoni itama taji dalilina nayi mata hakan.
Sai dai har ya kusa kammalawa bata babu dalilin ta yasa na kara gaskanta da wani abu akasa wanda ni ban sani ba dayake faruwa a tsakanin su.
Yana gamawa na mike jikina ba kuzari yace idan kin hada kizo ki dan matsa min wuya na don yai min tsami yau sosai wanan kan ban san lokacin da nace haba yaya AA kafasan bani ce da alhakin yi maka komai ba a yau.
Kada mu shiga hakkin wata koni idan an min hakan ba zanji dadi a raina ba gaskiya don may kuma zan biye maka mu fasa halaka.
Yace kin fini sanin Allah ne khadija nasan maganan mai girma ce tunda ya ambaci sunana haka yau na bude baki da kyar nace na daiga ba zata ji dasin ganin haka bane idan ta shigo ta samay ni a nan din.
Zaman ta kikeyi ko nawa nace naka a sanyayye yace idan ba zaki min abinda na bukata ba to ki fice min don Allah ban son dogon magana yanzu.
Daukan kayan nayi da niyar fita yace ba zaki mun massage din ba ke nan dole na aje kayan hannu na na nufi inda yake gabana sai faduwa yake kamar wani zai kamani a lokacin
Dan jin nayi kafin in fara sai dai can na dora hannu na a hankali na fara mai sai naga ya gyara zama yana wani lushe ido sama kanshi ya nuna min ba tare da yai magana ba na kai hannu saman kan ina dan cakula mai a hankali.
Jin shitun yayi yawa yasa shi yin magana na dai ga kamar dole kike min kina iya tafiya yanzu yace yana mai sauke ajiyan zuciya.
Nace gaskiya kan a tukure nake tunda nasan ba hakkina bane yi maka haka yau don gudun zargi ina mun dade da gama wanan maganan .
Ai na dauka kina da fahinta amma tunda bayani kike son ji jeki zan maki bayani indan na shirya sai dai ba yanzu ba don kin gama bata min rai da gardaman ki nan.
Akan gaskiyana nake magana don ko ni ba zanso kai min haka ba kaga yanzu da Allah yasa ta shigo duk abinda ta fada a kan mu bamu da gaskiya ai.
Shiru yai min bai ce komai ba don ya matukar kuluwa da ni a lokacin dukawa nayi na dauke basket din kayan dana hada nafita daga dakin.
Kai ya girgiza bayan fitana tare da nisawa yace watau ita komai nata akan tsari yake ke nan da Nafisa ce dadin hakan zata ji sosai ba wani tunanen wani abu.
A falo na samay su zaune da yan uwanta ina fitowa tace Allah dai ya tsine wa mai satan kwana kiyi abinki yanzu lokaci ne gobe ko ance kiyi ba zaki gwada yi ba ai.
Ban kulata ba don dama nasan haka ne zai biyo baya don babu gaskiya ga wanan maganan saboda ta fimu gaskiya yanzu.
Ina shiga su Altine dake zaune suna hira tace kin dawo nace eh sai da nakai kayan kitchen na wanke na fito ina zama nace gaskiya dan uwan ki na son ya ja min magana in rasa bakin bada amsa.
Ya dai san yau banice da girki ba amma ya saka min dokan nice zan dinga bashi abinci ba tare da yai min bayanin komai yadda zan fihinta ba .
Yanzu gashi ina fitowa ta fara zargina tana fada min magana kan hakan dole na kyale ta don banda bakin bata amsa tunda babu gaskiya a ciki.
Maman biyu tunda kinga haka dole akwai wata a kasa gaskiya haka kawai da hankalin shi ba zai ce maki hakan ba ya kamata ki gane hakan.
Itama fa wurine bata samu ba da hakan zatai maki ai koda kuwa babu wani dalilin mai kwari zata so tai maki hakan Allah ne ya taimakeki ya doraki a kanta ai.
Don haka zagewa zakiyi yanzu ki nuna mai naki daman akan shi koda sun shirya a tsakanin su kin riga da kin kara kafa gwaunatin ki a zuciyar shi.
Ke dai mace ce mai ilimi ba sai na fada maki abubuwan da zakiyi ba yanzu dama naki ne a gidan nan ki fito da kalar ki ta gaskiya ga kowa na gidan nan ta yadda zasu fahinci rayuwan ki.
Akoma ana kyamatar ta acikin wana zuri,an ga baki daya kowa ya gane cewa gwaunatin buzuwa na kama karyane a baya tayiwa mutane.
Maganan Altine ya tsaya min sosai a raina don haka na fara neman mafitan hanyar da zanbi in nuna nawa hikimar data ce.
Ban dade ba na shige don in kwanta sai dai barcin yaki zuwa min da wuri yadda nake so sai can dare na samu yazo min duk da haka na samu tashi nayi nafila na mika bukatana a wurin Allah.
Washegari tunda ba school muke fita ba kitchen na fada na hada mai lafiyayen breakfast kafin wani lokaci na gama duk abinda zanyi.
Wanka na shiga na fito na shirya tsab dani falo na fito na samu sanyi ya hanasu fitowa daga daki tunda yau din san ina kitchen din.
Dakin na leka nayi masu ina kwana suna kwance tare da yaran sai dai ba barci sukeyi ba suna kwance ne suna hira nake fada masu zan hau sama a fito lafiya sukai min.
Na samay shi yana shirin jikin shi sai da na karaso inda yake nayi mai ina kwana ya juyo yana amsa min tare da fadin ya kuka tashi lafiya nace mai ina isa inda yake sa botturn din rigar shi.
Amsa nayi na karasa saka mai yana tsaye yana kallona na mika mai ties din shi yana sakawa na nufi gurin takalma na dauko mai wanda ya dace da shigar shi sai dana dan goge na aje mai a gaban shi.
Kallon takalman yayi yana dan murmushi nace ko takalman basuyi ma bane yace sunyi mana ina dai mamakin yadda kika san su zan saka.
Na sani mana tunda nasan shigar ka yanzu dan zama da kai a gidsn nan abinci na table yana jiran ka idan ka shirya.
Ai baki karasa shirya ni ba may ya saura na tambaye shi yace turare ko na juya gaban mirrow din shi na dauko turaren da yake amfani dashi idan zai fita na fara fesa mai a jiki.
Na gama tare da dago kai na kalle shi ni yake kallo na dan daga mai yatsu na biyu alaman yayi kyau yace ya gode na juya zan fita dakin ina kuma zaki yace yana kallo na.
Na gama abinda ya kawo ni ai kada in zake da yawa ba aikina bane taimaka maka kawai nayi ai juyawa nayi zan fice naji ya jawo ni zuwa jikin shi yana fadin ai baki isa ba sai kin karasa na fada maki.
Jin zafin yadda ya juyo ni nayi yasa na dan sake kara kadan nace wasshh mane ni yayi a kirjin shi yana fadin abu biyu zuwa uku ya rage maki ai kafin ki tafi nace.
Ai da ina zaton ka gama shiryawan ne ya sake ni yana miko min tsitsiyar hannun shi alaman in daura mai agogo a hannun nakama hannun na daura mai.
Bayan nagama nace sai na biyun kuma yace muje dining ki bani abincin tare muka fits zuwa dining din sai dana zuba mai ya fara ci ba dama in tafi don nasan wani matsala ne kuma yana cin abincin shi a tsanake har ya kare ya goge bakin shi.
Mikewa yayi nima na mike tare da fadin na ukun fa ko nagama ke nan yace da sauran ki saura nan yana mai nuno min gefen kumatun shi tare da fadin saura sallama.
Na gane nufin shi amma sai nace ba yanzu naga ka goge bakin ba ki ban kiss in tafi kina sani makara fa ba a kuma sanni da makara ba.
Kai na girgiza na nufi fuskan shi in mashi yadda yake so din ina kai bakina na sake mai kiss na juyo Nafisa na shigowa gurin.
Take ya daure fuska yana fadin may ya kawo ki nan may na fada maki akan part dina zaki fice muna ko sai na bata maki rai yanzu gurin nan.
Kamar zatai magana sai kuma ta juyo ta kalle ni ta juya ta fita rai bace nace haba yaya ko mai tayi maka bataci wanan hukinci ba daka dauka haka akanta.
Wani kallo ya watso min nace haba dai kuma a gabana kake fada mata wanan kalaman haka yaya babu kishiyan da zata so ai mata haka a gaban kishiyan ta fa.
Yace ni zan tafi sai na dawo a dawo lafiya nayi mai ina ci gaba da tattara kayan abincin zuciyana fam da tunane na dauko zuwa kasa.
Nafisa ce a main falo ta cika tayi fam da ita ina karasowa take fadin gurin ki ya cika an wulakantani a gaban ki yadda kike so.
Sai kijira zuwan naki ke ma don ba kyale ki zanyi ba akan hakan nace duk da ban san tsakanin ku ba idan kin tashi sai ki dauki raina tunda a hannun ki iko yake.
Kin gani nan nasan abinda nakeyi don ni ba jahila bace irin ki da za aiwa dan uwa abu inji dadi don nasan kambun namiji murdawa ne nima ban wuce haka a gare shi ba.
Amma ki sani umurni nake bi ni yanzu don mijinane a inda ya tsayar dani anan zan tsaya ban kari ko ragi don haka ki shiga taitayin ki ki lalaba ku shirya da mijin ki don ni ban san tsakanin ku ba yanzu haka.
Daga haka ban jira in ji amsanta ba na shige part dina na barta nan tana bakaken magana tana amaye zuciyar ta ko zata ji sanyi daga abinda take fuskanta.
Karyawa nayi na kwanta barci na samu nayi sosai sai zuwa sha biyu saura na falka tare da duban lokaci ga har rana yayi ke nan.
Wayan dake gefena na dauka ina dubawa sai naji ina son kiran shi a lokacin samun kaina nayi da danna mai kira wata zuciya tace mayvzan fada mai idan nakirashi din har wayan ya shiga ban sani ba ina can ina tunane a raina.
Sai muryan shi naji yana fadin Deedar ya akayi ne nayi saurin fadin ya aiki yace gashi muna tabawa lafiya kuke nace eh dama na kiraka ne in tambaya may za, a dafa maka yau.
Dan murmushi naji ys sauke yace duk abinda kika dafa min zanci don nasan mai dadi ne kamar mai dahuwan nace wani zance ke nan kuma.
Ai gaskiya na fada yau dai nasan ba cin haki ai ko don haka a dafa min komai yayi zamzam yadda zan gamsu dakyau don Allah don shekaran jiya am barni ina santi .
Sai anjima don naji kana son sakin layi ni bashi nakira ka fada min ba dana ni ko a yaushe zamzam nake don haka Allah yayi halittana.
Ai basai kin fada ba da zaki bar girki ki zauna ki samu hutu ai ni dakin kyauta min wallahi kin ga idan na dawo sai nima in raba in samu wanan ni,imar daki ka kwasa.
Dip na kashe wayan don kalaman shi sunfi karfin sauraren kunnuwana bai kokai ga aje wayan ba kiran shi ya kara shigo min sai da ya kusa katsewa na dauka.
Yace don may zaki kashe min waya ina magana nace wayan ne ai ya mutu yace to ya na hutar daku girkin komai za a kawo maku abinda zamuci da daren idan kuma akwai abinda kuke so sai ki min text kafin in bar office din nace mun gode na kashe wayan.
Ranan haka muka wuni muna hira bamuyi aikin komai ba don nace kada su girka komai a gidan basu dai tambaye ni ba suka kyale ni.
Da ya dawo ne aka shigo muna da ledoji kala kala lokacin ina daki laraba tazo ta kirani take fada min an shigo da sako don bata bude ko may nene sai idan nafito nace a bude.
Bayan na fito naga ledojin ne na umurcesu dasu bude nama ne na kaji sun sha hadi sai na rago da sauran kayan shaye shaye sai take away kala kala aka hado muna.
Ganin kayan sun muna yawa nasa laraba takai ma su Nafisa wanda na ware masu ita da Ihisan suka dauka na dauka zata bayar a dawo min dashi sai naga laraba ta dawo ba tare dasu ba.
Shirin tafiya buki muka shiga yi tun ana saura kwana uku mu wuce sai faman shiri muke part dina yayin da ita part din su ko a jikin ta.
Sanin halinta yasa ban damu da ita ba don zama muke ba mai shiga harkan wani a gidan ba ina kwana ba sanin halin da dan uwa yake ciki zama dai irin wanda bai dace ba ga addini.
Banda yadda zanyi don dole nima na koya na iya koda kuwa dan uwa zaiga abin cutawa dan uwa na har gara nima nakan dan tanka idan naga wani abinda bai kamata ba a gare su.
Ana gobe tafiyan mu ne ya kiramu a falon kasa kan tafiyan nan dai ta nuna ita bata san da zancen ba ai yace ba dole sai kin sani ba kamar yadda kika ce saidai ya zama dole duk wanda ke gidan nan yayi tafiyan.
Saboda haka ya saura gareki gobe karfe takwas zaku kama hanya ni sai alhamis ko jumma,a zan shi go idan Allah ya kaimu ban son jin komai ya fito daga gare ku kuje kuyi abinda ya kaiku ku dawo.
Ya bude briefcase din shi ya fara ciro kudi a ciki ya mika mata sannan ya miko min nace mu gode Allah ya kara rufa asiri.
Kallo ida take zaune tana faman juya kudin yayi yace yanzu ke bakiji kunya ba mutum haka baisan komai ba sai gadara da jahilci.
Yanzun kuma may nayi yace a gidan ku ba a koya maki godiya bane ko baki ji yadda yar uwar ki tayi godiya ba yanzu.
Samad har abin yakai ka zage ni a gaban wanan yace wanan din tafiki mitumci da sanin ya kamata don gashi tayi a gaban ki.
Yana fadin haka ya mike yabar gurin ta bishi da kallon mamaki kafin ta juyo kaina tace gurin ki yau ya cika a gidan nan sai dai naki kadan ne na baki nan da dan lokaci kadan.
Dariya nayi nace tunda ke ce da lokacin a hannun ki ga lokacin nan yana fadin kanshi wanan shirmay na fada maki yanzu ba shine mafita ba gare ki.
Da zaki koma gs Allah ki dawo hanya madaidaciya a zauna lafiya mutaru mu rufawa kan mu asiri da mijin mu da zaifi maki.
Ina fadin haka na mike ina cewa mudai mun gode Allah ya kara rufa mai asiri duniya dalahira don gobe akara muna.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/24/21, 7:50 AM - Fatima Amarya: Duk yadda yaso mu tashi da wuri hakan bai samu ba don fitan da mukayi tun safe zuwa gurin motar da zata daukan muna kayan dakin zainab din da kayan sobaniya da na hada a nan wanda ba wanda yasan dashi maryam ce kadai ta san da wanan sai yau da ake daure kayan ya gani baidai yi magana ba.
Set biyu yai mata inda idan mun dawo dayan nan gidan ta zamu gyara da dayan don haka shi bamu dauke shi ba.
Sai shabiyu da wani abu muka bar garin da tawaga na na bar maryam a wurin kayan wace ita daga baya zata samay mu kaduna idan an fara buki.
Ban tsaya bin ta kan Nafisa ba don banga alaman kamar zata tafi ba Al,kasim ne zai jamu sai dayan hilux dake dauke da kaya da zata bimu don haka duk a motana mukayi tafiyan .
Mun sauka kaduna lafiya sai dai nayi mamakin ganin duk zumudin zuwan da mukeyi acan kamar ba wani abinda ke faruwa.
Wanan ne karon farko da nazo tun bayan haihuwana wanda yanzu yakai wata ni masu yawa don yarana suna batun shekara daya ne sunyi wayo dosai do , har sun fara takawa.
Abinda yasa ban zuwa kaduna bai wuce abu daya ba shine rashin barkan da Fati batai min har wanan lokacin har wanan lokacin dama a lokkacin da na haihu din ta bugo waya tana fadin ashe an sauka to barka ba wani Allah ya raya ko wani abu.
Hakan baisa na fita zancen yaranta ba don duk karshen wata idan zai tafi nakan bada sakon da za,a kai wa su Affan din da daddy.
Hajiya mama tayi lorafin rashin zuwan mu har ta gaji sai in fake da yanzu karatuna yayi zafi banda halin tafiya ne niko naga zuwan nawa yana takurawa Fati shiyasa na kara dauke kafana.
Ban damu da rashin taron mu da batayi ba don dama da shirin mu muka zo da abinci mu da komai har abin sha mun tanada a bangarena.
Sai dai naji dadin don ashe su Fauziya na gidan hajiyan su ana cewa mun iso sai suka dira a gidan namu har lokacin anty