Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MIJIN Buzuwa Complete Complete Hausa Novel by Nil

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   93 / 144

276K to 279K   out of 431K words

na mike na shige ina fitowa na tsaya nayi na fila ban kwanta ba sai da na kwanta naji murya shi na fadin.
Wanan magana yasa kije min haka idan ban yi maki magana akan aikata ta,asan da kike son jefa kanki a ciki so kike in kyale ki kiyi.
Ban iya magana a lokacin sai dai a raina nace lalai namiji sai dai a barshi da halin shi yanzu yana nufi ya dauki maganan Nafisa da muhinmanci akan abinda taimin ko don ban haihu dashi bako kuma da gaskiya dai din Nafisa ce kawai a gabam shi.
Da asuba tunda mukai sallah na sauko daga dakin shi duk wanan sakkon da nayi na samu mama laraba ta gama gyara part dina.
Sai kamshi ke tashi komai tsab ta gyara har na shiga dakina nan ma komai tsab har toilet din ta gyara sai kamshi ke tashi.
A raina nace lalai tafiyan mu zaiyi kyau da mama Laraba fitowa nayi zuwa falo muka hade da ita a falon ta fito kitchen nace a, a mama aiki haka da wanan safen.
Tace uwar dakina ai tun kan a kira sallah nake idona biyu ina idarwa na hau abinda ya kawo ni yanzun ma kitchen na gama gyarawa.
Sai dai ban san may zaki girka ba yau amma dai duk da haka na dora maki ruwan zafi a wuta har ya tafasa ina ji nace kai nako gode mama gashi kuma guri ya dauki kyau haka.
Tace to uwar dakina shifa ya kawo ni nan yanzun ma zajen nan nawa kawai nake jiran tashin su in masu wanka.
Nace gaskiya mama nagode fa aiki haka gwanin yabawa Allah yasa mu dore a hakan tsakanin mu.
Tace insha Allahu mun riga da mun saba da wanan ai ko can abinda ke yawan hada mu da hajiya ta kaduna cewa take na faye kakalen aikin da ba a sakani ba ni kuma ban iya keta ba a rayuwana.
Kitchen na nufa na dora girki har wanda zasuci da rana idan na fita farar shimkafa na dafa sai da yayi wara wara na sauke yasha kayan hadi sosai su karas da koren wake da kabeji dahuwar tayi kyau sosai don haka na kwashena zuba a inda ya dace ma kowa.
Na samu tsoka zalla na yanka na tafasa da gishiri da maggi bayan ya dahu na dauko attarudu da tatasai albasa na dan daka su a turmi nayi miyar jajage don yafi dadin cin shimkafa.
Sai cooker outh dana dama na hado da madara zuwa falo su karya dashi don bai sayo muna sabon bread ba ranan idan zai dawo da dare yake shigowa dasu gidan.
Na samu an gama ma yaran wanka har ta shirya su cikin wasu kayan da uwar su tabayar da zamu zo nan falo na zaunar dasu suna karyawa na shige wanka a gurguje na fito na shirya don kada ya girshe ni.
Zamama ke nan zan karya sai gashi part din suka gaisa da laraba yaran nace ma ga Abba ku gaisa mana suka ce ina kwana.
Ya amsa masu tare da zama in kawo maka breakfast ne nan yace eh sai dai kiyi sauri kin san zaki makara fa na wuce zuwa kitchen na hado mai na kawo mai ya karya suna dan hira da laraba sama sama.
Muna gamawa ya mike ya fara fita ban fita ba sai dana kara jawa yaran kun ne na tsorata su nakuma yiwa laraba magan akan su rufe kofa kada su budewa kowa kofan.
Tace a tsorace ai ko murai ban budewa nasan halin gidan ba yau ba ai nayi masu sallama na tafi ta kargamay kofan ta ciki.
Mun dauki hanya shiru ina kallon titi naji muryan shi yana fadin wai ke kina nufin dan maganan da nayi maki kike wanan hura hancin haka.
Ko kina nufin a barki ki yi yadda ranku ke so ki biye nata ku zama daya kuyi aikin rashin hankali tunda kin san bakin ki take nema.
To wallahi bari kiji ban yarda da fadan duka ba ko babu lalurar ciki kaddara akewa gudu ai don ba karfin ku daya ba kema kin sani.
Kuyi na farko kunyi na karshe kada ku mayar dani sakaran namiji mana da baisan ciwon kansa ace gida ana irin wanan fadan.
Na dago kai na kalle shi sai na kawar da kaina gefe don kwar jinin da yai min a fuska da na kalle shi yadda ya dake fuska yana min fada acikin serious voice .
Muka isa na fita ranan bance dashi komai ba ya ja motar shi yabar gurin na shige cikin school din kai tsaye.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: A falon anty Salbiya muke zaune bayan barin mu makaranta mun gaisa na mika mata tsaraba da nazo mata dashi tai min godiya tare da tambayana mutanen gida.
Suna lafiya na bata amsa dashi kawai naci gaba da sauraren su ba tare da nayi magana ba bayan dan hiran kadunan da sukayi ta dubeni tace yau ko lafiya kike nace lafiya anty.
Tace to mu fara abinda ya kawo ku don nima fita nake son yi dan anjima kadan zan shiga barka anan makwabtan mu ne.
Kai na rausaya tare da sake dan guntun tsuki nace dama dai an barshi anty don ni banga amfanin yin hakan ba gaskiya.
Subbahanallahi tace dama kallon ki nake kawai don nasan da matsala tunda na ganki a haka nace anty may amfanin kai kaita kokarin gyarawa namiji rai shi bai san kanayi ba ma.
Dariya tayi tace zaka ko gyara kanwa ta don su din Allah ya dorasu akan mu dama haka zaman aure ya gada ko da kuwa baka da kishiya balle ke mai kishiya kishiyan ma kuma buzuwa buzuwa ko yar baruwan mu ce ba abin yarda bace kice ki bar mata miji don ke zaki sha tarin takaici.
Yanzun dai may ke faruwa nace wallahi anty mutumin nan mijin tace ne nan dai na kwashe labarin abinda ya faru tun a kaduna har dawowan mu nan Abuja na fada mata komai.
Allah sarki kanwa ta yo ai haka halin maza yake al,amarin sun dama sai hakkuri zaki ga abin magana su bashine abin yi a wurin su ba tun dai na miji irin naku da kullun a cikin ci da sha yake na saddabarun mata.
Yau da kin samu kanshi gobe juyewa zai yi kamar bashi ba sai ke ce mai tarin takaici shi bai san yana yi ba ai kamata yayi ki kara kaimi ba kice wai kin jaye ba kamar yadda kikace yanzu.
Ke ki fa gode ma Allah don wallahi kishi da wa yan nan mutuane ba abin wasa bane ke gashi har kin samu miji na kulaki bata samu yadda take so gaba daya ba a gurin ku.
Gyara kan da addua ai yanzun kika sa hannu khadija don ba fasawa zakiyi ba don shi gyaran nan da muke yi yana hana wani abu ko don kimar hakan da kake dashi.
Gaki a ganuwan cin ribar auren ki kike yanzu idan shakuwa da kauna bai shiga tsakanin ku ba a yanzu yaushe kike tunanen zakuyi shi sai gaba kun fara tara iyali kike ganin wanan abu zai yiyu a tsakanin ku komay.
Ke ki bar maza a inda kika gansu wallahi halin sai Allah daya halicce su don komai iyawan mace sai sun lasa mata wannan nakin cikin da namijin da suke dashi.
Ajiyan zucita na sauke nace nasa abin ne yai yawa wallahi anty anty tace nasa dai kike gani shida kike zaune dashi idan wata ta zauna dake ta fada maki halin nata mijin sai kiga aike mowa ce a gidan ki.
Mike ki gyara ki tofe shi da addua komai zaizo sai Allah ya kawo abin a cikin sauki gare ki ko yanzun ai ba haka taso abin ya tsaya a tsakanin ku ba kika san shirin da akai maku dan wanan tafiya na kwana biyu da kuka yi.
Akwai abinda yafi ciwa kishiya rai kamar miji yai tafiya da yar uwanta koda da yardan ta ne sai ya dan sosheta a rai wanan kishi a jinin mata yake sai dai ana son idan zakayi kada kayi na wuce wuri.
Yanzun missalin in tambaye ki tsakani da Allah ki fada min ke baki kishin su a ziciyar ko kadan don Allah ta fada tana kallon cikin fuskana da idonuwan ta.
Murmushi nayi na dukar dakai ina dariya tace kin gani haka abin yake ai kamar fagen yaki ne aure sai idan inda karfin mace ya kare ga mijin ta.
Ai tunda kika ga ko wani kabila na kishi akan mazan su to ki ji tsoron kalman nan ta kishi da kike ji don kishi na iya kai mace aljanna yana iya kaita wuta Allah yasa mu dace muka amsa da Amin.
Don haka barin baki wasu sirika yau irin na kasan mu banan nan ba sai dai zan fassara maki sunayen su da amfanin su a cikin kalman hausa yadda zaki gane muhinmancin su dakyau.
Ta mike ta shiga ciki sai gata ta dawo hannun ta dauke da wani jakka mai ruwan zaiba ta zauna ta dauko wani kwalba da aka nade da takarda mai ruwan gold tace cikin kallon inda nake kin ga wanan.
Na gyada mata kai tace shi muke kira ina gaban ki uwargida da yaren mu turare ne na sihiri ana shafa shi a wuya da duk wani gabobi na jikin ki amma banda gurin mamanki don gudun kansa gare ki.
Sai zaki gun maigida zaki shafa shi zaki iya gwadashi ko yau idan zaki girki ki gani kin gashi aikin shi shine yana sa dadin saduwa a tsakanin ku.
Idan kina amfani da wanan zaki mallaki mijin ki don sai yaji duniyar nan babu kamar ki zai dawo hannun ki ba sai kin je gun malami ba don hadi ne na sosai akayi shi ba kowa ne yasan shi ba ko ke don na soye maki ne kuma da wace ta turoki gareni akwai mutunci da yarda sosai a tsakanin mu
Shafa shi kuma yana sa wa mutum farin jini da kwarjini yana kara kafiyar soyayya a tsakanin miji da matar sa sosai dama wa yanda suke mu,amula tare.
Tamika min na karba ina kara juya dan kwalban a hannu na sai naga tayi murmushi ta dauko wani ta miko min na karba.
Tace muna kiran sa da bilkisu ma,ana sarauniya bilkisu ana dan zizara shi ne bayan kin shafa kwali karyan mutum yace zai kalli idon ki ya gaya maki maganan banza don kwar jini yake sa mace mai amfani dashi.
Ana amfani da shi ne musanmam mace mai irin kishiyar ki don ki rika yiwa kishiya kwarjini ko idan zaki shiga taro ko wurin dangin miji .
Zakiga suna haba haba dake ba wanda ya isa ya rainaki ko yai maki kallon wullakanci saka shi a idon ki kinga zai saka kaunar ki a gurin maigida yasa ki mallake shi a hannu ya samaki farin jini a gare shi.
Ajiyan zuciya na sauke ina jin kamar har na kama AA ga hannu nane kamar yadda take bayani yanzu tayi murmushi ta dauko min wani leda da akai siling din shi baka ganin abinda ke cikin sa sai ka bude.
Bayan na karba ina dan juya ledan a hannu na tace kin ganshi nan muna kiransa da mujallabul sheri ma,ana da turan ci back to sender.
Shima dafa,i ne sosai hayaki zakiyi dashi karfi gare shi sosai wallahi akwai na ruwan sa kamar turare da sabulun sa sai dai ban samu ba a lokacin da naje kasar mu.
Iddan kika turara shi a jikin ki duk wani aike da akai mike ko dako bakin aljani ke jikin ki sai ya kone shi ssamu ko sihiri ke ko tsafi ne akan ki idan kinyi hayaki dashi sai ya karye.
Yana magance duk wata matsala na cuta da ba,asan yana ajikin mutum ba yawan hayaki dashi yana kawo waraka da ikon Allah ga mutum.
Sai wanan da ace kina sana,a ne zaki ga fa,idar sa sosai shi sunan sa majabul khairi hayaki ne karfi gare shi sosai shima yana sa ka tara jama,a idan kina harkan kasuwanci kina amfani dashi jama,a zasu zasu rika tururuwa wajen sayen sana,ar ki.
Yin hayaki dashi a yadda kike zuwa makarantar nan da yadda mijin ki yake da jama, a idan baiyi hankali ba duk zasu dawo wurin ki don haka yawan hayaki dashi yana kawo ki rika samun alheri ta inda baki zata ba ma.
Tana kawai nan ta koma da jikin ta ga makarin kujera ta jingina tana murmushi tace ki gwada wa yan nan mugani akan su duk abinda kika gani kizo ki ban labari don zan yi tafiya zuwa sudan bukin yar uwata dake can.
Ajiyan zuciya na sauke tare da fadin na gode anty maryam tace anty mun gode amma nima gaskiya da anbani don abu ga hannu shine abu.
Dariya muka saka mata tace ke da baki aure ba tukun tace anty ai yin zanyi nan bada dadewa ba idan Allah ya yarda.
Tace to bari lokaci yayi kilama a lokacin naje kasar mu kinga sai in maki hadi mai kyau daga can tace to shike nan amma fa kin san alkawari kika dauka tace na sani.
Bamu dade ba mukka fitoo naso zuwa gaida anty hauwa don na kwana biyu ban je gidan ba saboda zuwa wurin anty Salbiyan da muke yanzu.
Ko da na dawo sai dana kwankwasa kofa sau biyu kamar yadda na fadama laraba amma hakan bai sa ta bude min ba sai da ta tambaya waye nace mama nice khadija ta bude tana min sannu da dawowa na amsa ina shiga.
Zama nayi a falo wurin su Affan ina tambayan su idan suna da damuwa laraba tace sai dai shi wanan mai kiriniyar ba wai sai in bude mai yaje waje nace dashi ya rufa min asiri ina zan sake dan mutane cikin wanan gardawan haka ni laraba.
Nace mama ai da kin bude mai sai ku fita tare ku dan sha iska amma yanzu barin dan kaisu su sha iska kin san ba yadda zaka iya tauye yaro a guri daya haka ai.
Idan ya kama sai ka iya uwar daki na sai ayi ai kin san komai daurowa ne Fati bata da yarda balle yadda tasan halin matar gidan nan a baya shine abinda takewa jiyewa zuwan su nan din ai kikaga tun farko bata yarda ba.
Yanzu ma ai don hajiya ta nuna mata fin karfi ne ga hakan don tafita tunane zuwan su nan zai kara kawo shakuwa tsakanin su da mahaifin su kamar yadda naga kinayi din nan.
Nace mama ashe kin gane manufana nazuwa dasu nan da nayi a yanzu tace duk wani mahankali da hange zai hango hakan ai yar nan.
Ciki na shiga na dan kewaya na fito na samay su zaune a falo nace ku tashi mu dan ja waje da sauri yaran suka mike tsaye.
Bamu tsaya falo ba na zaga dasu wajen gidan har inda nima ban taba kai kafana ba tun shiga na gidan mun taka da yaran ranan don dai su dan sake jikin su.
Leken mu naga Samiha tanayi ta window falon tsayawa nayi nace da ita duk da ta sake labulen falon idan an turo ki ne ko ke kika sa kanki gulma je ki karas da abinda kika gani yanzu kada dan kuda ya riga ki.
Bayan mun dawo a falo inda suke na zauna dasu wani tasha aka kai suna yaren su kuma babu mai kallo a lokacin.
Mikewa nayi na dauki remote din tv na mayar masu mbc cartoon suna kallo ganin wata garmaka daga cikin su ta mike ta shiga ciki yasa ni gyara zama da yaran ina jiran tsammani.
Talge baki shan rada sai ko gasu tare sun fito da ita daga dakin remote din tv na a hannu na rike tana zuwa ta tsaya a kaina tana fadin .
Ke may ye hujjan ki na canza masu chanal da kikayi suna kallo ko son iko da mulkin naki har yakawo akan yan uwana ya tashi ga maigidan kuma ya dawo gare mu ne.
Ban ko kalli inda take ba balle in san Allah yai ruwanta a wurin ta sake maimaita maganan ta a cikin tsawa nace ke ke ke wai wata irin fitinaniyar mace ce.
Ina nan dai gidan yaran nan ne kuma don jin dadin iyalin shi ba wasu ba ya saka wanan kayan haka na nuna mata kayan falon da hannu.
Ahhaye nanaye inji yan mata naki ikon da mulkin ke nan dadin abindai baki cikin gadon gidan nan idan ma don iyalin shi ne ba dai don ke ba bakar manya mai bakin nacin tsiya.
A haka zaki kare wurin kalan diya kina fadan gado dasu gadon da bazaki ci ko sisi a cikin sa ba kuma ki sani gidan nan gidanane kije can ki nemi gidan ki.
Nace gado gado yan cin gado manya to kin sani ko ki riga mai dukiyan mutuwa ko a lahira zakici gadon naki ke nan.
Bakar manya kurwa na kur akan ki ko kina yawo

93 / 144

Chapters