Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Fansar RAI Complete 1&2 Complete Hausa Novel by SIS Nerja'art

Author :  SIS NERJA'ART Category :  African Stories & Novels

Chapter   74 / 74

219K to 220.3K   out of 220.3K words

ganin batayi nasara ba tamik'e cikin fushi tana cewa ko da ba yau ba *Najla* sai na cika burina, sai na 'bata maki wannan kyakkyawar fuskar da kike tak'ama da ita bazan ta'ba barinki ba....



** ** ** **

Tunda suka shigo cikin garin kallon mutane kawai suke abun yana burgesu ganin yadda suke ta rayuwarsu, itako shugabar tasu yatsina fuska kawai take dan abun sam bai burgeta ba, suna tafiya a wajen titi wata mata tagifta ta gabansu nan d'aya daga cikinsu tafara lasar baki saurin shak'o wuyanta gimbiya najma tayi tace kar kikuskura kilashi wani a cikin garin nan domin garin nan yana da had'ari sosai duk mayen da suka kama basu barinshi a raye,,, tana fad'in haka tatureta gefe nan tayi saurin duk'awa cike da girmamawa tace kigafarceni ya shugabata.
Batare da ta amsa mataba tawuce gaba suna biye da ita a baya suna cikin tafiya a wajen kasuwa tana kallon wani shago da yad'auke mata hankali saboda cikowar mutanen da suke cikinsh nan wani tsoho yatafo da 'yar sandarshi yana dogarawa bai kulaba yad'an bugeta.
A fusace tajuyo takalleshi tare da shak'oshi cikin fushi tace kai wane irin dabba ne da zaka bugeni, bakasan wacece ni ba?.
Jikin tsohon yana karkarwa yace kiyi hak'uri bana gani sosai ne.
Batare da ta sakeshi ba tace bana yafiya a duk lokacin da akayi man laifi sai na d'auki fansa dan haka bazan ta'ba barinka ba, dogon harshenta tafara fiddowa daga cikin bakinta tana shirin lashe fuskar tsohon, daga bayanta taji andaka mata tsawa saurin maida harshen tayi tasaki tsohon tajuyo dan ganin wanda yayi tsawar

Wasu mutane ne tagani tsaye a bayan wani kyakkyawan saurayi yana sanye da kaya na sarauta duk sun fito daga cikin motocinsu, saurayin ne cikin 'bacin rai yace ke wace irin macece bakida hankali zaki shak'e tsoho ko iyayenki basuyi maki tarbiya ba?.
Tsayawa tayi tana kallonshi cike da mamaki jin kalaman da yake fad'a mata wanda tunda take a rayuwarta ba'a ta'ba fad'a mata irinsu ba sai yau da tashigo k'asar nan yawon bud'e ido.
Kallon tsohon saurayin yayi yaga yana ta kyarma sannan yakalli nakusa da shi yace aje arakashi gida.
'Dan russunawa yayi yace angama ranka yadad'e nan biyu daga cikin mutanen suka yi saurin nufar inda tsohon yake suka ruk'oshi suka sa cikin mota suka tafi da shi.

Kallon kallo suka dinga yi shi da Gimbiya Najma yana mata kallon tsana, inda ita kuma take jifanshi da mugun kallo, sai kuma chan yajuya aka bud'e mashi mota cikin k'asaita yashiga aka rufe nan sauran mutanen nashi kowa yashiga mota suka bad'a ma su Najma k'ura suka tafi.

Cikin 'bacin rai tace wanene wannan? Wanene shi da har zai d'aga min murya? Ya zama dole kubishi kugano min inda yake da kuma matsayinshi a garin nan dan bazan ta'ba barinshi ba!!!
Mata ukku ne suka 'bace lokaci guda.
Nan Najma takalli sauran tana hucci sai kuma tarufe idanunta tana motsa baki ahankali nan ita da sauran matan suka 'bace 'bat.


___kuyanginta ne zaune kusa da ita suna ta mata hidima inda ita kuma take ta murza zoben da yake hannunta, k'wank'wasa k'ofa akayi nan masu tsaron k'ofar sukayi saurin bud'ewa.
Wata farar macece tashigo fuskarnan fara fat.
'Dago kai Najla tayi takalleta tace Hasisa ina kika shiga yau tun d'azu ina ta nemanki.
Saurin duk'awa tayi tace kigafarceni ya shugabata hak'ik'a na zo maki da wani labari da zai sakaki cikin farin ciki.
Idanu Gimbiya Najla tazuba mata hakan yaba Kuyangar damar cigaba da maganarta dan tasan shugabar tasu ba me yawan hayaniya bace...
Yau 'yar uwarki tafita da bak'ak'en kuyanginta yawon bud'e ido inda ni kuma nayi amfani da tsafina nabisu batare da na bari ta ganni ba, wata k'asa ce me suna Miraj mukaje inda mutane ne suke rayuwa a k'asar suna rayuwa ta 'yanci sannan suna da arzik'i sosai k'asar tana cikin k'asashe da ake ji da su wajen dukiya sannan sarkinsu ya kasance me adalci saidai abinda zai baki mamaki su d'in suna bin wani addini sannan su mutane ne ba irin muba, kowane maye yana tsoron zuwa k'asar miraj saboda basu yarda da maita ba duk lokacin da suka kama maye basu barinshi suna had'a wuta me zafi suk'oneshi wannan dalilin ne yasa muke tsoron tunkarar k'asar tun shekaru d'ari biyu a chan baya, saidai wasu daga cikinmu sunsha suyi k'ok'arin zuwa k'asar sukama mutanen ciki wasu suna samun nasarar dawowa da ransu wasu kuma ana kamasu akashe.

Gimbiya Najla idanu tazuba mata tana saurarenta, cigaba tayi da cewa saidai abun mamaki da ban tsoro a yau d'innan wani mutum me shiga ta alfarma yanayinshi kawai zaki kalla kigane shi d'in jinin sarauta ne ya harzuk'a Gimbiya Najma da kalamanshi da yayi mata wanda taci alwashin d'aukar fansa bazata ta'ba barinshi ba dan a yanzu haka ta tura bak'ak'en kuyanginta dan sugano mata asalin mutumin......


____*****_____

....A yanzu nice shugabarku nice shugaba a k'asar Nairan ya zama dole kowane mahaluk'i yayi min mubaya'a fararen mayu da bak'ak'en mayu duk wanda yak'i haka zan kasheshi a yanzun nan,,, tana fad'in haka tazauna saman kujerar mulki...




Tsugunne take a gaban gawar tana ta rusa kuka nan wata kuyanga tashigo cikin sauri tamaida k'ofar tarufe cike da girmamawa tace ya shugabata ya kamata kitashi kibar masarautar nan dan a yanzu 'yar uwarki ta aiko azo akawo mata ke, jama'arta suna nan dayawa sun nufo d'akinki.
'Dago fuskarta tayi da tayi jajir saboda tsananin kuka takalli kuyangartata har ta bud'e baki zatayi magana sukaji anfara buga k'ofa dak'arfi, kuyangarce cikin sauri tanufo inda take tataimaka mata tamik'e tsaye..........

+++++++++++

...Ranka yadad'e ya kamata kaduba maganata baidace ace kamar kai ba a matsayinka na babban sarki ace d'anka yarima yana zaune babu aure bayan duk wata dukiya yana da ita shin idan baiyi aure yanzu ba sai yaushe zaiyi ko sai bayan mutuwarmu kaduba kaga 'yar uwarshi yadda take k'aunarshi tana binshi ammah ko kad'an baya kulata shin hakan da yakeyi ya dace kenan.....bud'e k'ofar da akayi aka shigone yasa taja bakinta tayi shuru saboda yanayin takun tafiyar da tajiyo yasa tagane Yarima ne, sai a lokacin sarki yad'ago kai yakalleta sannan yamaida kallonshi ga yarima d'an da yad'auki son duniya yad'aura mashi.....


_____
..Ya kamata ace Gimbiya ta fito a wannan ranar anyi girkin masarautar nan da ita kar kumance hakan shine al'adar masaraurar nan duk amaryar da aka auro acikinta dole ne bayan sati biyu tafito tashiga kitchen dakanta tagirka abincin da Yarima, sarki da sarauniya zasu ci a ranar nan wannan sak'one aje afad'a ma gimbiya!!!

Wata kuyanga ce cikin sauri tamik'e tafita dan ta isar da sak'on uwargijiyarta.
Wadda tagama bayanin juyawa tayi takalli Sarauniya mahaifiyar yarima da itama take kallonta nan tasakar mata murmushi mai cike da ma'anoni sannan tawuce gaba inda sauran kuyanginta suka take mata baya.


A lokacin da sak'on ya iso agareta tsaye tayi tarasa ta inda zata fara, k'arar k'araurawa tajiyo daga waje nan tafara jiyo muryar jakadiya tana cewa a yau ranar murnar ce agaremu auren yarima da gimbiyarshi ya cika sati biyu a yanzu haka muna jiran fitowar gimbiya zatazo tagirka ma yarima da iyayenshi abinci me dad'i wanda zasuci dan nuna farin cikin wannan ranar.
Kallon agogo tayi da daidai lokacin k'arfe sha d'aya daidai tabuga saurin matsawa tayi tad'age labule nan taga yanayin gidan ko akwai rana sosai.
Ja tafara yi da baya cike da tashin hankali tana tunanin ta yadda zata iya fita a wannan lokacin dan ta san ba irin wannan lokacin bane lokacin fitarta.....


*_KUWWA DA KUWWA....._*
(Bata korar buzu)
Labarin ya sha banban da wanda kuka saba karantawa.
shima ga duk me buk'ata zai sameshi akan farashi naira d'ari biyu (200), saidai bazan fara sakinshi ba har sai na gama typing d'in part 1.
Kar kubari abaku labari


Kukasance da ni acikin sabon free novel d'ina wanda yake tafe gajeren labari me suna *NADAMAR RAI*


_Taku har kullum sis Nerja'art✍🏻_
v

74 / 74