Author : SIS NERJA'ART Category : African Stories & Novels
gaisa nan yanuna mashi kujera yazauna, tambayarshi yayi ya aiki ya amsa da Alhamdulillah.
DPO jujjuyawa yayi a kujerar da yake zaune sannan yace Barrister Faruk ba komai yasa na kiraka ba sai akan case d'in jawahir akan kisan Alhaji Sa'idu wanda a yanzu mun k'ara samun k'wak'k'warar hujjar da tanuna mana tana da hannu a cikin kisan shi zamu mik'a case d'in a kotu dan ya kamata kotu tayi gaugawar d'aukar mataki saboda abu sai k'ara cigaba yake.
Shuru Faruk yayi yazuba mashi idanu yana kallonshi har yakai aya sannan yace DPO na ji bayaninka saidai inaso kasan cewa wannan zancen duk ba gaskiya bane jawahir bata da hannu acikin mutuwar Alhaji Sa'idu Nepa yakamata kudaina zarginta saboda kun duba CCTV Camera a daidai lokacin da akayi kisan muna a hotel kaga babu hujjar da zatasa ace itace takasheshi.
'Dan guntun murmushi DPO yayi yace Eh munga haka ammah wannan bai isa yazama k'wak'warar shaida ba, inaso kasan wani abu duk mutuwar wad'anda ake zarginta akansu kusan haka yafaru kuma muna tunani tana amfani da layar zana ne tana 'bacewa taje takashesu sannan su kansu lauyoyinta bata barsu ba tana acikin gidan yari takashesu.
Na ji wannan saidai ban gamsu da hujjarka ba.
Cikin d'aga murya DPO yace Barrister nasan aikina sannan ina k'ok'ari wajen ganin na kawo cikakkun hujjoji da dole za'a yadda cewa itace takashesu kamar yadda tun yanzu na fara samu dan mun samu hoto kamar yadda muka samu an aje a mutuwar sauran mutanen shin wannan ba hujja bane?
Murmushi Barr Faruk yayi yace kusan haka saidai inaso kasani nima zanyi bakin k'ok'arina a matsayina na lauyanta.
Jinjina kai DPO yayi yace dakyau Barr Faruk.
Mik'ewa yayi tare da mik'a mashi hannu sukayi musabaha sannan yace na barka lafiya.
Ta'be baki DPO yayi yace ba damuwa a duk lokacin da buk'atar nemanka yataso zakaji kirana.
Ohk ba damuwa inspector sai na ji ka.
Tunda yakama hanya ba abinda yatsaya mashi a rai sai maganganun da jawahir tafad'a mashi kenan har hukuma sun sanar da su akan kisan da akayi ma mahaifinta ammah ba'a d'au wani mataki ba? Indai hakane to da wannan damar sukayi amfani wajen d'aukar fansar kisan da akayi ma iyayenta saidai taya zan samu cikakkun hujjojin da zan iya kareta da su? taya zan wanketa gaban kotu? A fili yace ya zama dole jawahir kiyi min magana indai har kinason barin gidan kason nan ammah ita fa wannan aljanar...bai rufe bakiba sai gani yayi ta mirrir d'in motarshi kamar wannan tsohuwar ce zaune tana kallonshi da k'walak'walan idanunta saurin jan burki yayi yatsaya tare da waiwayawa baya ammah baiga kowa ba, ajiyar zuciya yasafke tare da jingine kanshi a jikin kujera kusan minti ukku sannan yatada motarshi yanufi gida.
Yana isa wanka yayi yashirya sannan yafito parlor yasamu iyayenshi Momcy tazubo mashi lunch yazauna yayi suka d'an ta'ba hira yatashi yakoma d'akinshi wayoyinshi gabad'aya yakashe dan kar atakura mashi yad'auko laptop d'inshi tare da diary d'in jawahir yazauna yana aiki saida yaji k'walwarshi ta d'auki caji tana buk'atar hutu sannan ya ajiye tare da kwantawa saman gadonshi bai dad'e da kwanciya ba bacci yai awon gaba da shi daman abu ga wanda bai samu yaruntsa ba.
Ba shine yafarka daga baccin da yake ba sai wajen biyar a gurguje yai wanka sannan yad'auro alwallah.
Bayan ya gama duk shirinshi yad'auki laptop d'inshi da key d'in motarshi yafita dan yaje chan gidanshi da yake gani zaifi samun kwanciyar hankali yayi aikinshi yana fita daidai lokacin motar nasiba ta cinno kai cikin gate d'in gidan.....
_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:09 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*
*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Award Together]
_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai biya d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction ta wannan number d'in 09035938246_
_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_
PART TWO
_~GORON SALLAH~_
*PAGE 2*
Kallon motarta yayi yad'auke kai sannan yawuce yanufi parking space wajen motarshi, wani irin parking tayi yana ji lokacin da taja burki dak'arfi, tabud'e motar tafito cikin sauri tanufi wajen da yake tafiya tare da kiran sunan shi.
Ja yayi yatsaya batare da ya juyoba har ta iso, gabanshi tatsaya tana kallonshi damuwa k'arara ta bayyana a fuskarta cikin karyayyar zuciya tace haba Faruk yanzu har ni zaka gani na zo ammah kashareni baka ma da lokacina.
Faruk sai a lokacin yakalleta yace ba haka bane Nasiba taya kike tunanin zan shareki.
Ba ga shinan ba ka yi, bansan menayi maka ba har zaka yanke hukunci irin haka faruk, wane irin laifi nayi maka da har zaka k'i amincewa da aurena, ko sona ne kadaina yi,,,, tafad'a hawaye suna fita daga idanunta.
Hankalin faruk ya tashi sosai ammah bai nuna mataba yace ko d'aya Nasiba ba haka bane ke kanki shaida ce ina sonki kuma ba wai na fasa aurenki bane mahaifinki ne kawai yakeso yabada matsala a cikin maganar aurenmu.
Katseshi tayi tace koma dai minene faruk bai dace saboda aikinka kak'ini ba, meyasa kake son fifita aikinka akaina? Kana nuna min kamar aikinka ya fini matsayi a wajenka.
'Dan guntun murmushi yayi yace Nasiba kidaina cewa haka ko d'aya ba haka bane huruminki daban na aikina daban banaji zan iya had'a soyayyarki da komai saidai me bazan ta'ba bari sonki yashafi aikina ba bansan dalilin da yasa mahaifinki yakeso yashiga cikin aikina ba idan har baiyi niyar bani aurenki ba kawai sai yafito yafad'a min ba wai sai ya sa min dokar da bata shafi aurenmu ba.
Fashewa da matsanancin kuka tayi tace Faruk ban ta'ba tunanin haka daga gareka ba koma menene na d'auka zaka iya sadaukar da shi akan soyayyarmu, me zai hana kahak'ura da koma menene muyi aure.
Zuba mata idanu yayi yana kallon yadda take kuka bilhak'i duk sai yaji tausayinta ammah yana tunowa da yadda sukayi da mahaifinta sai yagirgiza kai yace bazan iya haka ba, kamar yadda wani uzuri na aikina bazai hanani aurenki ba toh haka shima aurenki bazai shiga hurumin aikina ba duk son da nake maki zan iya hak'ura har zuwa lokacin da mahaifinki zai amince muyi aure dan haka kar kiga laifina a ciki kiyi hak'uri,,,
Yana fad'in haka yawuce yanufi wajen motarshi yabud'e,, cikin kuka Nasiba tafara k'wala mashi kira ammah yashareta yashiga yamaida yarufe yatada motar yabar gidan, ta window yana kallon yadda take kuka tana bin motar da kallo, duk sai yaji babu dad'i wani irin abu ya tsaya mashi a rai, yana fita daga gate d'in gidan taka burki yayi yatsaya tare da kife kanshi a jikin steering yana jin wani irin tausayinta da soyayyarta sun mamaye mashi zuciya, shi kanshi ya san yayi k'ok'ari sosai wajen danne sonta, girgiza kai yayi ahankali yace Nasiba mahaifinki ne yasaka mu cikin wannan halin ammah ni ina sonki.
Ya dad'e a wajen sannan yaja motarshi yatafi, tuk'i kawai yake ammah yana jin babu dad'i a ranshi har ya isa gidanshi da yaci buri sutare shi da amaryarshi Nasiba.
Nasiba ganin yadda yaficce bai ko tsaya saurarentaba yasa tacigaba da kukanta tare da juyawa cikin sauri tashiga cikin gidan, Momcy da shigowarta parlor kenan sai ganin Nasiba tayi kamar anjefota.
Cike da mamaki tamatso wajen tana cewa lafiya Nasiba me yake faruwa?
Kasa yi ma Mom bayani tayi sai ma cigaba da kukan da take nan hankalin Mom ya ida tashi taruk'ota sukaje saman kujera suka zauna sannan tace dan Allah Nasiba kidaina kukan haka kiyi min bayani me yake faruwa?
Cikin sheshek'ar kuka tace Mom Faruk ne.
Ajiyar zuciya Mom tasafke tace me yafaru da Faruk d'in wani abu yayi maki?
Cigaba da kukanta tayi dan batasan abinda zatace ma Mom ba.
Ganin haka yasa Mom tace shikenan kidaina kukan kibarni da shi zai zo yasameni.
Tsagaitawa tayi daga kukan tace baimin komai ba cewa yayi bazai aureniba.
Zaro idanu Mom tayi tace shi Faruk d'in da kanshi yace haka?
Sadda kanta tayi k'asa tace ba wai hakaba ya ce min aikinshi ya fiye mashi ni.
Jinjina kai tayi cikin ranta tace watau kenan k'arya yayi masu da yace yayi magana da Daddyn Nasiba akan kar ayi baikonsu sai ta gama karatunta, to me yake nufi da hakan, koma menene zaya dawo gidan yasameni,,, dafa Nasiba tayi tace kinga kidaina 'bata hawayenki insha Allahu babu abinda zai hana aurenku da Faruk kibarni da shi.
Wata irin kunya ce takama Nasiba tace Mom ba wai haka ba kawai dai....sai kuma tayi shuru.
Murmushi Mom tayi tace koma menene kar kidamu kinji?
'Daga kai tayi alamun toh sannan tamik'e tace Mom bari intafi gida.
A'a Nasiba tun yanzu? Ko ruwa fa baki sha ba.
Kanta sadde k'asa tace Allah Mom nagode daman sauri nake Hajiya ta aikeni.
Toh shikenan Nasiba kikwantar da hankalinki babu abinda zai hana aurenku da Faruk kibarshi zai dawo gidan yasameni, kigaishe da Hajiyarku kinji.
Cikin jin dad'i tace toh Mom zataji sosai.
Tunda tashiga mota inba goge hawaye ba babu abinda take maganganun Faruk sun tsaya mata a rai sosai dan bata ta'ba tunanin hakan daga gareshiba musamman yadda yake nuna mata so ta d'auka ba wani case ba hatta aikinshi zai iya hak'ura da shi saboda ita sai gashi taga ba hakaba, ammah meyasa su Daddy sukace dole sai ya janye ya tsame hannunshi daga case d'in sannan zasu amince subashi ita? Miye had'in aurensu da aikinshi?,,, buga steering d'in motar tayi tare da girgiza kai a fili tace sam hakan bai daceba.
Wajen k'arfe biyar motocin police ukku suka tsaya a harabar gidan yarin inda police d'in suka fito wasu suka tsaya a nan wasu kuma suka shiga ciki tare da ogansu direct office d'in shugaban gidan suka je inda DPO yashiga ciki su kuma suka ja suka tsaya bakin k'ofa.
Bayan sun gaisa da Alhaji Mahadi ne DPO yake ce mashi mun dai dawo akan case d'in yarinyar chan.
'Dan guntun yawu Alhaji Mahadi yagad'e yace toh 'yallabai dafatan dai ba wani abu yasake faruwa ba?
No bakomai saidai akan kisan Alhaji Sa'idu Nepa wallahi ka yi sakaci da kayarje aka fita da ita alhali ka san hakan baya daga cikin aikinku abar me laifi lauyanshi yafita da shi koma za'a fita ai kyau a had'a da su da police bare ma wannan yarinyar da take da had'ari.
Cikin sanyin jiki yace hakane d'alla'bai nima sai daga baya naga rashin dacewar hakan ammah Barr Faruk mutum ne me amana na sanshi sosai wannan yana daga cikin dalilin da yasa na amince mashi.
Shuru DPO yayi na d'an lokaci sai chan yace ai bata a nan duk yadda kad'auki mutum bai zama dole hakaba, inma haka ne taya zasu iya fita su kad'ai ai zata ma iya guduwa kaima kanka ka san iya dad'ewarmu muna bincike akan case d'innan kafin mugane itace take kisan, shikenan dai kakiyaye yanzu bari inje inganta dan akwai wasu tambayoyi da nakeso inyi maka.
Alhaji Mahadi yace toh shikenan babu damuwa, nan yad'auko wayarshi yakira wani ma'aikaci yazo yayi ma su DPO jagora har d'akin da aka gark'ame jawahir.
Suna isa suka sameta zaune ta jingine kanta da bango tana kallon gefe d'aya har suka shiga bata d'aga kai takallesu ba.
DPO ne yamatsa kusa da ita tare da d'an tsugunnawa a gabanta yace sannu ko jawahir.
'Dago kai tayi takalleshi sai kuma tamaida kallonta a gefe d'aya.
Jinjina kai yayi sannan yace nasan ko ban fad'a ba kinsan abinda yakawoni inaso ki amsa laifinki na kashe Alhaji Sa'idu Nepa kamar yadda kika kashe sauran.
Ahankali tabud'e baki tace banda masaniya akan mutuwarshi.
'Dan guntun murmushi yayi yace ko kina da hujjar da zaki iya kare kanki da ita bayan bincikenmu ya nuna mana kece? Shin abun tambaya ko kina layar zana ko wani siddabaru ne?.
Shuru tayi kamar bataji abinda yaceba.
Juyawa yayi yakalli wata police mace yace tambayar min ita.
Cikin sauri tazo wajen jawahir sai ji tayi anja mata gashi dak'arfi wanda hakan yasa saida tasaki 'yar k'ara, muryar macen taji ta ce bazaki amsa tambayar da akayi maki ba.
Runtse idanunta tayi tare da kai hannunta zata rik'e hannun police d'in sai ji tayi ta sa mata wani abu me kamar k'arfe a wuyanta wanda yataimaka wajen d'ago kanta sama, ji tayi abun ya shak'eta sosai muryar police d'in taji ta ce bazaki amsa tambayar da akayi makiba.
Dak'yar tabud'e baki muryarta tana rawa tace ni bansan komai akan hakaba.
Taya zamu yadda da hakan bayan jiya kun fita tare da Barr Faruk.
Tsananin azabar da takeji ne yasa tafara safke numfashi kad'an kad'an dak'yar tace na fad'a maku bani ba....k'ara matse mata wuya da akayi da k'arfen yasa takasa k'arasa fad'in abinda yake bakinta nan idanuwanta sukayo waje.
Ganin haja yasa DPO yace ak'yaleta.
Ana janye mata k'arfen daga wuyanta nan taduk'e tana tari tare da rik'e wuyanta.
Muryar DPO taji yana cewa jawahir idan har kika cigaba da 'boye min gaskiya fiye da wannan zansa ayi maki, inaso kifad'a min gaskiya game da mutuwar Alhaji Sa'idu ko shima bazaki amsa laifinba kamar yadda kika k'i amsa na sauran?
'Dago kai tayi a galabaice takalleshi tana nishi tace bai zama dole in iya amsa abinda banda masaniya a kai.
Murmushi yayi yace matsalata da ke taurin kai ammah da sannu zan safke maki shi, zanje incigaba da bincike idan har na ida tabbatar da kece kikayi kisan to nayi maki alk'awalin zaki fuskanci hukunci me tsauri akan k'aryar da kikayi min, yana fad'in haka yamik'e tsaye yace a kowane lokaci zaki iya ganina na dawo gareki a duk lokacin da kika ganni to ki tabbata asirinki ya gama tonuwa kuma zaki fuskanci hukuncin daidai da abinda kika aikata,,, yana fad'in haka yajuya yatafi inda sauran police suka take mashi ba.
Jawahir da idanu tabishi hannunta yana rik'e da wuyanta har lokacin numfashinta bai ida komawa daidai ba dan idanuwanta ko gabad'aya suka birkice, kwanciya tayi a wajen tana safke numfashi sama sama kafin daga bisani tafara motsa bakinta ahankali kamar me karanto wani abu chan sai ga wani haske ya bayyana a chan k'arshen bangon d'akin jawahir tashi tayi zaune tana tari sama sama nan tayi yunk'urin mik'ewa tsaye ammah takasa lokaci guda takoma takwanta tare da runtse idanunta ahankali hasken yabayyana a wajen da take yashiga jikinta,,, nan bacci yayi awon gaba da ita.
Alhaji Sufyan da Hajiya maijidda daidai lokacin da suka fito daga d'aki zata raka mijinta da zai fita suka jiyo k'ara a d'akin Nasiba cikin sauri su dukansu suka nufi d'akin, suna zuwa suka tura k'ofar suka shiga, su dukansu ja sukayi suka tsaya lokacin da suka ganta tana watse d'akin duk kayan kwalliyar da suke saman mirror ta zubar da su tana kuka, cikin sauri Hajiya Maijidda tanufi wajenta tarik'eta tana cewa lafiya Nasiba me yake faruwa?
Fad'awa tayi jikin mahaifiyartata tare da fashewa da sabon kuka tana cewa Mummy meyasa su Daddy zasuyi min haka bayan sun san inason Faruk, miye had'in aurenmu da aikinshi? meyasa zasuce dole sai ya yanje daga wani case sannan zasu bashi ni? Hakan da sukayi sun kyauta mana kenan?
Hajiya Maijidda juyawa tayi takalli mijin nata da yake tsaye sannan tamaida kallonta ga d'iyarta da take rungume jikinta tace yanzu Nasiba akan haka ne kike nema kimaida kanki mahaukaciya?.
Cikin kuka tace fiye da haka ma zanyi mummy indai akan son Faruk ne, saboda haka ya daina kulani d'azu na je gidansu ya shareni.
Alhaji Sufyan takowa yayi yamatso wajen da suke tsaye yace haba Nasiba minene abun damuwa ni fa taimakonki nayi domin naji labarin cewa case d'in da faruk yad'aukar ma kanshi yana da had'ari sosai dan yarinyar kisa tayi ba mutum d'aya ba ta kashe mutane dadama ke hatta lauyoyinta bata bariba, tana abu saikace ba mutum ba duk wanda yanemi yara'beta sai taga bayanshi, shi kanshi Faruk ya san da haka ammah bansan dalilin da yasa yanace sai ya tsaya mataba taya kike gani zan d'auki 'yata inba lauya irin faruk.
Cikin kuka tace Daddy,,, sai kuma tayi shuru.
Cigaba yayi da cewa ki kwantar da hankalinki indai har Faruk dagaske yake sonki na tabbata zai janye game da wannan case d'in sannan zai zo yanemi aurenki, ina jin tsoro kar wani abu yashafeki game da case d'in nan Nasiba kiyi tunani a kai ni mahaifinki ne me son farin cikinki.
Janyewa tayi daga cikin Hajiya maijidda tawuce dagudu tafita tabar d'akin tana cigaba da kukanta.
Su duka da idanu suka bita sai chan Hajiya Maijidda tace kar kadamu Alhaji katafi kawai kabarni da ita zan fahimtar da ita yadda zata gane.
Ajiyar zuciya yasafke yace to shikenan maijidda dan Allah kiyi k'ok'arin hakan.
Toh Alhaji insha Allahu, sai ka dawo.
Toh Allah yasa nan yawuce yatafi ita kuma tanufi part d'inta dan tasan chan ne kawai Nasiba zataje.
_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:09 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*
*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Award Together]
_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_
_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_
_~GORON SALLAH Last page~_
*PAGE 3*
Wajen k'arfe taran dare Barr Faruk yabaro gidanshi tunda yafito daga cikin gidan zai shiga mota yadinga ji kamar ana bin bayanshi sai ya waiga sai yaga ba kowa cikin ranshi yace inma aljannu ne to na fi k'arfinsu.
Mota yashiga yabar gidan tuk'inshi yake a nutse har ya isa gida, direct part d'inshi yawuce yai wanka yashirya, yana cikin saka kaya Dad yakirashi a waya yace yasameshi a parlor, amsawa yayi da toh.
Saida yagama shirinshi sannan yafita yasamesu zaune shi da Mom.
Gaishe da iyayenshi yayi sannan yazauna yace Dad gani.
Dad yace na ganka Faruk tambayarka nakeso inyi mi yahad'a ka da Nasiba?
'Dago kai yayi yakalleshi yace Dad wani abu tace na yi mata?
Mom harararshi tayi tace ba a saniba ana tambayarka kana tambayar mutane.
Kwantar da murya yayi yace ba haka bane Mom kiyi hak'uri.
"Kaine dai zaka ba kanka hak'uri, wallahi Faruk baka kyauta ba d'azu