Author : SIS NERJA'ART Category : African Stories & Novels
lokacin da yaga wannan go slow da aka had'a na abubuwan hawa ba adadi ya yi tsaki ya fi ak'irga musamman da yaga babbar mota ce tahad'a wannan go slow d'in, lokacin da yasamu damar wucewa yana isa airport yatarar jirgi tuni ya safka dan haka yafara tunani ina ma zaiyi shin wajen jawahir zai koma ko kuma zai je gidan Alhaji Tanimu nepa? Daga k'arshe yayanke shawara da yaje gidan Alhaji Tanimu nepa kasancewarshi babba yasa gidanshi yakasance ba 'boyayye bane dan haka yaja mota cikin sauri yanufi hanyar gidan.
Lokacin da ya isa daidai lokacin aka kawo gawarshi daga asibiti a gaban idanunshi iyalenshi suka dinga kuka suna zubewa, hankalin Barr Faruk ba k'aramin tashi yayi ba cikin ranshi yace wannan aikin jawahir ne, buga motarshi yayi da k'arfi a fili yace jawahir bansan irinki ba kin cika taurin kai, ganin yadda dangin mamacin suka tashi hankalinsu duk sai abun yabashi tausayi dan haka yashiga motarshi yabar gidan.
Koda aka tafi da driver chargi office tambayarshi aka yi akan mutuwar Alhaji Tanimu yanace akan baisan komai ba akai nan fa aka dinga dukanshi ammah yanacd da cewa shi dai ba shi yazo d'aukar Alhaji Tanimu ba dan a lokacin ma bai fito daga gida ba kuma koda sukayi wayar farko da Alhaji yafad'a mashi lokacin da zaizo d'aukarshi sai kuma daga baya yakirashi yace yabari sai goma da rabi lokacin jirginsu zai safka saisa ma baizo ba a lokacin sai wajen k'arfe goma da rabi, cikin galabaita yace ammah wallahi ba nine nazo d'aukar Alhaji ba.
Tsayawa DPO yayi yana kallonshi yanayin yadda yai maganar babu alamun k'arya a cikinta, jinjina kai yayi yace taya zamu tabbatar da hakan bayan motar Alhaji ce wacchan ma toh wanene yad'aukota bayan kowa kai yagani.
Cikin kuka yace wallahi iyakar gaskiya ta ce nafad'a maku bani bane ni lokacin ina gidana.
DPO kallon police d'in da yake tsaye wajen yayi yai mashi nuni alamun yazo zasuyi magana dan haka yabiyoshi suka fita.
Bayan sun fitane DPO yakalleshi yace gaskiya wannan lamarin akwai d'aurin kai a ciki banga alamar mutumin nan shine yai kisan nan ba.
Yace Eh gaskiya nima na lura da haka dan jiya da mukaje gidan mukayi tambaya megadi ya ce mana yaga anfita da mota kasancewar glass d'in motar bak'ine yasa bai gane wanda yake cikiba ammah ko a lokacin ya san Driver yana cikin Quarters d'in gidan saisa baikawo komai a ranshi ba dan ya san shine kad'ai yake fita da motar toh bayan wasu mintuna kuma ya ga driver ya fito da wata motar har suka gaisa yace Alhaji zai je yad'auko airport ya san yanzu jirginsu yana gab da safka nan megadi yayi mashi adawo lafiya iya abinda yasani kenan bai kawo komai a ranshi ba game da fitar wacchan motar ta farko kuma akwai tazarar kusan rabin awa tsakanin fitar wacchan motar da wadda driver yafita da ita, babu alamun da yanuna na cewa ya ga dawowar driver bayan fitar motar farko.
Fuzgar da iska DPO yayi yace tabbas hakane dan daga airport zuwa inda aka kashe Alhaji Tanimu tafiya ce me d'an nisa ammah ya akayi haka bayan kowa ya ce shine yagani a cikin motar sannan a lokacin da aka kashe Alhaji Tanimu ba'a ga tsayawar motar ba bare ace anga fitar wani toh wai duk ya hakan tafaru?
Shuru officer yayi yana nazarin maganar DPO chan DPO yace saidai idan har wanda yai kisan layar zana yayi yafita daga motar toh ammah taya hakan?,,, ahankali yace jawahir fa? Juyowa yayi yakalli officer yace ina tunanin wani abu akan haka yanzu kuyi sauri kuje kubincika min motar da aka kashe Alhaji kuga ba wani hoto da aka ajiye a ciki.
Ohk Sir angama.
Barr Faruk koda yakoma gidan kaso samun Jawahir yayi zaune ta zuba ma gefe d'aya idanu yana isa cikin d'aga murya yace menene haka kika aikata? Tabbas nasan kece kika kashe Alhaji Tanimu miye amfanin shara'ar da ake da har bazaki iya hak'ura kotu tak'watar maki hak'k'inki ba.
Mik'ewa tayi tsaye tana kallonshi ido cikin ido cikin murya me kama da ta kuka tace bana son kotu tak'watar min hak'ina nafiso ink'wata dakaina shin ni a lokacin da suka kashe min nawa iyayen wanene yak'watar min nawa hak'in? Hawaye ne suka fara gangaro mata a idanunta tace babu wanda yai k'ok'arin taimakona haka aka banzatar da maganar mutuwar iyayena sai kace ankashe dabba, shin kuna tunanin hakan baimin ciwo ba? Ko kuna tunanin 'ya'yansu zasu shiga damuwa kamar yadda nashiga? Ko kad'an bazasu shiga damuwa kamar ni ba saboda su mahaifi kawai suka rasa ni kuma har da mahaifiyata narasa.
tsaye yayi yana binta da kallo matsawa tayi gaba kad'an tajuya mashi baya sannan tacigaba da cewa na rasa duk wani farin cikin rayuwata tun bayan rasuwar mahaifiyata a da ina ganin kamar bayan ran mahaifina ina da sauran gata tunda ga mahaifiyata ashe ba haka bane ita kanta saida suka rabani da ita, ban sake kwatanta shiga farin cikiba sai da yaya umar yashiga rayuwata ashe wannan ma nad'an lokaci ne, duk saboda dukiya suka rabani da kowa nawa sannan sukayi amfani da dukiyata duk wannan bai ishesu ba ina a cikin gidan nan sun je sun kwashe files d'in filayen da suke mallakina shin ni me na'aikata wanda ba daidai ba a nan? Juyowa tayi takalleshi tace dan kawai na rama abinda akayi min shikenan na aikata kuskure? Zalunta ta fa akayi ammah ba wanda yataimaka min sai yanzu da nasamu wacce take taimaka min sannan za'a ce banyi daidai ba?
Barr Faruk jikinshi sanyi yayi sosai cikin sanyin murya yace ba wai haka ba jawahir ni ina tare da ke zan taimaka maki nafiso sugurfana a gaban kotu dan su wankeki daga laifin da ake zarginki da shi.
Cikin muryar kuka tace ba wai zargi bane dagaske ne duk na kashesu kuma ban ta'ba nadamar hakan ba ina da burin in ida kashe sauran inyaso nima kotu tayanke min hukuncin kisa zanfi farin ciki da hakan.
Jawahir duk kibar wannan kiyi yadda nace maki na maki alk'awali zan taimaka maki na ganin an hukunta duk wani me laifi ko da ace d'an uwanane ko wani makusancina yake da hannu a ciki na maki alk'awalin sai na gurfanar da shi a gaban kotu, abu guda kawai zakayi shine kisanar da ni sauran suwanene? Sannan ina kawunki da umar?
Girgiza kai tashiga yi tace wannan ne ban saniba abinda dai nasani shine na kashesu, na kashe yaya umar da hannu wannan shine nadamar da nayi a rayuwata,,,, ta k'arashe fad'a tare da fashewa da kuka.
Mutuwar tsaye barr faruk yayi yace dagaske kin kashesu?
Ban san ya akayiba ta rabani da rabin raina dan kawai bata k'aunar aurenmu da shi bansan dalilin kasheshi ba kawai dai abinda nasani....tana zuwa nan sai kuma taja bakinta tayi shuru.
Ganin haka yasa Faruk yace jawahir kikwantar da hankalinki kiyi min bayanin komai nayi maki alk'awali zan taimaka maki.
Cikin sanyin jiki tace bansan me zan ce ba barrister ammah duk wani bayani yana cikin memory card d'in yaya umar.
Taya zan samu memory card d'in?
Girgiza kai tayi tace bana tunanin samunshi zai kasance acikin sauk'i.
Cikin rashin fahimtar maganarta yace meyasa bazai kasance acikin sauk'i ba, kar kidamu kifad'a min inda zan samoshi.
Shuru tayi na d'an lokaci sannan tace banaso wani abu yasameka saboda ni na tabbata bazata ta'ba barinka kaje kad'auko ba.
Kinga jawahir kicire komai a ranki kifad'a min insha Allahu ni zan je ind'akko shi.
Wucewa tayi wajen 'yar tagar nan tatsaya sannan tace yana a chan cikin gidanmu ina tunani a babban parlor saidai nemanshi ba abune me sauk'i ba a k'asa nayada shi nima kaina ban iya cewa ga inda yake ammah wani lokaci zan kwatanta tuna inda yake.
Jinjina kai Barr Faruk yayi yace shikenan ni zan je ind'auko shi kikwantar da hankalinki.
'Daga kai kawai tayi alamun toh sannan takoma tazauna tare da had'e kai da gwiwa tana jin wani irin ciwo a ranta dan ya ta'bo mata inda yake mata k'aik'ayi.
Ganin haka yasa Barr Faruk yajuya yafita.
Ko da police suka je suka bincika motar basu samu wani hoto ba dan haka suka koma suka sanar da DPO duk da haka saida yakira Alhaji Mahadi yatambayeshi jawahir yashaida mashi tana nan cikin gidan yarin ba'a fita da ita ko'ina ba.
Saida Drivern Alhaji Tanimu yayi kwana ukku a wajensu suka tabbatar da badai shi d'in bane yai kisa sannan suka sakeshi kisan ya d'aure ma kowa kai nan jama'a suka dinga tunanin aljannu ne inda DPO yafi tunanin da sa hannun jawahir a ciki saidai baida shaidar da zai iya zarginta ya dai bar abun a ranshi.
_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:11 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*
*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Award Together]
_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai biya d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction ta wannan number d'in 09035938246_
_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_
*PAGE 7*
Bayan ya bar gidan yarin tun a mota yakira Barr Bilal a waya yatambayeshi inda zai sameshi yafad'a mashi yana gida dan haka direct yawuce gidan Barr Bilal yana isa yakirashi a waya yafito bayan sun gaisa ne yace Barr Bilal wani taimako ne nake nema a wajenka.
Barr Bilal yace toh Barrister Allah dai yasa ba akan case d'in jawahir bane.
Murmushi yayi sannan yace kaidai ka cika tsoro kuma anyi sa'a akanshi ne.
"Toh fa ka ji irinta nidai gaskiya Barrister kayi hak'uri wallahi ina tsoron case d'in yarinyar chan ban shirya mutuwa yanzu ba".
Dariya Barr Faruk yayi yace toh ai mutuwa tana kan kowa kaga kakwantar da hankalinka yanzu bari muyi maganar da takawo ni.
Barr Bilal cikin sanyin jiki yace toh shikenan oga ai dole abi abinda kakeso.
Jingine jikinshi yayi a motarshi sannan yace Barr Bilal shin ko zaka iya rakani gidan su jawahir? Sannan idan akwai wani abu da kasani agame da 'yan gidansu inaso kasanar da ni.
Shuru yayi nad'an lokaci sannan yace toh gidansu dai na sanshi saidai a rufe yake a yanzu sannan mutanen gidansu a yadda naji duk sun mutu ko ma ince suna cikin wad'anda takashe.
Da mamaki Barr Faruk yake kallonshi yace dagaske ta kashesu har da Umar?
Cikin rashin fahimtar abinda yake nufi yace wanene kuma shi?
Shuru Barr Faruk yayi cikin ranshi yace Jawahit mi yasa kika aikata wannan kuskuren? Chan kuma yaja numfashi yace shikenan zanje muyi magana da Alk'ali zan san yadda zanyi in samo makullin gidansu muje dan akwai abinda nakeson d'aukowa zuwa gobe.
Toh nidai zan dai rakaka intsaya nesa da gidan ammah babu abinda zaisa inshiga dan inason raina.
Murmushi Barr Faruk yayi yace toh shikenan babu damuwa hakan ma nagode yanzu bari inje inga Alk'ali.
Barr Bilal yace toh Barrister koma me kenan sai kata'boni a waya.
Toh shikenan sai ka ji ni suna yin sallama yashiga motarshi yatafi.
Ya yi niyar zuwa wajen alk'ali sai kuma yayi tunani key d'in wajen DPO kawai zai iya samunshi dan haka daga nan yawuce chan station wajen DPO yai mashi bayanin abinda yakeso, tambayarshi DPO yayi me zaya d'auko a cikin gidan?.
Barr Faruk yace akwai bincike me muhimmanci ne da yakeson yi a cikin gidan.
Wannan ba hujja bace babu abinda zaka samu akan bincikenka kadai tsaya bincikenka akan jawahir.
Murmushi Barr Faruk yayi yace ammah ai ina akan aikina ne kuma aikina ya bani dama zan iya kowane irin bincike a matsayina na lauya.
Jinjina kai DPO yayi yace shikenan idan har aikinka ya baka dama sai kayi yadda kaga ya dace ammah ni bazan bada key d'in gidanba saboda bai dace ashigaba tunda ba kowa a ciki.
Shuru Barr Faruk yayi bai sake cewa komai ba dan ya san DPO ya fad'i hakane dan kawai yana jin haushinshi akan 'yar tsamar da sukayi, daga k'arshe ma yatashi yatafi yana tunanin yadda za'a yi yasamu key d'in gidansu jawahir.
Haka dai yakoma gida har sukayi lunch yana tunanin mafita Momcy ko ta yi mashi tambayoyi ba adadi akan ganin yadda yake ta tunane tunane tun da suka zauna yin lunch saidai yace mata bakomai daga k'arshe yace gajiya ce bacci kawai yakeson yi, yana gamawa tace yatafi yahuta dan haka yatafi part d'inshi a parlor yakwanta yana tunanin yadda zai 'bullo ma lamarin yana a haka bacci yayi awon gaba da shi.
Baifi baccin minti talatin ba yafarka saboda mafarkin da yayi saurin tashi zaune yayi cikin ranshi yana addu'a Allah yasa mafarkin shi yakasance gaskiya kallon agogo yayi yaga k'arfe hud'u ta gota dan haka yatashi yawatsa ruwa sannan yayi sallah yana gamawa yazari key d'in motarshi yaficce yabar gidan.
A karo na biyu yakoma gidan kaso nan yanemi buk'atar sake ganin Jawahir aka amince mashi yana shiga yasameta kwance tana ta bacci nan yatsaya yana tunanin ko yatasheta yatambayeta saidai kuma bayason tashinta, ya yi kusan minti goma a tsaye yana tunanin yadda zaiyi, gefe d'aya kuma yana tunanin mafarkin da yayi cikin ranshi yace wannan ai mafarkine bai zama dole yakasance gaskiya ba jawahir da take nan ciki a ina zata samu key d'in gidansu? Chan kuma yayi wani tunanin dan haka yawuce wajen dutsin nan nacikin d'akin yana dubawa bayanshi da mamaki sai ganin keys yayi guda biyu nan yad'auko mamaki duk ya ida cika shi cikin ranshi yace tabbas yarinyar nan akwai abubuwa masu rikitarwa a tare da ita taya za'a ce tana cikin gidan nan me tsaro ammah a tare da ita akwai wasu abubuwa batare da sanin kowa ba, toh ammah kodai aljanarta take kawo mata? Inko hakane mezaisa bazatayi k'ok'arin fitar da ita daga gidan ba?
Ganin ta motsa ne yasa yakatse tunaninshi yawuce yabar d'akin, k'arar rufe k'ofar da megadi yayi ne yasa tafarka daga baccin da take ahankali tabud'e idanunta tashi tayi zaune tajingine kanta a jikin bango kan kace mi hawaye sun fara wanke mata fuska wanda ita kad'ai tasan dalilin yin haka chan kuma sai tamik'e tanufi wajen 'yar k'aramar tagarnan da haske yake shigo mata ta nan tatsaya wata tsuntsuwa ce guda d'aya take ta shawagi a wajen nan jawahir tazuba mata idanu tana kallonta tana murmushi chan sai ganin tsuntsuwar tayi ta haye saman wani icce dake bayan d'akin ta girgiza ta zama k'aton maciji, tsaye jawahir tayi tana kallonshi nan taga ya tunkaro inda take ahankali tace Ammi.
Yana isowa wajen tagar tayi saurin ja da baya nan macijin yashigo dogo ne sosai dan saida yanannad'e jikinshi saboda tsawon d'akin bazai iya d'aukar ko rabinshi ba ahankali tace Ammi mi kikeso agareni?
Wani irin haske tagani ya fito daga bakin macijin sai gani tayi hasken ya kauraye d'akin lokaci guda macijin yazama siffar wannan tsohuwar, matsowa tayi a dudduk'e tatsaya gefen jawahir cikin shak'ak'ar murya wadda bata fita sosai tace kina ta aikata kuskure a karo na ba adadi jawahir kin cika taurin kai.
Kallon tsohuwar take chan kuma sai ta janye idanunta tace Ammi taya kike tunanin zaki cigaba da samuna cikin ruwan sanyi bayan laifin da kika aikata min?
Bushewa da dariya tsohuwar tayi tace a wajenki ne hakan yakasance laifi ammah ni a wajena ba haka bane.
Cikin d'aga murya tace saboda kin tsaneshi saisa kike ganin haka kinyi amfani da damarki kin rabani da farin cikina alhalin bai........maganar me gadi ce tajiyo yana cewa ke kuma dawa kike surutu haka?
Kallon Ammi tayi da take tsaye tana kallonta sannan tajuya takalli megadi batare da tayi maganaba dan ta san baiga Ammi ba.
Cikin fad'a yace ke baki iya nusuwa kamar yadda sauran sukeyi sai kullum kidinga damun mutane da surutu kar kibari insake jin bakinki.
Har yagama maganar yajuya yatafi jawahir batace mashi komai ba tamaida kallonta ga tsohuwar da take cigaba da kallonta har ta bud'e baki zatayi magana tsohuwar tatari numfashinta tace jawahir taurin kanki ne yasa kike cigaba da zama nan da ace zaki ajiyeshi da ni zan fitar da ke daga nan ammah wanchan barristern yana so yashiga sha'ani na kuma gab nake da inyi maganinshi...
Tun kan tarufe baki jawahir tace shin shima zaki kasheshi ne kamar yadda kika kashe sauran? Wane laifine ya aikata maki?
Bushewa tayi da dariya tace jawahir duk abinda naso shi nake aikatawa.
Cikin fad'a jawahir tace a wannan karon bazan ta'ba bari ki aikata abinda kika so ba.
Cigaba da dariya tsohuwar tayi nan jawahir tawuce takoma tazauna tana kallo tsohuwar ta'bace, tura hannuwanta duka biyun tayi cikin gashin kanta.
Bayan sallar isha'i yana kwance a d'akinshi ya d'age kanshi sama yana kallon ceiling Momcy tashigo d'akin baiji shigowarta ba sai ji yayi ana shafa mashi kai, lumshe idanunshi yayi tare da yin murmushi.
Faruk meyasa kake yawan damun kanka da tunani baka tsoron wani abu yasameka.
Tashi yayi zaune yana cigaba da murmushi yace momcy ba tunani nake ba.
Zama tayi gefenshi tace Faruk ni mahaifiyarka ce nafi kowa sanin halinka na san kana son Nasiba saidai zuciyarka bazata barka ba, naso ace ka yi masu yadda sukeso dan subaka aurenta.
Rik'o hannun mahaifiyar tashi yayi yace momcy kiyi hak'uri indai har Nasiba rabona ce zan sameta kicigaba da tayani da addu'a kawai, cikin sanyin jiki tace shikenan faruk insha Allahu zan cigaba, wata leda tamik'a mashi tace ga wannan Malam ya aiko maka dashi d'azu.
Amsa yayi yace nagode zan kirashi zuwa gobe tunda yanzu dare yayi.
Momcy tace toh shikenan bari intashi intafi Daddynka na chan na baro shi kad'ai.
Murmushi yayi yace toh Mom sai dasafe.
Allah yakaimu Son.
Washe gari wajen 11am barr faruk yakira Barr Bilal yafad'a mashi zai zo yarakashi gidansu Jawahir nan Barr bilal yace yanzu zasu shiga kotu ne saidai da anjima dan haka Barr Faruk yace shikenan zuwa anjiman sai muje.
Bayan sallar la'asar ne Barr Bilal dakanshi yazo gidan yad'auki Barr Faruk suka kama hanya tunda suka fara tafiya kowa shuru yayi chan Barr Faruk yaga shurun ya yi yawa duk surutun Bilal ammah yau ya yi shuru dan haka yajuyo yakalleshi yace ya dai Barr Bilal lafiya yau naga ka yi shuru?
Ta'be baki yayi yace taya kake tunanin zan iya magana bayan zaka kaini inda zan mutu wallahi Barrister da ace ba