Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Fansar RAI Complete 1&2 Complete Hausa Novel by SIS Nerja'art

Author :  SIS NERJA'ART Category :  African Stories & Novels

Chapter   15 / 74

42K to 45K   out of 220.3K words

kanki koma menene dai shikenan nasan dai kina sane da aikin da yake gabanmu gobe.
Wani irin kallo jawahir tayi mata tare da jan tsaki tajuya zata tafi, wani farin abu ne yafito daga cikin idanun matar jawahir bata ankara ba sai ji tayi an fizgeta da k'arfi anbuga da bango nan tasulale tafad'i a sume, matar na ganin haka tabushe da wata irin dariya nan ta isa wajen da jawahir take kwance a sume, wani irin abu tadinga karantawa wanda ba kowane zai gane abinda take cewa ba saboda yaren da take, wata 'yar kwalba ce tabayyana a hannunta k'arama tabud'e ta takarkata a wajen fuskar jawahir sai ga wani abu kamar jini yana zubowa har saida yak'are sannan tagirgiza ta'bace....










_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:10 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Award Together]


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai biya d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction ta wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 5*

Sai bayan sallar isha'i sannan Barr Faruk yakoma gida saida sukayi dinner da iyayenshi sannan yawuce d'akin shi yayi wanka yai shirin bacci yana hawa saman gadonshi zai kwanta nan haske yad'auke gabad'aya duhu yabayyana a d'akin, tsaki yaja tare da mik'a hannunshi saman bedside zai d'auko wayarshi sai ji yayi wayam babu komai lalubawa yashigaa yi cike da mamaki ganin a sama ya ajiyeta ammah bai gantaba, ahankali yaji ana bud'e mashi k'ofar d'aki nan yai zaune yana jira yaji wanene yashigo, tafiya yafara ji anayi a tsakiyar d'akin, cikin rashin tsoro yace wanene? Momcy?.
Shuru yaji ba amsa sai ma k'arar tafiyar da aka cigaba da yi cikin d'aga murya yace koma wanene yayi magana man?
Nan ma shuru sai jin wata irin k'ara yayi shuuuuuu chan kuma yaji an datse d'akin daidai lokacin haske yadawo.
Mamaki yakamashi sosai yana juyawa yaga wayarshi ajiye inda ya aje ammah kuma duk ya laluba d'azu bai ji taba, ahankali yace watau wani yad'aukar min waya shine yanzu yamaido, mik'ewa yayi cikin sauri yafita yabar d'akin duddubawa yadinga yi ko zai ga wani ammah baiga kowaba har yasafko parlor su Dad ne yagani zaune shi da Mom suna ganinshi sukace ya dai Faruk lafiya kake ta sauri haka?
Murmushi yayi yatsaya daga saman step yace bakomai Dad ku ne kuka shigo d'akina?
Cike da mamaki sukace mu kuma?
Daman na ji an shigone lokacin da aka d'auke wuta kuma ina ta magana na ji shuru.
Dad kallon Mom yayi itama takalleshi sannan suka maida kallonsu ga Faruk sukace yaushe kuma aka d'auke nepa ba dai yanzu ba?
Da mamaki yake kallonsu yace bakuga an d'auke ba? Yanzu fa aka maidota.
Dad yace a'a Faruk akwai nepa gaskiya ba'a d'aukeba.
Cikin ranshi yace toh ya akayi haka? Me hakan yake nufi,,, ganin yadda iyayen nashi suke kallonshi yasa yai murmushi yace ina ji wutar d'akina ce tad'auke tadawo bari inje inkwanta.
Mom tace toh ammah kace ka ji kamar anshigo d'akin kuma bamuga kowa ya zo ya wuceba.
Cikin nuna rashin damuwa yace ina ji k'ofar ce tayi k'ara bari inje inkwanta sai dasafenku.
Basu kawo komai aransu ba sukace toh shikenan sai dasafe.

Juyawa yayi yakoma d'akin shi cikin ranshi yana tunanin toh kodai aljannu ne suke bibiyarshi? Addu'a yayi yahau gadonshi yakwanta bai kawo komai a ranshi ba, bai dad'e da kwanciya ba bacci yai awon gaba da shi.





Da asuba saida Dad yazo yatasheshi sannan yasamu yaje masallaci yasamu sallah cikin lokaci dan haka koda yadawo baccinshi yakoma.....

Wajen k'arfe tara yafarka daga baccin da yake a firgice yatashi saboda mummunan mafarkin da yayi dafe kai yayi tare da furta Alhamdulillah da yaga mafarki ne yake ba gaskiya bane dan mafarkin sosai yatsorata shi.
"Wata k'atuwar macijiya ce yagani tana binshi da gudu shi kuma yana ta gudu da dukkan k'arfinshi dan yasamu yatsira, a duk lokacin da zai waiga sai ya ga tana gab da taddoshi ga bakinta tana bud'ewa alamun zatayi mashi tsartuwa, k'ara gudu yake yana neman mafaka ahaka har ya iso wajen wani k'aton gida, wani irin dad'i yaji lokacin da akaron farko yayi tozali da gidan dan haka yana isa baiyi wata wata ba yashiga, daidai da ya shiga k'ofar gidan tamaida kanta tarufe sai gani yayi gidan ya koma mashi wani k'aton fili duk itace ne kawai a ciki, tsaye yayi yana bin filin da kallo chan yafara jiyo kuka ahankali yana tashi, waiwayawa yadinga yi yanaso yajiyo inda yakejin sautin kukan wata 'yar siririyar hanya ce yagani dan haka yabita yana tafiya chan bayan wani icce yahango mutum zaune, cikin sauri ya isa wajen sai ganin jawahir yayi tana ganinshi tabushe da dariya tare da mik'ewa tsaye nan take tayi girgiza sai komawa tayi wannan k'atuwar macijiyar.
Saurin ja da baya yafara kafin daga bisani yajuya yacigaba da gudu nan ko macijiyar tacigaba da binshi, daga nesa da shi yahango wasu d'ungozon mutane tsaye wani irin farin ciki yaji nan yai saurin isa wajensu yana cewa kutaimaka min ammah babu wanda yakalleshi har yashiga tsakiyarsu lokaci guda yaja yatsaya lokacin da yayi tozali da mutum kwance a k'asa alamun ya mutu murya yajiyo daga bayanshi an bushe da dariya wadda takusan rikita mashi dodon kunne saida yai saurin toshe kunnuwanshi da hannuwanshi har saida dariyar talafa sannan yajanye, kunnuwanshi ne suka jiyo ana cewa wannan shine aikin da zan yi a yau d'in nan!
saurin juyawa yayi sai baiga kowa ba dan haka ya ida isa wajen mutumin da yake kwance a k'asa har ya kai hannu zai janye abinda aka rufe mashi fuska da shi yaji wata irin murya ta yi mashi magana da k'arfi me kama da gargad'i ance kar kakuskura abud'e!!!! daidai nan yafarka daga baccin.

Sosai mafarkin yatsorata shi saidai abun ya tsaya mashi rai sosai wai jawahir ce take bibiyarshi tana son taga bayanshi ammah kuma ba wannan ba toh shi mutumin da yagani kwance wanene shi? Tunowa yayi da muryar da take dariya tace wannan shine aikin da zanyi yau,,, sai kuma jawahir tafad'o mashi a rai jiya da take fad'a mashi gobe akwai aikin da zatayi, ahankali yace toh me hakan yake nufi? Kenan tana nufin kisa zatayi?
Ture blanket d'in da yayi rufa da shi yayi cikin sauri yamik'e yafad'a toilet.
Bayan ya yo wanka a gurguje yashirya ko breakfast bai tsayaba ganin momcy bata fitoba yasa yaficce yabar gidan.
Motarshi yafizga cikin k'ank'anin lokaci ya isa gidan kaso, bai biya ta wajen Alhaji Mahadi ba shugaban gidan saidai yakirashi a waya yashaida mashi zuwanshi da son ganin jawahir da yake cikin sauri dan haka ya amince mashi yaturo wani ma'aikaci sukaje tare.

Suna isa cikin sauri yashiga d'akin kwance yasameta gashin nan duk ya baje mata fuska da alama bacci take, ajiyar zuciya yasafke cikin ranshi yace wannan duk yaye yayen mafarki ne, juyawa yayi zai tafi sai kuma yaja yatsaya ahankali yajuyo tare da tsugunnawa a gabanta wani farin abu yagani kamar Alli anyi rubutu da shi k'ananu a kusa da inda take kwance k'ura idanunshi yayi akan rubutun sai gani yayi ansa sunan Alhaji Tanimu Nepa 10:30am, gaban Faruk saida yafad'i a fili yasake maimaita sunan sannan yace me zatayi da sunanshi ko shima ta kasheshi?
Ammah kuma me lokacin yake nufi 10:30am, tsugunne yayi wajen yana tunani chan yatuno da yashiga mota ya ji a redio ana sanarwa a yau babban d'an kasuwa Alhaji Tanimu Nepa zai zo gaisuwar rasuwar d'an uwanshi da k'arfe goma jirginshi zai safka.
Saurin girgiza kai yayi yace a'a bai dace ba hakan, kiran sunan jawahir yafara yi ammah shuru bata ko motsa ba batada banbanci da matacce, ganin haka yasa yaduba agogon hannunshi sai gani yayi k'arfe goma da minti biyar, ahankali yace ya kamata inyi wani abu a yanzun nan, mik'ewa yayi cikin sauri yawuce yafita ko bankwana bai tsaya yi da megadi ba kamar yadda yasaba.


Motarshi yashiga yajata dagudu yabar gidan yarin, gudu yake sosai cike da tashin hankali yana cewa meyasa haka jawahir? Meyasa bazaki bari hukuma tad'auki mataki ba idan har yana da hannu a cikin mutuwar iyayenki, bazan bari kikasheshi ba yazama dole intseratar da shi dan ina son samun bayanai daga wajenshi, gudu yake sosai kamar wanda zai bar garin daidai da round d'in da zai sadashi da airport aka had'a wani irin go slow da yai sanadiyar tsaida duk wani abun hawa da yake wajen.
Hankalin Barr Faruk ba k'aramin tashi yayiba tsaki kawai yakeja yana duba agogo ji yake kamar yafito yabar motar yataka k'asa ya ida isa da k'afafunshi.




K'arfe goma daidai lokacin jirgin sama yasafka wanda ya iso daga k'asar Europe a filin jirgi mutane ne suke fitowa daga cikin shi chan sai ga Alhaji Tanimu ya fito cikin sauri driver d'inshi yaje ya amshi kayanshi yasaka a mota inda security suka take mashi baya dan yi mashi rakiya zuwa gidanshi kamar yadda yabuk'aci hakan dan akula da lafiyarshi, bud'e mashi mota akayi yashiga motoci biyar ne a gaban wadda yake ciki sai biyar a bayanta duk na masu kula da shi, yana zaune a gidan baya ya kame nan wayarshi tafara ringing.
'Daukota yayi yai picking fuskarshi d'auke da murmushi yake wayar yana cewa nan da mintuna kad'an zan iso gida kujirani, wani irin burki da aka ja ne yakatseshi daga wayar da yakeyi cikin 'bacin rai yakalli driver d'in yace bakada hankali? Ko bakasan aikinka ba da zaka wani ja burki haka?
Ahankali yace kayi hak'uri megida nan yaja motar suka cigaba da tafiya.
Camera d'in wayarshi yabud'o dan yad'auki kanshi hoto dan yatura ma iyalanshi kamar yadda suka buk'ata nan yak'yalla juyo da wayar yayi dan yaga hoton da yayi abinda yagani ne acikin wayar yai mummunan d'aga mashi hankali nan take yafara zufa cikin d'aga murya yace ma driver tsayar da motar nan!!!

K'iiittttt driver yaja mota yatsaya, security na ganin haka su ma duk suka tsayar da motocinsu, Alhaji Tanimu yana jin mota ta tsaya baijira aka bud'e mashi ba yabud'e dakanshi cikin sauri yafita yatsaya tsakiyar security yana mazurai.
Tambayarshi sukayi ko lafiya.
Hoton da yad'auki kanshi yanuna masu yace kuduba kugani wallahi aljanah ta biyoni har ta shigar min a hoto

Amsar wayar sukayi cikin sauri suka duba sai kuma suka mik'a mashi sukace basuga komai ba.
Amsa yayi yasake kallo shima baiga komai ba nan yasaki ajiyar zuciya.

Driver d'inshi ne yace ranka yadad'e k'ila idanunka ne sukayi maka gizo kaga kamar aljanah ammah ni dai banga komai ba.
Katseshi yayi yace dallah malam rufe ma mutane baki, yanzu kowa yashiga mota mucigaba da tafiya


Kowa komawa yayi yashiga mota nan aka cigaba da tafiya.

Alhaji Tanimu zaune yayi yai shuru duk a tsorace yake dan shi macemacen nan sun d'aga mashi hankali sosai musamman ma ta k'anenshi ya zama dole da ya yi masu gaisa zuwa gobe zai tattara iyalansa sukoma chan Europe da zama dan chan yafiye mashi kwanciyar hankali.

Yana cikin tunanin wayarshi tafara ringing dubawar da zaiyi da mamaki sai ganin number d'in Malam Salahu driver d'inshi yayi mamaki duk yakamashi yace wannan kiran fa bayan gashinan yana tuk'i shine kuma yake kiranshi.
Sharewa yayi har ta tsinke a karo na biyu wani kiran yasake shigowa da wata sabuwar number, tsaki yaja sannan yai picking daga chan 'bangaren yaji muryar driver d'inshi ya ce 'Dallabai gani na iso Airport d'in banganka ba kuma antabbatar min cewa jirginku ya safka.

Cikin Alhaji Tanimu murd'awa yayi sai ji kayi wani abu k'ululululuuu lokaci guda tsoro yad'arsu a ranshi yace Salahu kana nufin ba kai bane kazo d'aukata?
Daga chan 'bangaren cikin rashin fahimtar maganar megidan nashi yace 'Dallabai ai cemin kayi sai goma da ishirin saisa ban zo ba sai yanzu, Alhaji tanimu sakin wayar yayi a tsorace yalek'a mazaunin driver dan ganin wanene zaune sai gani yayi wayam motar babu kowa ita kad'ai take tafiya.
K'ara yasaki da dukkan k'arfinshi baisan lokacin da fitsari yakubce mashi ba nan yakai hannu zai bud'e murfin motar yafad'a waje dan bai damu da ko yaji ciwoba indai zai fita yatseratar da rayuwarshi sai ji yayi k'ofar a rufe take, bubbuga glass yashiga yi yana k'walah ma security kira a tunaninshi ta hakan zasu jiyoshi ammah babu ma wanda yasan yana yi, k'ara kallon mazaunin driver yayi yaga ba kowa still dai motar ita kad'ai take tafiya sai shi da yake zaune a cikinta, nan take yasume a inda yake zaune.........












_Sis Nerja'art✍🏻_[7/24, 11:11 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Award Together]


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai biya d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction ta wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_



*PAGE 6*

....Kamar an tadashi haka yafarfad'o daga suman da yayi nan yafara tunani Allah yasa mafarkine ba gaske ba abinda yagani, k'ara lek'awa yayi yaga motar dai ita kad'ai ce take tuk'a kanta nan gabanshi yacigaba da dukan ukku ukku, motsin da yajine a kusa da shi yasa yai zumbur yawaiga, wata mata ce yagani zaune gefenshi sanye cikin shiga ta alfarma ta dad'e fuskarta da bak'in glass ta juya baya tana kallon tagar mota.
Saurin ja da baya yayi tare da jinginewa a jikin murfin mota kan kace mi zufa ta wanke mashi fuska dak'yar yabud'e bakinshi yana rawa yace dan Allah kiyi hak'uri kitafi ku kuke ganinmu ba mu muke ganinku ba.
Juyowa tayi tare da bushewa da wata irin mahaukaciyar dariya, ahankali glass d'in fuskarta yacire kanshi nan take kyakkyawar fuskarta takoma wata irin mumunan halitta wadda ta ida firgitashi, har saida yakusan sake wani sumar yaji an wanka mashi wani gigitaccen mari ba shiri yafarfad'o, wata irin k'ara yasaki a tsorace tare da kai hannu zai bud'e k'ofar motar sai ji yayi an rik'e mashi hannu gam har saida yasake sakin k'ara.
Wata irin mummunan murya marar dad'in saurarece tafara fitowa daga bakin matar muryar da tasa gabad'aya motar saida ta amsa....Alhaji Tanimu bazan ta'ba barinka ba yadda kayi silar mutuwar mijina kaima ya zama dole kamutu!!!
Cikin Alhaji Tanimu katsawa yayi baisan lokacin da yafara zawo ba, cikin rawar murya yace kiyi hak'uri wallahi bansan komai ba, babu wanda nakashe dan Allah kibarni da raina.
Bushewa tayi da wata mahaukaciyar dariya tace bai kamata ace ka mance zunubin da ka aikata ba na kashe Alhaji Muhammad.
A firgice yamaimaita sunan yace Alhaji muhanmad?
Maimakon tabashi amsa sai cewa tayi kaduba kaga motocin da suke zagaye da kai gaba da baya saidai duk da wannan tsaron ya zama dole kamutu domin na dad'e ina jiran wannan ranar bayan kun raba mijina da ranshi ni kaina baku barni ba saida kuka ga bayana sannan dukiyar d'iyata kun cinyeta saboda zalunci irin naku.
Had'e hannuwa yayi waje guda jikinshi yana rawa yace dan Allah kiyi min rai wallahi bansan komai ba akai indai dukiya ce nayi maki alk'awali zan mallaka maki dukan abinda namallaka kar kikashe ni.
Cikin k'araji tace mutuwarka ta zama dole Tanimu rayuwarka batada sauran amfani domin maha'inci irinka baidace yacigaba da rayuwa ba, duba agogo kaga daidai lokacin da yadace kamutu ya yi nasan bakada wata wasiyya da zaka bayar tunda babu ma wanda zaka ba a kusa.
Alhaji Tanimu yana yin yunk'urin yin magana sai ganin hannun matar nan yayi ya cafki wuyanshi, numfashinshi d'aukewa yafara yi nan yacigaba da yunk'urin magana ammah yakasa, dariyar mugunta tashiga k'yalk'yatawa, nan idanuwanshi duk sukayo waje saboda tsananin shak'a, jijiyoyin kanshi duk suka mimmik'e hannu yasa zai k'wace kanshi daga mak'arar da tayi mashi ammah baida k'arfin haka dan gabad'aya k'arfinshi ya tafi nan yafara shure shuren mutuwa, saida taga jikinshi ya saki alamun ya mutu sannan tak'yaleshi tabushe da wata irin mahaukaciyar dariya daidai lokacin motar tafara kauce layi tana tafiya tana karkacewa lokaci guda tatsaya a saman titi nan duk sauran motocin suka tsaya ana tunanin lafiya motar Alhaji tai irin wannan tsayawar cikin sauri duk suka fito suka nufi wajen motar suna zuwa suka k'wank'wasa glass ammah shuru, sun dad'e tsaye a wajen ganin suna neman had'a go slow yasa d'aya daga cikinsu yafasa glass d'in da mamaki sai ganin Alhaji sukayi a kwance shi kad'ai cikin motar babu driver cikin sauri suka bud'e motar ganin kokad'an baya numfashi yasa suka d'aukeshi cikin sauri suka nufi asibiti inda wasu suka tsaya suka kira jami'an tsaro nan da nan titi yacika da mutane ana ta kora jawabi saidai abinda yafi d'aure masu kai babu driver kuma tunda suke tafiyar basuga lokacin da mota tatsayaba har driver yafita suna cikin wannan halin ne wayar Alhaji Tanimu tafara ringing d'aya daga cikin jami'an tsaro ne yad'auko wayar ganin driver d'in Alhaji ne yake kira yasa yai picking batare da ya yi magana ba, daga chan 'bangaren akace Alhaji ga dai ninan airport d'in ina ta jira ko jirgin da yasafka ba naku bane?
Jami'in tsaro ne yace kana magana da jami'an tsaro muna buk'atar ganinka a yanzu.
Wani wahalallen yawu yahad'e yace 'yalla'bai lafiya? Me yake faruwa? Ina Alhaji?
Bai bashi amsaba saidai yafad'a mashi inda zaizo yasamesu.


Cikin dak'ik'a kad'an ya iso wajen cikin d'aya daga cikin motocin Alhaji nan fa kowa mamaki yakamashi DPO yakalli security's yace wannan shine kuke nufi?
Sukace eh Ogah shine mune dai zai raina ma hankali yafita bayan ya kashe Alhaji yaje yad'auko wata motar.

Cikin rashin fashimtar maganarsu driver yace d'alla'bai me yake faruwa ne? Ina Alhajin?
DPO yace koma menene muje station yanzu a chan sai kayi bayanin komai.
Bayani kuma? Wani abune yafaru d'alla'bai?
Maimakon yabashi amsa sai ma ankwa da yasaka mashi nan suka tafi da shi station.


Koda aka kai Alhaji Tanimu asibiti nan aka tabbatar da mutuwarshi dan haka aka d'auki gawarshi aka kai gida hankalin iyalenshi ya tashi sosai nan sukaita kuka.
DPO ne yafad'a masu wanda ake suspecting da yin kisan nan fa kowa yaita mamaki.





Barr Faruk ya shiga damuwa sosai

15 / 74