Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Fansar RAI Complete 1&2 Complete Hausa Novel by SIS Nerja'art

Author :  SIS NERJA'ART Category :  African Stories & Novels

Chapter   50 / 74

147K to 150K   out of 220.3K words

tamaida kallonta ga Aljanar d'an guntun murmushi tayi sai kuma tahad'e fuska lokaci guda sannan tace na tsaneki ke ba Ammina bace.

Bushewa tayi da dariya a karo na ba adadi saida tayi me isarta sannan tace kidaina furta kalmar tsana agareni ya zama dole kidinga min biyayya.

Cikin d'aga murya jawahir tace baza'ayi maki biyayya ba daga yanzu ina so kifita daga rayuwata babu ke babu ni idan har kika sake shiga rayuwata zan kasheki!

Wata irin k'ara aljanar tasaki tace wannan kuskure ne kike aikatawa jawahir.

A fusace jawahir tanufi wajenta da gudu rik'e da wannan wuk'ar tun kan ta isa Aljanar tanuna ta da yatsanta me kama da sanda sai ga wata iska ta taso tana zuwa sai d'aukar jawahir tayi tai wurgi da ita sai gata chan gefe ta fad'a ta baya dak'arfi.
Kwance tayi k'asa tana jin wani irin zafi a bayanta, chan kuma tayi yunk'uri tatashi zaune.
Matsowa Aljanar tayi kusa da ita tamik'a mata hannu alamun tamik'o hannunta.
Hawaye ne suka cigaba da fita daga idanun jawahir ba tare da ta mik'a hannunta ba tace na tsaneki Ammi kikasheni kawai kamar yadda kika kashe Yaya Umar inko baki kasheni ba ni zan ga bayanki bana k'aunarki.


Muryar Aljanar ce tafara fita bibiyu tace wannan kuskure ne kike aikatawa na gargad'eki akan kidaina cewa kin tsaneni ammah kin k'i to dasannu zani azabtar da ke yadda baki tunani kisaurareni.



Alhaji Tanimu koda ya iso gidan a k'ofar da zata sadaka da cikin gidan yatsaya yakira wayar Alhaji Mu'azu ammah har ta k'arashi ringing bai d'agaba kusan missed call biyar yayi mashi yana shirin yin na shidda ne yajiyo anfasa k'ara a cikin gidan dan haka cikin sauri yanifi cikin gidan yana shiga yai sallama yaji shuru a parlor yafara jiyo kuka ahankali yana tashi dan haka yanufi parlorn yana d'aga labule da gawar Alhaji Mu'azu yafara cin karo.....








_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:11 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Award Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 9*


Cikin sauri yashiga parlorn yanufi wajen gawar tashi yatsaya cike da firgita yace Alhaji Mu'azu lafiya? Kwanciyar me kakeyi nan ko bakada lafiya ne? Jin sautin kukan jawahir yasa yajuya sai a lokacin yakula da ummah da ke shimfid'e k'asa itama babu alamun numfashi atare da ita gefe guda kuma jawahir ce wajen gawar Umar tana jijjigashi tana kuka, tsorata yayi sosai cikin sauri ya isa wajen jawahir yana zuwa akid'ime yace ke me yasamesu ya akayi suke a nan ba dai mutuwa sukayi ba dai ko?
Ko d'agowa batayi takalleshi ba bare yasa ran samun amsar tambayarshi ganin haka yasa yace tambayarki nake me yafaru da su?
Nan ma shuru wuk'ar da yagani gefenta ne yasa a fusace yace bazaki bani amsar tambayar da nake maki ba? Sai a lokacin tajuyo takalleshi da rinannun idanuwanta da suka fara firgicewa kallo d'aya tayi mashi tad'auke kai shi kanshi saida yasha jinin jikinshi ammah hakan baisa yayi shuru ba jinjina kai yayi yace wannan mutuwa sukayi kuma nasan kece kika kashesu, mi yasa zaki kashesu? Me suka aikata maki? Wallahi bazan ta'ba barinki ba ya zama dole hukuma tasani kema akasheki.
Mik'ewa tayi tsaye bai ankaraba kawai sai ganinta yayi gabanshi baisan lokacin da ta isoba har saida yad'an tsorata, kallonshi tatsaya yi bata ko k'yaftawa ganin haka yasa yad'an ja da baya dan yanayin kallon da takeyi mashi na tuhuma ne cikin dakewa yace ke lafiya ko nima kasheni zakiyi kamar yadda kika kashe sauran? Wallahi sai na sanar da hukuma.

Sai a lokacin tabud'e baki dak'yar cikin dashewar murya tace Alhaji Tanimu Nepa ka zo ne dan ka amshe sauran dukiyata a wajen Abba ko?

Gabanshi wani irin mummunan fad'uwa yayi dak'yar yahad'iye wani yawu dake mak'ale cikin bakin shi nan yafara inda inda yace ni ni kuma? A'a ni ni ziyara nakawo mashi.

'Dan guntun murmushi tayi tace na san komai,, matsowa tafara yi wajenshi yayi saurin ja dabaya yace k'aryane ni bansan komai ba akan dukiyarki wai ma wacece ke?
Binshi tafara yi yanda cigaba da yin baya baya tace tabbas nasan haka kuma nasan kana da hannu akan mutuwar mahaifina kaima.

Tsorata yayi sosai da jin maganar da tayi cikin ranshi yace wanene yasanar da ita mune muka kashe iyayenta bayan lokacin da mukayi maganar a d'aki muka yita mu takwas ne acikin gidan babu wani mahaluki a ciki toh ammah kuma....muryarta yaji ta ce wannan haka yake na san kana da hannu a ciki.
Hanyar k'ofa yanufa yana cewa a'a bansan komai ba akan mutuwarsu.
Tsaye jawahir tayi tana kallonshi chan sai tafad'a saman kujera tazauna tare da dafe kanta ganin haka yasa yayi saurin juyawa zai bar d'akin sai jin muryarta yayi ta ce idan har kasanar da wani abinda yafaru sai na kasheka!
Da gudu ya ida fita ko motarshi bai tsaya shiga ba dan kar ma ya'bata lokaci yabar gidan.

Wani irin kuka tadinga yi a nan inda take zaune k'arar wayar da taji kusa da itane yasa tajuya sai ganin wayar Umar tayi tana d'aukowa taga recording ne yayi saving cikin sauri takunna tana saurare taji duk abinda yafaru ne akayi recording a tsorace ta ajiye wayar tana tunanin wanene yayi recording d'in......



Faruk yana gama saurare ajiyar zuciya yasafke ahankali yace watau abinda yafaru kenan dukkansu ta kashe har da Umar? Toh ammah banji.....k'arar buga gida yafara jiyowa ana knocking nan yakalli agogo yaga duka k'arfe d'ayan dare cike da mamaki yace to wanene yake buga gida a wannan lokacin ko dai megadi ne
Mik'ewa yayi sai ji yayi andaina bugawa har zai je yabud'e sai kuma yafasa yakoma yazauna.

Dariya ce yafara jiyowa tana tashi daga wajen tagar d'akinshi dan haka yak'ara sautin karatun alk'ur'ani sannan yacigaba da aikinshi har wajen k'arfe biyun dare sannan yakwanta bacci.



Wajen k'arfe sha d'aya yaje gidan kaso yana isa yasamu jawahir tsaye a wajen da tasaba tsayuwa, tsayawa yayi daga bayanta har ya bud'e baki zaiyi magana sai jin muryarta yayi cikin sheshek'ar kuka ta ce ka yi k'ok'ari sosai da har ka iya ku'buta daga hannun Ammin saidai ina baka shawara kacigaba da addu'a dan itace zata cigaba da tseratar da kai daga sharrinta dan daga baya na gane ba taimako kawai Ammi ta ke ba har da zalunci take tunda har ta iya kashe wanda baida hak'k'i acikin mutuwar Abbu.............


A lokacin da nagama sauraren recording d'in na yi mamaki sosai kuma na tabbatar Yaya Umar ne yayi shi tabbas a ranar na san dole sai police sun zo tunda har nayi sakacin barin Alhaji Tanimu a raye yafita saidai ban yi nadamar abinda Ammi ta aikata ba saidai rad'ad'in mutuwar Mijina da nakeji, cikin sauri nad'auko wayar dan inaso tazama sheda akan abinda na aikata dan akasheni nima sai ji nayi an fizge wayar daga hannuna sai gani nayi ta fad'i k'asa safkowa nayi daga saman kujera zan d'auko wayar sai gani nayi anjata tayi hanyar k'ofa tsayawa nayi ina kallonta sai jin muryar Ammi nayi ta ce bazan ta'ba bari kid'auki wayar nan ba babu wanda ya isa yad'auketa har yasaurari abinda yafaru.
Juyawa jawahir tayi tana waige ammah bata gantaba dan haka tafara takawa saida tad'auki diary d'inta da Umar yashigo da shi parlorn, sannan tanufi wajen k'ofar sai wayar tacigaba da tafiya tafita daga cikin d'akin motsin da takeji a bayantane yasa tagane Ammi tana bayanta dan haka tacigaba da tafiya har saida takai wajen wani bokitin k'arfe da tafiddo d'azu zata d'ibi ruwan mopping tagoge kitchen dan a lokacin da akayi abin 'yar aikinsu ta je gidansu zata kwana biyu, rarimo bokitin tayi cikin sauri tajuya daidai lokacin da Ammi take bayyana cikin zafin nama tabuga mata shi a kai, sannan tayi wurgi da shi da sauri tad'auki wayar dagudu tanufi d'akin 'yar aikinsu da bakomai a cikinshi tana shiga tazauna k'asa jikinta yana rawa tabud'e wayar taciro Memory card d'in, dariya tafara ji gabad'aya d'akin yana amsawa da ita cikin wata irin kakkausar murya taji muryar Ammi tana cewa kin aikata kuskure jawahir bazaki ta'ba yin nasara ba akan abinda kike son samu.
Rik'e memory d'in tayi gam a hannunta cikin rawar murya tace k'arya kike Ammi baki isa kihana ni samun abinda nakeso ba, na fad'a maki kifita daga rayuwata bana sonki na tsaneki.
Wata irin k'ara taji anfasa sannan cikin muryar fushi taji Amminta tana cewa ina gargad'inki da furta kalmar tsana agareni jawahir domin hakan zai iya jawo maki shiga cikin wani irin mawuyacin hali a rayuwarki.
Cikin kuka tace taya zan daina tsanarki bayan kinyi amfani da jikina da hannuna wajen kashe mijina? na tsaneki Ammi, tana fad'in haka tahad'e kai da gwiwa tacigaba da rusa kuka.



Bayan fitar Alhaji Tanimu wayarshi yad'auko yakira DPO yashaida mashi abinda yafaru nan DPO yace yajirasu gasunan zuwa.

Jawahir tana cikin kukan tajiyo jiniyar motoci ammah hakan bai sa tad'ago ba dan tasan daman tabbas sai hakan ya faru, tana jiyosu suna shigowa cikin gidan inda wasu duk suka zagaye gidan parlor suka fara shiga inda suka ga su Alhaji Mu'azu kwance, tsaye sukayi a wajen gawarwakin suna dubawa DPO hana kowa yayi yata'ba gawarwakin yace aje azo mashi da duk wani mahaluki da yake cikin gidan sannan yakira likita a waya.

Tana jiyo police suna bud'e sauran d'akuna ammah bata motsaba har suka shigo cikin d'akin da take zaune tsawa suka daka mata sukace me take a nan bata ko d'ago kai ba bare har tatanka masu dan haka biyu daga cikinsu suka shugo suka kamata memory d'in ne yakubce daga hannunta yafad'i tana so tayi magana ammah takasa babu wanda yalura da shi daga cikinsu saidai suka d'auko wayar Umar suka fita da ita a parlor suka kaita suka zaunar da ita k'asa inda tatadda megadinsu shima a zaune yayi zugum yana kallon gawarwakin iyayen gidanshi.

DPO kallonta yayi sannan yamaida kallonshi ga Alhaji Tanimu dake tsaye wajen gawar Abba yace wannan ce Alhaji?.
Kallonta Alhaji Tanimu yayi sannan yace Eh itace tabbas ita takashesu.
Daidai lokacin likita ya iso yana duba Abba da Yaya Umar yace ai sun mutu ammah ummah suma tayi dan haka aka tafi da ita asibiti.

Matsowa DPO yayi yatsugunna gabanta yana k'are mata kallo har lokacin kanta sunkuye k'asa tana hawaye jinjina kai yayi yace me zakice a game da mutuwar mutanen nan?
Shuru tayi bata amsa mashi ba, damk'o gashinta yayi tayi saurin runtse idanunta yace tambayarki nake shin kece kika kashesu?
A nan ma ban bashi amsar tambayar da yayi min ba muna a haka aka kawo mashi hoton Yaya Umar da na Abba wanda Ammi ta ajiye min ansa maker an yi masu tick koda yaduba yaga exactly irin wanda duk yatsinta ne lokacin da aka kashe su Alhaji Jamilu dan haka yasa aka kamani aka tafi da ni policestation aka rufe ni tsawon kwana biyu yana bincike inda yatabbatar da nice nayi kisan daga nan yamakani a kotu, kwana biyun nan da nayi kusan kullum sai Alhaji Tanimu ya zo ya dubani abinda yake bashi mamaki bana tare da wata damuwa atare da ni kuma har lokacin ban bud'e baki nayi magana ba, duk zuwan da Alhaji Tanimu yakeyi so kawai yake imbud'e baki in amsa ma police nice nayi kisan ammah nak'i a ranar da aka mik'a case d'ina kotu koda yazo yake tambayata shin ko akwai hanyar da zanbi inkare kaina a kotu?
'Dan guntun murmushi nayi ganin shi kad'ai ne a wajen yasa nace kar kadamu da wannan saidai ina so kaje kafara shiri dan kaine mutum na gaba da zaka bak'unci lahira.
Dariyar mugunta yayi yace taya kike tunanin zaki kasheni bayan ke hukuncin kisa ne za'a yanke maki bazan ta'ba bari kibar gidan ba koda kin bari a gidan kaso rayuwarki zata k'are, , sannan duk wasu takardu da suke mallakinki na samu nasarar d'auko su a cikin gidan ku zan mallake dukkan dukiyarki hatta ta cikin account d'inki zanyi k'ok'arin ganin na mallaketa.
Murmushi tayi a karo na biyu tace wannan ba matsala bane saidai inaso kasani daga kai har wad'anda kake tare d su babu wanda zai iya tsere wa daga hannuna dole sai kun mutu kamar yadda sauran suka mutu.

Dariya Alhaji Tanimu yadinga yi har saida aka zo aka koma da jawahir d'akin da take a rufeta.

Ranar litinin aka zo aka d'auketa cikin motar 'yansanda aka tafi da ita kotu koda aka je batace uffan ba tana ganin lauyoyi biyu suna ta fafatawa da wani lauya da taso taganeshi ammah takasa wanda yake a matsayin shi yake kareta har aka gama shara'ar bata fahimci komai ba tana ji ana ta mata tambayoyi saidai tabisu da idanu.
Ganin bata amsa cewa itace tayi kisan ba yasa Alk'ali yayanke mata hukuncin zama gidan yari na tsawon sati biyu kafin adawo zama na biyu, daga nan kotu aka wuce da ita gidan mata inda aka had'eta d'aki guda da wasu mata biyu masu irin laifinta na kisa,, saidai su kallo d'aya zakayi masu kaga babu alamun imani atare da su mugaye ne nan fa suka fara mata gani gani tare da nema surainata.
Saidai duk wannan baisa jawahir takula su ba saidai tayi zaune waje d'aya tayi shuru tana jinsu suna ta hira ammah bata kulasu ko kad'an bataga alamar damuwa a tare da su akan zaman da suke a cikin gidan kason nan ba, inda ita kuma saboda rashin sabo yasa takasa sakewa tana ji gabad'aya rayuwar ta canza mata saidai ko kad'an batayi nadamar abinda ta aikata ba, kusan kullum sai anzo anfita da su an kaisu sunyi aiki me wahala, a duk lokacin da suka fita dan yin aikin jawahir bata k'ara sanin inda hankalinta yake har sai anmaidasu d'an kurkukun d'akinsu.



Bayan sati d'aya lauya me kareta yazo aka fiddota aka kaita wajen da aka tanada dan ganawa da me laifi idan aka zo ziyartar shi musamman ma lauyoyi idan har lauyan ya buk'aci haka, koda tazo taga shine wanda taga yana kareta a kotu tsayawa tayi tana kallonshi murmushi yayi yace sannu jawahir na san dai kin sanni a matsayina na abokin mahaifinki yakamata kikwantar da hankalinki kinutsu ki amsa min duk tambayoyin da zanyi maki ni zan taimaka maki kifita daga gidan nan.
Tunda yafara magana idanu tazuba mashi tana kallonshi har yakai aya sai a lokacin tayi murmushi tace Barr Mubarak ko?
Shima murmushin yayi yace Eh haka ashe kin gane ni ai na d'auka bazaki iya tunani ba tunda tun bakida wayau sosai narabu da zuwa gidanku, nayi mamaki sosai da yakasance d'iyar abokina ce take rayuwa a nan gidan kaso har ake yayata labarinta a gari akan cewa ta yi kisa wannan dalilin ne yasa nazo inwanke ki akan zargin da akeyi maki.
Tarar numfashinshi tayi tace ba wai zargi ba Barrister bana buk'atar taimako irin naka domin baka dace kataimaka min ba katafi kawai.
Murmushi yayi yace baidace kice haka ba ga wanda yakeson taimaka maki.
Itama murmushin tayi cikin alamun nuna rashin damuwa tace fiye ma da hakan zan ce gareka barrister katafi kawai kanuna tausayawarka ga wani na daban ba wai wacce takasance abokiyar gabanku ba.
Da mamaki yake kallonta yace abokiyar gabanmu fa kikace? Wacece abokiyar gabanmu kuma ni da wa?
Ta'be baki tayi tace na san ka san komai, koma me kenan da sannu zan fahimtar da kai.


Haka suka rabu Barr Mubarak bai samu had'in kan jawahir ba a rana ta biyu koda yadawo nan ma bai samu yadda yakeso ba har suka zauna zama na biyu a kotu nan ma bata amsa laifinta ba akan zargin da akeyi mata dan haka akace ak'ara mata wata d'aya a gidan kaso sannan adinga sata aiki me tsanani.


Saida tayi sati biyu tana faman wahala duk wani aiki me wuya ana sata saidai abinda zai baka mamaki jikinta bai ta'ba nunawa ba, a lokacin da take sati na ukku ne Barr Mubarak yazo dan yagana da ita koda aka fiddota wajen da zasu gana kallonta yayi yai murmushi yace sannu malama jawahir
Idanu tazuba mashi batare da ta ce komai ba ganin haka yasa yacigaba da cewa jawahir taurin kanki ya yi yawa kin sanni kuma kinsan taimaka maki zanyi kisamu kifita da gidan nan dan baidace da ke ba a matsayinki na d'iyar babban mutum irin Alhaji Muhammad kibani had'in kai intaimaka maki.


Idanu tazuba mashi batare da ta ce komai ba ganin bata da niyar yin magana yasa yad'auko wasu takardu yamik'a mata yace amshi wannan signing kawai nakeso kiyi min idan har kikayi ni kuma na yi maki alk'awalin zan taimaka maki wajen ganin kin bar gidan nan.
Kallon takardun tayi sai taga na filaye ne guda biyu ga sunan Mahaifinta nan a jikin takardun, d'an guntun murmushi tayi sannan tace ba wai ka zo da niyar taimako na ba kawai dai kace ka zo da niyar cin dukiyata kaima, a matsayinka na abokin Abbuna baka kasance mutumin kirki irinshi ba.

Kinga ba wannan natambayeki ba indai har kinason barin gidan nan ya zama dole kiyi abinda nakeso inko ba haka ba kina ji kina gani za'a kasheki.
Matsowa tayi kusa da shi tace toh menene dan na je inda iyayena sukaje!
Ko ance maka bansan lokacin da kaje katsaya ma Abba ba wajen ganin kun k'wace ma Ammina hak'inta ta k'arfi da yaji ba? Kasan komai akan dukiyar mahaifina ammah son zuciya yahana kafad'i gaskiya, kuma tabbas nasan su Alhaji Tanimu ne suka turoka wajena, tir da hali irin naka.

Dariya Barr Mubarak yayi yace dakyau na ji dad'i da kika gane hakan a yanzu tunda kinsan halina ya kamata ki cika wad'annan takardun dan samun ku'butar ki daga gidan nan inko ba haka ba a banza zaki mutu sannan dukiyar da take mallakinki zata dawo k'ark'ashinmu hatta companyn mahaifinki kinga shikenan zuri'ar Muhammad me shadda ta zama tarih.....bai gama rufe baki ba tayi kukan kura tayo kanshi kafin yayi

50 / 74