Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Fansar RAI Complete 1&2 Complete Hausa Novel by SIS Nerja'art

Author :  SIS NERJA'ART Category :  African Stories & Novels

Chapter   59 / 74

174K to 177K   out of 220.3K words

rasa rayuwarta gashi na yi mata alk'awalin zan taimaketa kukwantar da hankalinku babu abinda zai faru da ni ina akan gaskiyata ubangiji yana tare da ni basu isa suyi min abinda Allah baiyi min ba su d'in azzalumai ne barinsu a doron k'asa daidai yake da cigaba da yad'uwar zaluncin su sannan.....wani irin gigitaccen mari Dad yad'aukeshi da shi wanda yasa saida yai saurin ja da baya tare da dafe kuncinshi yana kallon mahaifin nashi.
Mom ce tace ka min daidai Alhaji.
Cikin fad'a Dad yace kai wane irin shashasha ne wanda baisan abinda yakeba watau mu zakayi ma wa'azi ko? Toh bari kaji indai har mune iyayenka ya zama dole ka ajiye aikin nan yau yau d'innan.
Inkuma ba haka ba saidai yaza'ba ko mu ko aikin,,, cewar mom cikin 'bacin rai.

Runtse idanunshi yayi da suka kad'a sukayi jajir sannan yasulale yazauna k'asa dirshen ahankali yafara furta innalillahi wa'inna ilaihiraji'un, sannan yabud'e idanunshi yasafkesu akan iyayenshi muryarshi tana rawa yace Dad dan Allah kuyi hak'uri kutaimaka min kunsan girman alk'awali....mom ce takatseshi tace wallahi Faruk kasake magana sai na k'ara maka wani marin, aikine mun hana shi kuma idan har kai ka isa da mu kaje kayi yadda kakeso,,, tana fad'in haka tawuce a harzuk'e tabar wajen.
Dad ma bayanta yabi suka bar Faruk nan zaune dirshen a k'asa, duka hannunshi yasa yadafe kanshi yace wannan wace irin *K'ADDARA CE* menene yake shirin faruwa da ni? Me yasa su Alhaji Mansur basubar abun a tsakaninmu ba saida suka saka iyayena a ciki? Ya jawahir zataji idan har taji labarin na janye?
Wasu siraran hawaye ne suka gangaro mashi yace Mom Dad meyasa kuka kasa fahimtata?
Wayarshi ce tafara ringing yashare kamar bazai d'agaba sai kuma yad'auko yana dubawa sai ganin number d'in Alhaji Mansur yayi dan haka yayi picking cikin 'bacin rai.
Dariya ce tafara tashi sannan akace ya kaji salon namu Barrister? Ina fatan dai a yanzu ka janye gudun kar wani abu yasameka dan nasan iyayenka bazasu ta'ba jure ma rashinka ba.

Murmushi yayi cike da takaici sannan yace hakan bazai ta'ba sawa injanyeba ina nan akan bakana, tabbas a yanzu na tabbatar ku d'in matsorata ne da har kukeson janyewata, ba jarumta bace ace kun biyo ta 'bangaren iyayena nine nan daidai da ku dani yakamata kukara.

Daga chan 'bangaren akace kana nufin bazaka janyeba kenan?
Eh ina nan aka bankana sai na kunyataku a idanun duniya idan har ina da numfashi kowa sai ya san ku d'in azzalumai ne.

Dakyau Barrister kai d'in ka cika taurin kai ammah dasannu zamu saitaka muzuba mugani.
Tsaki yaja sannan yakashe wayar ranshi duk a 'bace, wajen yayi zaune dirshen yana tunanin ina ma ace iyayenshi zasu fahimceshi ammah yanayin da yagansu ya san bazasu ta'ba fahimtarshi ba musamman Dad da yake kaifi d'aya, yana nan zaune yana neman mafita aka fara kiran sallar la'asar Dad yafito yawuce masallaci ko kalllon inda yake baiyi ba dan haka shima yatashi cikin sanyin jiki yanufi part d'inshi cikin sauri yawatsa ruwa sannan yad'auro alwallah yana fitowa yasaka kaya yad'auki wayarshi cikin sauri yanufi masallaci dan har antada sallah a lokacin.

Saida yarasa raka'a biyu, bayan ya gama sallah zaune yayi a masallacin duk yana jinshi wani iri saidai yana kallon hakan akan abinda yafaru tsakaninshi da iyayenshi, saida yaga za'a fara sharar masallaci wajen k'arfe hud'u da rabi sannan yafito cikin sanyin jiki yataka yanufi gida, yana cikin tafiya sai ganin wata jeep yayi ta faka a gabanshi anbud'e k'ofar baya ko kallonta baiyiba yawuce zai tafi sai ji yayi ance dan Allah malam muna da tambaya.
Juyowar da zaiyi nan aka watsa mashi wani farin abu a fuska, runtse idanunshi yayi nan yanemi yaruga suka jawoshi da k'arfin tsiya suka saka a mota daga nan bai sake sanin inda kanshi yake ba.




Ahankali yafara bud'e idanunshi yana maidawa yalumshe, jijjagashi da akayine yasa yabud'e idanunshi nan yafara ganin mutanen da suke tsaye bibiyu, runtsewa yayi yasake bud'ewa sai ganinshi yayi cikin wani d'aki tsakiyar wasu mutane su biyar kowanensu d'auke da makami, yunk'urin tashi yayi sai a lokacin yajishi d'aure tamau, kallon kujerar da yake zaune samanta yayi ta roba and'aure mashi hannuwa da k'afafuwa, abinda yafaru da shine yafad'o mashi a rai yakalli mutanen da suke zagaye da shi dukkansu babu wanda fuskarshi take da kalar imani, d'aga murya yayi yace suwanene ku? Meyasa kuka kawoni nan?
Su duka shuru sukayi suna kallonshi.
Ganin haka yasa yakwatsa masu tsawa yace bakuji ina tambayarku nace wanene yakawoni nan wajen? Ko ku kurmaye ne?
Daidai lokacin aka bud'e k'ofa aka shigo da mamaki yake kallon wanda yashigo ahankali yace Alhaji Mansur?
Murmushi yayi yace tabbas nine barrister ashe ka farka ai tun jiya muke nan tare da kai kana ta bacci lallai da alama baccin ya yi maka dad'i.
Gabanshi wani irin mummunan fad'uwa yayi yace kana nufin tun jiya nake nan wajen?
Dariya Alhaji Mansur yayi yace sosai ma ai ba abun mamaki bane.
Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un Alhaji Mansur me yasa ka aikata min haka, ashe daman kaine kasa aka d'auko ni?
Kujerar da take kallon inda Faruk yake zaune yajawo yazauna sannan yace toh ya ka iya tunda taurin kanka ne yaja maka, kaga yanzu cikin ruwan sanyi na satoka yanzu kana nan tare da mu jibi bazamu shiga kotu da kaiba.

Shuru Faruk yayi yana tunanin halin da iyayenshi zasu shiga idan suka nemeshi basu ganshiba, cikin karaya yace Alhaji Mansur hakan da kayi bai dace ba domin ina akan aikina ne ba wai ina yin hakan dan in tozartaku ba.
Bushewa da dariya yayi yace ashe zakayi saurin karaya haka ban yi zaton haka ba saidai ka makaro Faruk, tunda har nagargad'eka baka jiba toh a nan zaka cigaba da rayuwarka da mutanena.

'Dagowa Faruk yayi yakalli mutanen d'aya bayan d'aya sannan yayi murmushi yace ban damu da duk abinda zakayi min ba Alhaji Mansur tunda ina akan gaskiyata sannan ko da ba ni ba ita yarinyar bazata ta'ba barinku ba sai ta kasheku kamar yadda takashe sauran abokan naku dasannu ku ma zaku bak'unci lahira,
Mik'ewa yayi a fusace yawanka mashi mari.
Saurin runtse idanunshi yayi saboda wani irin zafi da yaji ya ziyarci kuncinshi, d'agowa yayi yakalli Alhaji Mansur cike da mamaki bakinshi yamutu yakasa cemashi komai.
Nunashi da yatsa Alhaji Mansur yayi yace kasan abinda bakinka yake fad'a domin ni d'innan ba kanwar lasa bane na tabbata har yanzu baka ida sanin wanene ni ba, ba kowa bane zai takani yazauna lafiya.
Murmushi Faruk yayi yace wannan marin da kayi min bashi ne kad'auka karubuta ka ajiye wannan.
Alhaji Mansur har ya bud'e baki zaiyi magana nan wayarshi da take hannunshi tafara ringing dubawa yayi sannan yai picking basu ji abinda ake ce mashi ba saidai sukaji yana cewa Eh gashinan ya farka ai yanzu bamuda damuwa abokina kakwantar da hankalinka yana nan wajen a nan zai ci gaba da zama har sai lokacin da yasaduda yadawo hanya inko ba haka ba saidai yakasance tare da mu, dariya yafara kyalkyatawa sai kuma chan yace toh shikenan sai anjima sai mun had'e ai na d'auka zakazo kaga mutumin namu duk wannan jin kan nashi babu shi atare da shi yau, ai kabarshi ina nan da kai sai ya safke girman kan nan nashi,,, suna saurarenshi yagama wayar sannan yakalli Faruk yace toh Barrister daga yanzu ka ga gidanka nan a nan zaka cigaba da rayuwa babu kai babu fita,, sannan ku kuma yanuna wad'annan k'attin biyar yace kucigaba da kula da shi ban yadda ko tsakar gida abarshi yafito ba hatta toilet gashinan cikin d'aki.
Gabad'aya sukace angama oga.
Murmushi yayi sannan yawuce yafita.
Da idanu Barrister Faruk yabishi yana jin wani irin k'unci a cikin ranshi ba komai yad'aga mashi hankaliba sai iyayenshi da baisan halin da suke ciki ba, muryar d'aya daga cikin k'attin yaji wanda da alama shine ogansu ya ce ku zauna nan da shi bari inje indawo.
Amsawa sukayi da toh nan suka wuce suka zauna suna kallon Faruk nan yajingine kanshi a jikin kujerar tare da runtse idanunshi.



A chan 'bangaren iyayen Faruk ganin har dare bai dawoba kuma ga motocinshi duk suna gida dan haka suka fara tunanin ina yaje ko abokinshi yazo suka fita a mota, hankalinsu bai ida tashiba saida dare yayi baidawoba har k'arfe sha biyun dare sannan suka kira wayarshi suka ji ta akashe, atak'aice dai haka suka kwana rabi a zaune ammah bai dawoba.


Wasa wasa washe gari har azuhur bai dawoba dan haka Dad yadinga kiran abokan Faruk da yasani yana tambayarsu sukace basu ganshiba, nan hankalinsu ya ida tashi sukayi tunanin ko mutanen nan suka saceshi, Momcy kuka tadinga yi sosai akan rashin ganin d'an nata haka tashiga mota tadinga zuwa gidajen da tasan yana d'an zuwa ammah babu labarinshi.


Har dare haka suka ci nemanshi ammah babu 'bar'bashinshi ba su ba hatta duk wanda yake kusa da su saida yashiga tashin hankali akan rashin ganin Barrister inda daga k'arshe aka kai cigiyarshi gidajen television da na redio.



Nasiba suna zaune ita da iyayenta a parlor suna kallon news inda ita hankalinta yake akan waya tana chart a nan ne iyayenta sukaga hoton Barr Faruk an dallo ana cigiyarshi, jin sunan wanda ake cigiyane yasa tayi saurin d'ago kai tamaida kallonta ga TV gabanta wani irin mummanan fad'uwa yayi tace na shiga ukku Daddy Mummy kuduba min wallahi Faruk ne ake cigiya me yafaru da shi?.
Murmushi Alhaji Sufyan yayi yace tabbas wannan Faruk ne ikon Allah ko ya akayi haka, yanzu haka wajen iya yin shi ne yayi ma wad'anda suka kasa hak'uri suka d'aukeshi ko kuma wannan yarinyar takasheshi.
Hajiya Maijidda rik'e baki tayi tace na shiga ukku yanzu Faruk d'inne ya'bata tun shekaran jiya?
Nasiba da tayi mutuwar zaune hankalinta ya tashi sosai kasa cema iyayen nata komai tayi tana ta kallon hotunanshi da ake dallawa a TV ana cigiya chan sai ga hawaye sun fara fita nan tasa ma iyayenta kuka.
Su dukansu kallonta sukayi cike da mamaki sukace ke kuma kukan me kikeyi?
Cikin kuka tace Daddy Faruk d'ina ba'a ganshi ba ya 'bace .
Daddynka fusata yayi yadaka mata tsawa yace ke bana son shashancin banza ai ba ubanki bane ya'bace da zaki ma mutane kuka kuma yaushe Faruk d'in yazama naki wannan azzalumin maci amana, inma banda abinki miye abun tada hankali kan 'bacewar wanchan butulun?
Cikin sheshek'ar kuka tace wallahi Daddy Faruk ba mugu bane mutumin kirkine bana son wani abu yasameshi dan Allah muje nemanshi.

Mummynta ce takai hannu tabuge mata maki tace ke dai shashasha ce miye abun tada hankali ga 'bacewar wanda yaso yatozarta mahaifinki yanzu haka rashin mutuncin yayi ma wasu sukaji basu iya hak'uri,

K'ara sautin kukanta tayi tana jin wani irin haushi akan maganar da iyayenta suke marar dad'i akan Faruk dan ita ta san har yanzu tana jinshi a ranta.


Mahaifinta ne yace kibarta kawai Hajiya sai tayi ta yi tunda ita batasan ciwon kanta ba bata kishina duk cin zarafin da yake mana bata gani ni wallahi dad'i ma naji yanzu ai iyayenshi zasu gane abinda muke fad'a masu akan abubuwan da d'an nasu yakeyi tunda su basu iya hanasu.

Mik'ewa Nasiba tayi cikin sauri tajuya tafita daga parlorn tana cigaba da kuka.

Mummynta ce tace oh ni yau naga ikon Allah watau Alhaji yarinyar chan dai da alama bata hak'ura da yaron chan ba.

Cikin 'bacin rai yace kibarta ko kukan jini zatayi bazata ta'ba auren Faruk ba ko da ace yana nan bare ma baya nan dan bazan ta'ba ba irinshi auren d'iyataba.

Shuru Mummyn Nasiba tayi dan ita babu abinda tatsana sama da 'bacin ran d'iyartata dan ma ba hali da ta je ta lallasheta.


Nasiba kuka tadinga yi kamar wadda aka aiko ma da sak'on mutuwa wani irin tausayin Faruk ne taji ya d'arsu a zuciyarta, wayarta tad'auko takira numbers d'inshi dukansu a kashe nan tacigaba da rusa kuka daga k'arshe tatashi tad'auko mayafinta tazari key d'in motarta tabi ta k'ofar baya taficce batare da sanin iyayenta ba.

Tuk'i take ammah kuka takeyi ahaka har ta isa gidansu Faruk, tana isa ko tsayawa rufe motar batayi ba tashiga gidan da gudu, duk mutane ne zazzaune anyi cirko cirko kowa yana jimamin 'bacewarshi tsawon kwana biyu, a parlor tasamu Mom zaune tana ta matsar hawaye ana lallashinta tana zuwa tafad'a jikinta tare da fashewa da wani irin kuka me ban tausayi, cikin kuka tadinga cewa Mom dan Allah ina Faruk? Dagaske ne ya 'bace? Dan Allah Mom kice min Faruk d'ina yana d'akinshi wallahi ina sonshi bana so inrasa shi.
Mom kamar jira take nan itama d'in tafashe da kuka, k'ok'arin k'wace Nasiba akayi daga jikin Mom ammah tarik'eta gam.
Dakyar aka samu aka 'ban'bareta nan takwanta a k'asa tana cigaba da rusa kuka, aka rasa wanda za'a lallasa ita da Mom.

Alhaji Sani Maishadda da abokan Faruk ne suka dinga k'ok'arin zuwa wajaje nemanshi inda a chan garin daura kakanshi yasa aka dinga safkar alk'ur'ani ana sadaka....








_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:14 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Award Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 18*

Mummyn Nasiba saida tafaki idanun mijin nata sannan tanufi d'akin d'iyartata dan talallashi abunta sai gani tayi wayam babu ita nemanta tafara yi tana dubawa a parking space taga babu motarta dan haka tasan ta fita dawowa tayi tasamu mijin nata tace oh ni Alhaji watau yarinyar chan fita tayi daga gidan nan.

Da mamaki yake kallonta yace kina nufin bata nan?
Eh na duba d'akinta kuma naga motarta bata nan.
K'wafa yayi yace watau gidansu Faruk taje dan bata jin magana kibarni da ita zata dawo gidan tasameni.


Har dare Nasiba tana gidansu Faruk hawayen idanunta sun kasa tsayawa fuskarnan duk ta kumbura saboda tsananin kukan da tasha tana zaune gefen Mom koda aka kawo masu abinci daga ita har Mom k'in ci sukayi saida akayi da gaske sannan suka d'an ci, suna nan a haka Barr Junaid da Nas suka shigo saurin mik'ewa tayi tanufi wajen da yake tun kan yayi magana tatari numfashinshi tace Junaid anga Faruk d'ina ko?
Junaid kallon Nas yayi su dukansu jikinsu ya yi sanyi sannan yakalli Nasiba tare da girgiza mata kai.

Ja tafara yi da baya nan wasu hawayen suka wanke mata fuska tace shikenan tunda ku bazaku iya ganoshi ba ni zan je innemeshi da kaina, ni zan iya dawowa da shi.
Barr Nas ne yayi k'arfin halin cewa kiyi hak'uri Nasiba muna bakin k'ok'arinmu ammah har yanzu Allah baisa andaceba insha Allahu zamu gano Faruk kikwantar da hankalinki.

Wajen Mom takoma tatsugunna kusa da kujerar da take zaune tace Mom kin gani ko basu ganoshi ba kidaina kuka ni zanje in nemeshi.

Ganin yadda take magana kamar zararra yasa mom ta girgiza kai tace a'a Nasiba babu inda zakije insha Allahu zasu gano mana shi.
Fashewa tayi da kuka tace Mom har sai yaushe?
Kwantar mata da kanta saman cinyarta tayi nan tafara lallashinta dan batasan abinda zatace mata ba.
Kuka tadinga yi sosai har saida Dad yadawo nan yasamu yalallasheta tadaina kukan ganin har tara ta yi yasa yace tatashi tatafi gida, da fari ta ce babu inda zataje har sai Faruk ya dawo saida Dad yadinga lalla'bata sannan tahak'ura tatashi tatafi.


Tana isa gida a parlor tasamu iyayen nata mahaifinta sai kaiwa da kawowa yake tana shigowa yace daga ina kike?
Batare da ta damu da yanayin da taganshi ba tace daga gidan su Faruk nake...bata rufe baki ba taji ya wanka mata bari.
Saurin dafe kuncinta tayi tare da kallon mahaifin nata cike da mamaki dan wannan shine karo na farko a rayuwarta da yata'ba marinta.
Nunata yayu da yatsaya yace ke har kin isa kitsallake maganata? Da izininwa kika fita daga gidan nan?
Shuru tayi tare da sadda kanta k'asa tana hawaye kanta yayo zai rufeta da duka Hajiya Maijidda tayi saurin shan gabanshi tace a'a Alhaji dan Allah kar kabugeta yarinya ce Nasiba batasan komai ba sai andinga kwatanta mata.
Wata uwar harara yawurga mata yace Nasibar ce yarinya?
Shuru tayi tana kallonshi.
Cigaba yayi da cewa toh wallahi duk lokacin da tak'ara barin gidan nan sai na mugun sa'ba mata ban yarda ko nan da waje tasake fitaba.
Wucewa Nasiba tayi sumi sumi tanufi d'akinta tana ji yana cewa ka ga 'yar iskar yarinya ni zaki maida banza watau ke ga shugabar soyayya ko?

Mummyn Nasiba ce tace Alhaji ayi hak'uri.
Tsaki yaja sannan yawuce a fusace yakoma d'akinshi.


Bayan d'iyartata tabi tana zuwa tasameta zaune saman gado ta dafe kuncinta tana ta kuka, zuwa tayi tazauna kusa da ita tace haba Nasiba meyasa bakiji yanzu gashinan kinja ya doke ki.
'Dago kai tayi takalli mahaifiyartata cikin sheshekar kuka tace Mummy fad'a min menene laifina a ciki? Dan kawai ina son Faruk, ai bani nadasa ma kaina son nashi ba meyasa ake ganin laifina?
Matsowa Mummy tayi kusa da ita tare da dafata tace haba Nasiba kidaina cewa haka kinga kema baki kyautaba ya kamata zuwa yanzu ace kin cireshi a ranki ko dan saboda tozarcin da yaso yayi ma mahaifinki kinga a yanzu mahaifinki yana fushi da ke saboda abinda kikayi baki kyautaba.
Girgiza kai tashiga yi cikin kuka tace Mummy kune zakuga rashin kyautawa ta ammah ni zuciyata gani take hakan shine daidai dan saboda tana son Faruk, indai har abinda nayi a wajenku ba daidai bane to kuyafe min na ji ni me laifi ce saidai bazan ta'ba iya cire son shi ba ammah ina fatan inyi k'ok'arin cireshi a raina ko da ace hakan zai zama sanadiyar mutuwata indai har hakan zaisa infaranta maku.
Rungumeta jikinta Hajiya Maijidda tayi tace a'a Nasiba kidaina cewa haka dan bamuso murasaki munason ki sosai.
'Dagowa tayi takalleta tare da yin murmushi wanda yafi kuka ciwo sannan tace indai har kuna so na to ya kamata kubarni incigaba da kasancewa da soyayyar Faruk dan zuciyata tana sonshi hakan kawai zakuyi min ingane cewa kuna k'aunata.
Da mamaki take kallon d'iyartata da soyayya ta gama rufe mata idanu cikin sanyin jiki tace Nasiba kinsan dai duk duniyar nan babu wanda yakaimu

59 / 74