Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Fansar RAI Complete 1&2 Complete Hausa Novel by SIS Nerja'art

Author :  SIS NERJA'ART Category :  African Stories & Novels

Chapter   63 / 74

186K to 189K   out of 220.3K words

wad'annan 'barayin sukaci.

Su Alhaji Mansur duk'awa sukayi k'asa suna kuka suna cewa dan Allah Alk'ali ataimaka mana wallahi hukuncin nan ya yi mana tsauri ataimaka a safsafta mana tunda mun amsa laifinmu sannan kud'in da suka rage hannunmu basu kai wanda muka ci mata ba.

Girgiza kai Alk'ali yayi yace wannan ne kuma bazai yuwu ba dole ayi maku hukunci daidai da na kowa, kubar ma ta wannan sai kun biyata kud'in da kukaja aka rufeta tsawon shekara guda batare da hak'k'inta ba.


Mutanen da ke zaune cikin kotun salati suka farayi suna Allah wadai da halin su Alhaji Mansur.



Jawahir da take tsaye tun d'azu inba hawaye ba babu abinda take, hannu tad'aga tafara yi ma Allah godiya sai kuma chan cikin kuka tace tunda dai har gaskiya ta bayyana na ji dad'i bana buk'atar komai daga wajensu subar kud'in na yafe kawai dai akashesu su ma shine zan fi jin dad'i.

Alk'ali yace ba maganar yafewa a cikin hukuncin da kotu tazartas ya zama dole subiya wad'annan kud'in, kallon police yayi yace atafi da su subiya kud'in ga list nan na kud'inta da sukaci idan kud'ad'ensu basu isaba kusiyar da duk wata k'addara da suka mallaka.
Su kuma wad'annan (yanuna wad'anda suka sace Faruf yace) atafi da su gidan yari zasuyi bauta tsawon shekara guda sannan asakesu, yana fad'in haka yabuga table d'in gabanshi.


Nan take aka saka ma su Alhaji Sufyan da Alhaji Mansur ankwa aka fita da su.

Nasiba da take tsaye wajen motarta ita da mahaifiyarta suna kuka nan suka nufi wajen da mahaifin nata yake kafin su isa 'yan jarida har sun rufeshi sun fara mashi tambayoyi a matsayinshi na d'an siyasa, kutsawa sukayi suka isa wajen, yana ganinsu yayi saurin sadda kanshi k'asa......






_Sis Nerja'art✍🏻_[7/24, 11:21 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Ward Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 21*

Nasiba cikin sheshek'ar kuka tace Daddy kalli abun kunyar da kajawo mana yanzu hakan da kayi daidai ne? Kaduba kaga halin da kajefa kanka da mu a ciki a idanun duniya, meyasa kabi son zuciya ka aikata hakan? Ba ka tunanin yadda rayuwarmu zata kasance, taya kake tunanin laifin nan da ka aikata zai goge a idanun mutane? Ya kakeso muyi da rashin ka? Meyasa haka Daddy, meyasa?,,, kukan da yaci k'arfinta ne yasa tayi saurin juyawa, har lokacin kan Alhaji Sufyan yana sadde a k'asa ji yake kamar a mafarki abin yafaru hawaye ne suka fara fita daga idanunshi, muryar matarshi yaji cikin muryar kuka tana cewa Alhaji ban ta'ba tunanin haka daga garekaba wallahi ka ban kunya ka zubar mana mutunci da k'ima daga ni har 'ya'yanka tirr da wannan halin naka, daman Nasiba ta fad'a min akwai abinda yake faruwa a kotu muzo mugane ma idanunmu ashe daman abinda zamuzo mugani kenan? Meyasa haka Alhaji!,, Nasiba ce tajuyo cikin sauri tarungume mahaifiyartata sai a lokacin yad'ago kai yakalleta.

Police tisashi sukayi a gaba aka wuce da shi dan dama tuni antafi da Alhaji Mansur mota, 'yan jaridar da suke ta mashi tambayoyi bai samu ya amsa ma kowaba saboda halin nadama da yashiga.
Suna jin tashin motar nan su Nasiba suka k'ara sautin kukan da suke dan sunsan tabbas a yanzu ya yi masu nisa daga rayuwarsu.



Ana gama shari'ar Barr MB ne farkon wanda yafara mik'ewa yaba Barr Faruk hannu suka gaisa sannan yatayashi murna, Barr Junaid ko dasauri yazo yarungume abokin nashi yana cewa Faruk ka dawo, nagode ma Allah da mutanen nan basu samu damar cutar da kai ba, muna ta wahalar nemanka ashe kana hannun azzaluman chan.
Murmushi Faruk yayi yace Junaid kaidai ko,
Sai a lokacin yajuya yakalli inda jawahir take tsaye tana kuka har ya taka zai tafi sai ji yayi anrungumoshi tare da fashewa da kuka, dubawar da zaiyi sai ganin mahaifiyarshi yayi cikin sauri yarungumeta yace Mom d'ina.
Cikin kuka tace nagode ma Allah da yamaido man kai Faruk wallahi na shiga damuwa sosai akan rashinka ashe zan sake sakaka a cikin idanuna, mutanen chan sun zalunceni ban yafe masuba da suka rabani da kai, ina sonka sosai d'a na.
K'ara rungumeta yayi jikinshi cike da jin tausayin mahaifiyartashi yace nima haka mummyna ina k'aunarki sosai, a yanzu babu wanda zai sake rabamu muna tare.
Dad da ya iso a lokacin dafashi yayi yace d'ana Faruk, k'wallah ce tacika mashi idanu yace ashe zamu sake ganinka nagode ma Allah da basu rabani da kai ba.
'Dan guntun murmushi yayi yace Daddyna nima ina farin cikin sake ganinku.
Farin ciki suka dinga yi sosai a wajen duk wani me k'aunar Barr Faruk saida yazo yatashi murna duk da haka hankalinshi yana wajen jawahir samu yayi yajanye Mom daga jikinshi yace yana zuwa nan yanufi inda take, yana zuwa yabud'e baki zaiyi magana sai tarigashi tace nagode sosai Faruk da namijin k'ok'arin da kayi akaina tabbas ka cika mutumin kirki ka taimakeni a daidai lokacin da nake buk'atar taimako ka wankeni daga zargi a idanun jama'a, koda akaina ka fuskanci matsalar rayuwa ammah hakan bai sa kabarni ba nagode, nagode, nagode sosai Faruk.
Cike da jin tausayinta yace jawahir kidaina cewa haka domin wannan ba komai bane kin cancanci hakan ko ma ba keba hak'k'inane intaimaka ma duk wani wanda yake buk'atar taimako irin wannan hatta rayuwata zan iya bayarwa akan aikina.
Da mamaki take kallonshi cikin ranta tana jinjina ma k'wazo irin na Faruk da son taimakonshi, wasu sabbin hawayen ne suka gangaro mata tace ina ma ace Ammina tana raye taga irin wannan ranar, ina ma ace zanga irin farin cikin da zata shiga, ina ma ace Yaya Umar yana raye,,,, kukan da yaci k'arfinta ne yasa tayi saurin juya mashi baya.
Faruk har ya bud'e baki zaiyi magana sai ganin Nasiba yayi gabanshi tsaye tana kuka, idanu yazuba mata ganin yadda take kuka bilhak'k'i, cikin sheshek'ar kuka tace Faruk dan Allah kayi hak'uri da abinda yafaru tabbas na yi kuskure da nakasa fahimtarka, mahaifina baiyi mana adalciba dan duk shine yajefamu a cikin wannan halin nayi nadamar kasancewarshi a matsayin uba agareni dan bai cancanci hakan ba, Allah wadai da mahaifi me hali irin nashi.
Tarar numfashinta yayi yace a'a Nasiba kidaina cewa haka ko ba komai shi ubane.
K'ok'arin rage sautin kukanta tayi sannan tace tabbas shi ubane ammah ba irin uban da yadace ayi alfahari da shi ba domin ya 'bata mana suna a idanun duniya wallahi na yi nadamar rayuwata ina ma ace inmutu inhuta da wannan rayuwar Faruk ban ta'ba tunanin haka daga mahaifina ba ashe daman shine yasaceka, hannuwanta tahad'e waje guda tace dan Allah Faruk kar kakamani da laifin da bani na aikata ba, tabbas nayi maka mummunan fahimta a lokacin da kaso kafahimtar da ni komai saidai duk hakan daman ubangiji ya k'addara hakan zai faru dan Allah kayafe min ba dan halina ba.
Wani irin tausayinta ne yaji ya d'arsu a cikin ranshi yace Nasiba wallahi bakiyi min komai ba inma kinyi na yafe maki dan baki cancanci inrik'eki acikin raina akan wani laifi da ba nakiba.

Fashewa tayi da kuka tace nagode sosai Faruk nagode, sai a lokacin tajuya inda jawahir take tsaye ta juya baya matsawa tayi tatsaya gabanta tace na tabbata kowanene akayi ma irin abinda akayi maki sai ya ji ba dad'i a ranshi dan an zalunceki anci amanarki dan Allah ina neman afuwarki akan abinda mahaifina ya aikata maki.
'Dago kai jawahir tayi tana kallonta.
Ganin haka yasa Nasiba tace ba wai ina neman afuwa bane akan asaki mahaifina saidai ina neman afuwa akan kasancewata 'yarshi mukaci da hak'k'inki dan Allah kiyafe min.
'Daga mata kai kawai Jawahir tayi batare da tayi magana ba.

Nasiba kallon Faruk tayi tace dan Allah Faruk kar wannan abun da yafaru yasa kabarni dan Allah kar kakalleni da halin mahaifina inaso kacigaba da kasancewa tare da ni.

Juyawa yayi yakalli iyayenshi da aketa tayawa murnar dawowar d'ansu sannan yace Nasiba yanzu ba lokacin wannan maganar bace, kallon jawahir yayi yace muje kugaisa da iyayena.

Bata musaba tajuyo tabi bayanshi suka tafi suka bar Nasiba nan tsaye tana kuka, daidai lokacin mahaifiyarta tazo nan tafad'a jikinta tana cewa Mummy na rasa Faruk ya daina sona, meyasa?
Girgiza kai Hajiya Maijidda tayi tace a'a Nasiba kizo muje gida kawai.
Haka tabi mahaifiyartata suka tafi.

Faruk nuna ma iyayenshi Jawahir yayi nan suka gaisa suka yi mata jaje sannan suka tayata murnar ku'butar da tayi daga gidan kaso.


Mom dai tana manne da d'an nata chan tace Faruk wai ya akayi kaku'buta daga hannun wad'anchan azzaluman?
Murmushi yayi yace Mom muje gida sai insanar da ku komai.
Dad ne yace Alhamdulillah kinga zuwan da mukayi kotu ya yi amfani daman raina ya bani zamu ga Faruk saisa nace maki muzo, yanzu kuzo muje gidan.



Gabad'ayansu suka d'unguma suka nufi gida dan da fari har Jawahir ta k'i binsu ta ce ita dai subarta a nan zata tafi gidansu saidai Dad yace shin mu ba iyayenki bane Jawahir? Ko bakomai nima matsayin uba nake a wajenki saboda matsayin mahaifinki a wajena.
Da mamaki suke kallonshi tace daman ka san Abbu?
Murmushi yayi yace sosai ma muje gida zan sanar da ke inda nasanshi, bata musaba sannan tabisu suka nufi gidansu Faruk gabad'ayansu har da su Barr Nas da Barr Junaid.


Suna zuwa Mom d'akinta taja Jawahir tahad'a mata ruwan wanka tayi bayan ta fito tad'akko mata wata jallabiya tabata tasaka saida sukayi sallah sannan suka fito parlor Jawahir dai ta kasa sakin jiki dan ita rayuwarta ba mai saurin yadda da mutane bace tunda tataso haka take, suna nan zaune su Dad da su Faruk suka fito kusan lokaci guda bayan sun dawo daga masallaci, koda suka zauna Dad cewa yayi afara kawo abinci aci kafin afara wata magana dan haka Mom taje tasanar da masu aiki, nan da nan aka fara shigo masu da abinci iri iri kowa yafara serving d'in kanshi ammah banda jawahir ganin ta k'i sakin jiki yasa mom ta d'ibi abincin tajata sukaje d'akinta tace Jawahir kisaki jikinki nan ma gidane kiyi abinda kikeso mu bamuda matsala kinji.
Murmushi tayi tace nagode Mom.
Duk yadda Mom taso taci abincin k'i tayi dak'yar tad'anci kad'an tabarshi dan haka tak'yaleta.

Bayan kowa ya kimtsa cikinshi suka had'u a parlor.

Dad ne yafara cewa toh Alhamdllh a yanzu sai kasanar da mu yadda akayi kaku'buta.


Faruk murmushi yayi sannan yakwashe yadda akayi aka saceshi yafad'a masu da yadda yadinga shan wahala a wajensu har zuwa shigowar d'an uwan nasu da takeaway yakawo ma sauran.
Su duka idanu suka zuba mashi suna kallonshi cike da mamaki dan Mom ko hawaye tafara ganin haka yasa Faruk yacigaba da cewa "duk a tunanina wannan me dariyar ya tafi jin shurun da yayi sai chan naga bayyanar wata tsohuwa a gabana dudduk'e tafiyarta dakyar dakyar " kallon jawahir yayi yace ke dai na san kin gane ko wacece, d'aga kai tayi alamun Eh, cigaba yayi da cewa tana bayyana kallona tatsaya yi sai chan tace Barrister daman ban fad'a maka ba nice kad'ai nake da ikon taimaka ma Jawahir?
Wani irin kallo nayi mata cikin nuna rashin tsoro nace taimako na ubangiji ne shikad'ai yake iya taimaka ma bawansa.

Bushewa tayi da dariya tace bazanyi maka jayayya ba saidai ina farin ciki guda a yau Jawahir ta yi nadamar da dadad'ewa nake jira tayita ammah saboda taurin kanta batayiba a yanzun ma abun bak'in cikin ta yi ne ba dan komai ba sai dan tana neman intaimaka maka.
Kallonta faruk yadinga yi cikin nuna rashin fahimtar maganarta.
'Dan dogaro sandarta tayi tamatso kusa da shi sannan tacigaba da cewa a lokacin da za'a fito da su akaisu kotu hankalinta a tashe yake ganin haka yasa nabayyana a gareta natambayeta ko tana buk'atar taimakona?
Girgiza kai tayi tace bana buk'atar taimakonki.
Bushewa da dariya tsohuwar tayi tace cikin ke da Faruk dole sai wani ya riga wani shek'awa lahira.
A rikice jawahir tace ban fahimta ba me zai faru da faruk d'in?
Sake bushewa tayi da dariya saida tayi me isarta sannan tace zasu kasheshi a bayan an yanke maki hukunci a kotu saboda kar susakeshi yatona masu asiri.
Fashewa Jawahir tayi da kuka cikin sauri taduk'a k'asa tace Ammi na rok'eki dan Allah kitaimakeshi kar kibari sukasheshi bai cancanci hakan ba.
Girgiza kai tayi tace bakida ikon neman taimakona batare da yin nadama ba.
'Dago kai tayi fuska sha'be sha'be da hawaye tace indai har akan Faruk ne na amince saida taruntse idanunta cike da takaici sannan tace na yi nadamar kalmar da nafad'a maki kiyi hak'uri insha Allahu bazan sakeba, ina sonki Ammina....dariyar da taji ana kyalkyalawane yasa tayi saurin bud'e idanunta dan gabad'aya d'akin yake amsaba dubawa tayi taga babu Ammin tata saidai muryar dariyar taji tana fita, tana nan duk'e a haka akazo aka fita da su aka tafi da su kotu.
Tana kawowa nan a bayanin nata tanuna inda Faruk yake zaune da sandarta sai gani yayi d'aurin da akayi mashi ya kwance, cikin muryarta me ban tsoro tace zaka iya fita ga k'ofa chan a bud'e nan da minti takwas zata iya rufe kanta, jin haka yasa Faruk yayi saurin mik'ewa duk sai yajishi wani iri dakyar yafara takawa dan a lokacin matar har ta 'bace, bin gidan yadinga yi da kallo bai san inda yakeba da karambani yagano k'ofa yana fita k'ofar tana maida kanta tadatse tsayawa yayi yak'are ma gidan kallo saida yagane anguwar sannan yasamu abun hawa yahau yanufi gidan Barr Nas, ya yi sa'a ya sameshi a gida nan yayi ta murnar dawowarshi wanka yayi yashirya cikin sauri, sannan yace ma Nasir yad'auko mashi ajiyar da yakawo mashi ranar da za'a kamashi dan dama jikinshi ne yadinga bashi kamar akwai abinda zai iya faruwa da shi wannan dalilin ne yasa yad'auki dukkan shedun da yatara yakai ma Barr Nas ya ajiye mashi wajenshi hatta wayarshi da yafi amfani da ita saida yakashe yabashi dan ya san a cikinta ya ajiye abubuwa dadama masu muhimmanci,daga nan suka fito cikin sauri suka nufi kotu dan a lokacin sun makara dan sunsan dole cikin biyu ayi d'aya ko angama shari'ar Jawahir ko kuma ana cikin yi....yana kawowa nan a labarin yace wannan shine abinda yafaru da ni.

Hankalinsu gabad'aya saida yatashi sosai Dad yace tabbas Alhaji Sufyan ya kasance maha'inci ban ta'ba tunanin haka daga gareshiba ace da sa hannunshi aka sace min d'a duk kusancin da ke tsakaninmu ina mashi kallon abokina na k'warai ashe ba haka ba.


Jawahir sai a lokacin tad'ago takalleshi tace ya akayi kasamo Ummah katafo da ita?
Murmushi yayi yace lokacin da naje asibitin naga halin da take ciki nan nanemi taimakon likitocin suka taimaka suka ban ita nacanza mata asibiti inda zata fi samun kulawa dan asibitin da su Alhaji Mansur suka kaita wata k'aramar asibiti ce wadda basuda wadatattun kayan aiki kuma sunyi hakane dan kawai suna so tamutu itama, toh cikin ikon Allah ina maidata chan suka dinga bata kulawa sosai har tafara samun sauk'i, dan tana iya motsa 'bare d'aya na jikinta saisa ma nace atafo da ita tunda tana magana.


Shi kuma megadinku buzu wannan aikinki ne dan kece kika samar mana taimako Amminki tasanar da mu inda yake.

Jinjina kai su Dad suka dinga yi mamaki duk ya cikasu.
Barr Junaid yace lallai sharrin su Alhaji Mansur ya fi tunanin duk wani me tunani ashe duk wannan k'ulla k'ullan su sukayi shi sukaja aka kama baiwar Allahr nan.

Dad girgiza kai yayi yace wasu mutanen macen zuciya garesu babu abinda sukasa gaba sai son kansu, kallon jawahir yayi yace tabbas na san mahaifinki dan abokin kasuwancina ne a lokacin da yake raye kamfanina da nashi kusan tare suke tafiya dan ma baza'a had'a ba nashi kamfanin ya fi nawa d'aukaka saboda wasu kayan ya fini saidai shi ba mutum bane me bak'in ciki yana son cigaban mutane nan yasa muka had'a hannu tsakanin kamfanina da nashi muna shigo da kaya tare wani lokacin idan kamfaninshi yana buk'atar rancen kud'i a nawa kamfanin yake zuwa yana ranta nima haka akan wannan ne yasa muka k'ulla abota sosai akan kasuwancinmu dan kowa yana son cigaban d'an uwanshi bamufi wata takwas a haka ba nanemi rancen wasu kud'i saboda wasu kayan aikin injin da nakeso inje Dubai insiyo yad'auki kud'in yabani, koda naje Dubai saida nayi kusan wata ukku sannan nasamu yadda nakeso naturo da kayan ni ban dawoba a wata na biyar ne naturo mashi da kud'inshi daga chan saidai 1 million da tarage ban bashiba, ak'alla saida nayi wata goma sannan nadawo k'asar nan bayan na dawo ne nasamu labarin rasuwarshi nan hankalina yatashi sosai haka nad'auko million d'aya d'in nan naje gidanshi nayi sallama nasa aka kira man matarshi koda tafito nayi mata gaisuwa sannan nabata cheque d'in kud'in, tun bayan rasuwarshi na so mucigaba da kasuwanci tsakanin kamfanina da nashi ammah d'an uwanshi yak'i dan haka nabarshi lokaci guda kamfanin yadaina kawo kud'i yadda yakamata nawa yazo yafi shahara, a haka nak'ara nema muhad'a hannu da Alhaji Mu'azu mumaido ma kamfanin tattalin arzik'inshi ammah yak'i dan gani yake kamar wani cutarshi nakeson yi wannan dalilin ne yasa nafita harkar kamfanin.


Jawahir fashewa tayi da kuka tace tabbas kaine Alhaji Sanin da yazo gida yakawo ma Ammina cheque akan kud'in ne aka nemi a salwantar da rayuwarta

Su duka kallonta suke cike da mamaki Barr Nas yace kamar ya?
Kwashe komai tayi tasanar da su akan mutuwar Amminta nan duk jikinsu yayi sanyi sukayi ma iyayen nata addu'a.

Mom ce tarungumota jikinta tana lallashinta dakyar aka samu tayi shuru sannan Dad yace Jawahir kikwantar da hankalinki mu zamu zauna da ke zamu kula da ke duk abinda kikeso zamuyi maki kid'aukemu a matsayin iyayenki.
'Dago kai tayi takalleshi tayi murmushi tace nagode sosai Dad da wannan karamcin da kukayi min saidai ina so

63 / 74