Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Fansar RAI Complete 1&2 Complete Hausa Novel by SIS Nerja'art

Author :  SIS NERJA'ART Category :  African Stories & Novels

Chapter   53 / 74

156K to 159K   out of 220.3K words

motarka ka fita daga gidan marigayi Alhaji Tanimu Nepa ni kuma lokacin nashiga gidan zanyi masu gaisuwa, shine nakeso inji ya kake da shi daman ka sanshi?

Allah Sarki ai Alhaji Tanimu Mahaifin abokina ne Nazir tare mukayi secondary school da shi muna mutunci sosai da shi, shi naje ma gaisuwa dan kusan tun ranar da akayi rasuwar kullum sai na je.

Wani irin sanyi Faruk yaji a ranshi har saida farin ciki yabayyana a fuskarshi Alhankili yafurta Alhamdulillah.
Da mamaki Barr Nas yake kallonshi yace lafiya Barrister me yafaru naga kana fara'a?

Lafiya lau Nasir na ji dad'i sosai da jin bayananka a yanzu ina da k'warin gwiwar samun abinda nakeso watau wani case ne me zafi mukeyi shine nake son kataimaka min a ciki kayi min jagorar zuwa gidanshi.

Cike da mamaki yace case kuma? Wane irin case ne haka? Ko akan kisan da ake zargin anyi mashi dan naji anata jitajitar kasheshi akayi saidai anrasa wanda yayi kisan dan ajiya ma aka sako driver d'inshi an wankeshi daga zargin da ake mashi, saidai har yau anrasa wanda yayi kisan ana tadai bincike ankasa samun k'wak'k'warar shaida za'a iya kama wanda yayi laifin.

Tsayawa yayi yana saurarenshi har yakai aya nan yarasa me zaice tunani yafara yi yasanar da shi komai akan case d'in jawahir ko kuma yayi shuru abunshi,,
Muryarshi yace yaji ya ce ya dai Barrister ka yi shuru lafiya dai ko?

Girgiza kai yayi yace babu komai saidai kawai.....shuru yayi batare da ya k'arasa fad'in kalmar da take bakinshi ba.

Ganin haka ya Barr Nas yatashi yakoma kusa da Barr Faruk bisa 2 seater d'in da yake zaune sannan yace Faruk kayi min bayanin koma menene zan fahimceka kuma zan taimaka maka saboda ka cancanci haka.

Har cikin ranshi ya ji dad'in bayanin abokin nashi sosai kuma ya san tunda har yafurta toh zai taimaka mashi dan tun a makaranta baya da aboki kamarshi da Barr Junaid dan duk tare sukayi karatu har gama makarantar su sannan wajen aiki d'aya saidai Barr Junaid ne kawai a lokacin baiyi zurfin karatu kamar nasuba dan shi daga HND yatsaya su kuma har masters sunyi saisa sukafi shak'uwa da Barr Nasir sai daga baya ne dayakoma a kotun da Barr Junaid yake aikine abotarsu tak'ara k'arfi,,, jijjigashi Barr Nas yayi yace wai lafiyarka Faruk sai wasu tunane tunane kakeyi ya kamata kanutsu kafad'a min koma menene.

Shikenan Nasir zan sanar da kai komai yanzu nasan zaka taimaka min, bayan na baro court d'inku anmaidoni a nan HIGH COURT shine natarar ana wani case wanda bayan rasuwar lauyan da yake jagorantar case d'in yake kare wadda ake k'ara shine ni kuma na amshi case d'in yadawo hannu na dan kare wadda ake k'arar a lokacin da na lura tana buk'atar taimako ana nema atauye mata hak'k'i mutane da dama sun nemi su fahimtar da ni had'arin da yake cikin case d'in ammah ni duk wannan bai dameniba burina d'aya shine inwanke wadda ake k'arar a idanun duniya........
Kwashe komai yayi akan case d'in Jawahir yafad'a mashi saidai ya 'boye mashi gaskiya a game da Fatalwar da ke tare da jawahir har tsorata shi da ake babu abinda yafad'a mashi.

Hankalin Barr Nas ya tashi sosai da yaji labarin saidai bai katseshi ba har saida yagama fad'a mashi komai sannan yace tabbas naji labarin case d'innan ko ba ita bace Jawahir Muhammad? wadda tayi kisa har takashe lauyoyinta saidai na ji labarin ya d'an sha banban da wanda kabani ammah tabbas ina tunanin itace.

Eh itace saidai abinda aka fad'a ba gaskiya bane Nasir ni kaina ina neman hujjojin da zan tabbatar ma mutane da haka saisa a yanzu haka nakeso kayi min jagora zuwa gidan Alhaji Tanimu dan akwai abinda nakeso ind'auko.

Tun kan yarufe baki cikin sauri Barr Nasir yamik'e tsaye yace ka san abinda kake fad'a kuwa Barrister?
Taya kake tunanin zamu iya shiga gidan Alhaji Tanimu har wai kad'auko wani abu a d'akinshi batare da sanin kowa ba, ka san dai za'a iya kamamu idan har kuma hakan yafaru har kotu za'a banka mu sannan kisan da ake cewa anyi mashi mu za'a ce mun kasheshi gaskiya hakan bazai yuwuba kama daina wannan tunanin.

Shima mik'ewa yayi cikin sanyin jiki yace Nasir kar kadamu insha Allahu babu abinda zai faru zanyi k'ok'ari wajen ganin na yi komai batare da angane mu ba.

Cikin karaya Barr Nasir yace Faruk anya hakan zai yuwu da dai ka hak'ura kawai.

"Nasir kadaina cewa haka na yi maka alk'awari babu abinda zai sameka koma menene yafaru bazan ta'ba bari asakaka cikiba laifin gabad'aya nawa ne wannan alk'awarine nayi maka.

Ganin yadda yanace yasa Nasir ya amince sutafi, nan suka zauna yana cigaba da tayashi aikin da yake a nan sukayi azuhur yaba megadin shi kud'i yayo masu takeaway suka ci dan matarshi sai marece zata dawo.


Bayan sunyi sallar la'asar ne suka kama hanyar gidan Alhaji Tanimu inda gabad'ayansu zuciyoyinsu babu dad'i jikinsu ya yi sanyi sosai saboda basusan abinda zasu tarar ba idan sukaje, Barr Nas yake driving inda Barr Faruk yake zaune gefenshi yana ta sak'e-sak'e cikin ranshi har suka isa gidan suna zuwa aka hangame masu tankamemen gate d'in gidan suka cinna kan motar su a ciki,
Motocine sosai a parking space dan haka suka samu waje su ma suka ajiye tasu motar.

Barr Nas juyowa yayi yakalli Faruk yace Barrister wallahi ina jin tsoro sosai taya kake ganin shiga d'akin Alhaji tanimu zai yi mana sauk'i bayan akwai mutane sosai a cikin gidan.

Ajiyar zuciya yasafke yace nima ina tunanin haka Nasir saidai banda yadda zanyi tunda tun farko ni nayi ma yarinyar alk'awari zan taimaka mata kuma dole sai na samo wayar itace zata taimaka min nan da kwana goma inku'butar da jawahir dan da kwanaki goman nan sun shud'e na tabba za'a yanke mata hukuncin kisa dan wannan zaman shine zama na k'arshe da za'ayi, mushiga kawai in gwada sa'a ta.

Ammah ta ya kake tunanin zamu iya shiga cikin gidanshi har d'akin shi?

"Kar kadamu da wannan ni zan shiga ba kai ba bazan sakaka cikiba Nasir koma menene zai faru saidai yafaru da ni kad'ai yanzu fito mushiga ciki muyi masu gaisuwa dan inga yanayin mutanen da suke ciki.



Ajere suka tafi suna tsayawa suna gaisawa da jama'ar da suke zaune saman tabarma har suka shiga setting room d'in gidan inda dangin mamacin suke zaune suna amsar gaisuwa bayan sun gaisa sunyi masu gaisuwa Nasir yaduk'o da kanshi saitin fuskar Faruk ahankali yace banga Nazir ba ina tunani baya nan ammah bari intambaya, matsawa yayi kusa da k'anen Nazir da yake zaune chan k'arshen bango yatambayeshi inda Nazir yake yace mashi yana cikin gida dan haka suka tashi suka shiga koda matane a ciki ammah ahaka sukayi ta ratsawa suna gaishesu har suka shiga babban parlor inda suka samu matan mamacin zaune da mutanensu, gaishesu sukayi sannan Nasir yatambayi mahaifiyar Nazir inda Nazir yake tace yana chan part d'in Abbansu ya yi wasu bak'i kuje chan kusameshi kuce na ce ina jiranshi yakawo min keys d'in part d'in.
Barr Faruk kallon Nasir Yayi yai murmushi irin na da alama zamuyi nasara, girgiza kai Nasir yayi alamun a'a sannan suka mik'e suka nufi part d'in da yake mallakin megidan.

Tun da suka tunkari hanyar part d'in suka fara jiyo hayani alamun ana labari haka suka isa suna shiga suka tarar da su tsaisaye alamun tafiya zasuyi Nazir yana ganinsu yace A'a Barrister sannunku da zuwa.
Hannu suka mik'a masu duk aka gaisa sannan suka k'ara yi mashi gaisuwa.

Mutane ukkun nan da suke tsaye ne sukace mu zamu wuce Allah yajik'anshi yace toh nagode muje inrakaku, kallon su Barr Faruk yayi yace dan Allah kuzauna ina zuwa bari indawo.

abu daman ga wad'anda suke nema dan haka suka zauna haka yafita da abokanshi dan yarakasu.

Barr Faruk kallon Nas yayi cikin sanyin jiki yace ban san ta inda zan faraba barrister ammah bari infara ta'ba bedroom d'in inji idan bud'e yake, Barr Nas da yanuna alamun tsorata yace a'a Barrister kar fa ashigo aganka.

Batare da ya ce komai ba yamik'e cikin sauri yanufi hanyar da zata sadaka da bedroom d'in yana zuwa yamurd'a k'ofar yaji datse take gam nan fa duk yaji ba dad'i yadawo yazauna tare da dafe kai yace hakan bazai ta'ba yuwuwa ba nasan bazan yi nasara ba Nasir.

Ajiyar zuciya Nas yasafke yace kakwantar da hankalinka Faruk ko ma ba ta wannan hanyar ba insha Allahu zaka samu k'wak'warar shedar da zaka bayar.

Yana bud'e baki zaiyi magana suka jiyo taku alamun an nufo d'akin dan haka sukayi shuru sai ga Nazir ya shigo fuskarshi d'auke da murmushi yace kuyi hak'uri na barku ku kad'ai, wallahi abokaina ne da mukayi karatu da su a London

Sukace Allah sarki a'a babu komai, zama yayi yana kallon Barr Faruk yace kaima Barrister d'inne irin Nas ko?.
Murmushi yayi yace a'a shi dai ne lauya.
"Ayyah Allah sarki aini tun farko mancewa nayi da abokina babban lauya ne da shi zan saka acikin case d'in kisan da akayi ma mahaifina dan ak'wato mana hak'k'inmu.

Barr Faruk kallon Barr Nas yayi da shima yake kallonshi su dukansu sukayi shuru aka rasa wanda zaiyi magana daidai lokacin akayi sallama aka shigo su dukansu suka juya suka kalli k'ofa tare da amsawa wata dattijuwa ce tashigo nan duk suka gaisheta bayan ta amsa ne tace Nazir ina key d'in bedroom d'in Abbanku zamu d'auko sauran lemuna a ciki.

Aunty Amina kinsan dai anhana bud'ewa nima kaina dak'yar nasamu Ummah tabani key d'in nashigo parlor.

Harararshi tayi tace kai ni dallah bani ind'auko abinda zan d'auko sai inmaido maka kayi ta tseguminka saikace wata uwa abu zan d'auka a ciki.

Ganin yadda tafara d'aga murya tana fad'a yasa yaciro keys d'in acikin aljihu yamik'a mata amsawa tayi taje tabud'e tashiga.

Barr Faruk kallon kallo suka fara da Barr Nas sai kuma suka maida hankalinsu ga k'ofar bedroom d'in da tabud'e, Faruk ji yake kamar yayi tsalle yashige saidai hakan bazai ta'ba yuwuwa suna kallo tagama d'auko lemunan tarufe d'akin tamik'o ma Nazir key d'in, sannan tafara jidar lemunan tana fita da su.
Nazir a gefen da yake zaune ya d'age wani throw pillow ya ajiye Keys d'in a wajen yace muma ai yanzu zamu fita tun kan azo afara yi mana surutu tace da dai ya fi maku.
Faruk yana kallo nan ya ida sarewa yatabbatar bazai samu yadda yake so ba.

Bayan ta fita nan Barr Nas da Nazir suka fara hira inda shi kuma Barr Faruk yayi shuru abin duniya duk ya isheshi, Nazir bai damu da shurun da yayi ba dan yana ganin yanayinshi yagane shi d'in ba mutum bane me son hayaniya sosai ba, suna cikin hirar nan wayar Nazir tafara ringing d'aukowa yayi yai picking tare da yin sallama, basuji abinda akace mashi ba saidai ji sukayi yana cewa toh shikenan Kawu ganinan zuwa ai dama ina cikin gidan bari infito, kashe wayar yayi yakallesu yace bari ind'anje indawo wasu abokan Abba sukazo mana gaisuwa daga Kaduna, ajiyar zuciya Barr Faruk yasafke kafin Nas yayi magana shi yayi saurin cewa Allah Sarki toh shikenan babu damuwa sai ka dawo.
Nas dai murmushi yayi dan ya san dalilin Faruk na cewa haka.

Mik'ewa Nazir yayi yafita lokacin da aka sake kiranshi waya, yana barin d'akin cikin sauri Faruk yamik'e yanufi wajen kujerar da yazauna yana zuwa yahankad'e pillow yad'auko keys d'in wani irin farin ciki yaji a ranshi yajuya yakalli Nas da yakeyi mashi kallon mamaki ganin babu wani alamun tsoro a tare da shi har ya iya d'aukar key d'in, murmushi yasakar mashi tare da cewa ina zuwa bari inyi sauri inje ind'auko bazan 'bata lokaci ba.
Cikin sanyin jiki yace a'a Faruk ina jin tsoro.

Batare da ya tanka shi ba yawuce yanufi hanyar Bedroom d'in yana zuwa yasa key d'in da yaga Nazir ya nuna ma matar nan, yana murzawa sai ga k'ofa ta bud'e juyowa yayi yakalli Barr Nas da yagama tsorata sannan yazare key d'in yashiga cikin bedroom d'in yamaida k'ofa yarufe, tsaye yayi a bakin k'ofar yana bin d'akin da kallo komai na ciki ya ji sosai za'a iya cewa aljannar duniya kenan, ta'be baki Faruk yayi sannan cikin sauri yanufi wajen wardrobe d'in yana zuwa baiyi wata wata ba yabud'e yafara bincike cikin sauri dubawa yadinga yi ammah baiji wayar ba saida yaduba kusan sau ukku baiga komai ba nan hankalinshi yafara tashi yace shikenan and'auketa daga wajen toh ammah tana ina? Ko dai Jawahir batasan inda takeba daman haka nan tace min tana cikin wardrobe d'inshi?.
Tsaye yayi wajen, jikinshi duk ya yi sanyi sosai chan kuma yatuna da irin matsalar da zai shiga dan haka yajuyo cikin sauri zai fito yabar d'akin.


Nas da yake zaune tsoro duk ya gama cikashi Allah Allah kawai yake Faruk yafito kafin dawowar Nazir yana cikin haka kawai sai jiyo muryar Nazir yayi ya tunkaro d'akin yana waya yana cewa shikenan Ummah ganinan yamzu zan kawo maki keys d'in daman sun tafi yanzu ina tare da su Nas ne kuma shi dai d'an gidane babu damuwa sai mufito mukoma setting room.....









_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:13 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Award Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 12*

Barr Nas da yake zaune tsoro duk ya gama cikashi Allah Allah kawai yake Faruk yafito kafin dawowar Nazir yana cikin haka kawai sai jiyo muryar Nazir yayi ya tunkaro d'akin yana waya yana cewa shikenan Ummah ganinan yanzu zan kawo maki keys d'in daman sun tafi yanzu ina tare da su Nas ne kuma shi dai d'an gidane babu damuwa sai mukoma setting room.


Wayyoooo kar kuso kuga Nas a lokacin zufa ce tafara kwarara daga jikinshi yana jin kamar yanutse cikin kujera, tsoro da fargaba duk suka d'arsu a cikin zuciyarshi, Nazir na gama wayar ya ida shigowa cikin d'akin yana shigowa yakalleshi yace ya naga kana zufa? Sorry bari ak'ara Ac d'in daman d'azu muka rageta.
Shi dai da idanu yabishi kawai cikin ranshi yana cewa shikenan Faruk ya ja min, muryar Nazir yajiyo yana cewa ina abokin naka ba dai ya tafi ba?

Dabarbarcewa yayi yarasa abinda zaice sai chan cikin rawan murya yace am ya je waje zai amsa waya ne.
Toh shikenan bari mujira yadawo sai mukoma chan setting room ko kuma mutafi muhad'e da shi dan Ummah ta fara fad'a wai inkawo mata key d'in d'akin Abba saboda ba'a so ana shigowa yanzu za'a fara surutu.

'Yan cikin Nas saida suka kad'a yarasa abinda zaice ma Nazir sai chan cikin dauriya yace Nazir ko zaka taimaka min da ruwa insha kafin yadawo kaga kar mufita yadawo kuma bamu nan baisan inda muka nufa ba.
Mik'ewa Nazir yayi yace hakane kuma bari inje inkawo maka ruwan dan na nan ciki basuda sanyi inyaso in nagamu da shi sai infad'a mashi.
'Daga kai kawai yayi dan baya ji a yanzu zai iya magana saboda tsananin tsoron da yashiga juyawa Nazir yayi yafita dan samo ma abokin nashi ruwa.

Yana fita Nas yana son yamik'e ammah yakasa jikinshi ssi rawa yake yana nan zaune sai ga Faruk ya fito yana fitowa cikin sauri yarufe d'alkin, jin motsin tafiya yasa yawurgo ma Nas key d'in yayi saurin juyawa tare da kanga wayarshi a kunne kamar yana waya.
Nas tura key d'in yayi a k'ark'ashin throw pillow d'in da Nazir ya ajiye key d'in daidai lokacin Nazir yashigo yana cewa na sa yanzu za'a kawo maka.
Ajiyar zuciya Nas yasafke ganin asirinsu bai tonuba.
Nazir kallon Faruk yayi da yajuya yana waya yace ashe ya dawo ai da nafita ban ganshiba.
Murmushi Nas yayi yace Eh kana fita yadawo kuma aka sake kiranshi waya shine yamatsa chan yana yi.

Nazir yace Allah sarki yanzu kuzo mukoma setting room na san sun ragu gashi fitarnan da nayi andameni infito inrufo d'akin.
Murmushi Nas yayi yace haba ba damuwa ai mu ba bak'i bane, daidai lokacin Faruk yajuyo yana murmushi yace bakomai ai yanzu ma zamu tafi dan daga wajen aiki ake min neman gaggawa.

Nazir yace tun yanzu maimakon kubari sai anjima.
Kar kadamu muma munso mubari sai da anjima dan dai kiran gaggawar da akayi min ammah zamu dawo wani lokacin.

'Dauko key d'in Nazir yayi yace toh shikenan sai mufita gabad'aya in mik'a masu key d'in inhuta.

Faruk yana lura da Nas da yake ta yi mashi kallon tuhuma ammah yak'i kulashi ahaka har suka fita.
Saida suka jirashi yafara mik'a key d'in wa Ummanshi sannan suka tafi yarakasu har wajen mota yayi masu godiya suka shiga suka tafi, suna fara tafiya Nas yajuyo yakalleshi yace wai ya dai Faruk sai alama nake ta tambaya kuma ka gane nufina ammah kashareni wallahi hankalina ya tashi sosai Allah ya taimaka guy d'in nan bai gane komai ba.

Murmushi Faruk yayi yace daman ya gane da kai zaka fi kwana ciki tunda abokinka ne.

Au haka ma kace ko?
"Toh me kakeso ince?

Yanzu dai fad'a min shin ka d'auko wayar ko kuwa hakanan kafito baka gantaba?

Murmushi yayi yace Eh toh banga wayar ba.

Kana nufin baka gantaba hakanan kafito?,, Nas yatambayeshi cike da mamaki.

Juyawa yayi yakalli taga sannan yace ina nufin ban gantaba a inda jawahir ta fad'a min saidai na ganta a wani wajen na daban.

Ajiyar zuciya Barr Nas yasafke yace Alhamdulillah na ji dad'in haka gaskiya Barrister kai d'in nadaban ne saisa ko a school nake jinjina maka dan k'walwarka tana ja sosai.

Juyowa Faruk yayi yakalleshi tare da fiddo wayar daga cikin aljihunshi yana murmushi yace tabbas ina farin ciki Nas ko ba komai wayar nan zata taimaka min wajen samun duk wani abu da nakeso, yanzu dai mu wuce gidana kasafkeni dan ko motsta bazan d'auko gidanka ba.

Kallonshi Nas yayi yace ban gane insafkeka ba malam, muje dai ind'auko su

53 / 74