Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Fansar RAI Complete 1&2 Complete Hausa Novel by SIS Nerja'art

Author :  SIS NERJA'ART Category :  African Stories & Novels

Chapter   30 / 74

87K to 90K   out of 220.3K words

aikata na kashe mijinki wannan shine adalcin kawai da zamuyi.


Kuka tacigaba da yi cike da tashin hankali nan aka tafi da ita.


Jawahir wani irin tausayinta taji ganin yadda take kuka saidai me matar itace me laifi babu yadda za'ayi.

Haka me gabatar da k'ara yamik'e yasake bayani akan k'ara ta biyu aka fito aka fara yin shara'a.


Jawahir tana nan tsaye saida akayi ma mutane hud'u inda wasu aka yanke masu hukuncin kisa wasu kuma aka maidasu gidan yari, ita d'in kanta ta san dole cikin biyu za'ayi guda ko kisa ko yanke hukuncin k'arashe rayuwa a gidan kaso, wasu siraran hawaye ne suka gangaro mata cikin zuciyarta tace Barr Faruk rayuwarka kawai nakeji ba wai abinda zai faru da ni ba, ina ma ace Ammi zata taimaka taku'butar da kai.



Ana gama wad'annan shari'o'in megabatar da k'ara yamik'e yace sai shari'ar da takasance ta k'arshe a wannan ranar itace shari'ar Jawahir Muhammad Maikud'i wadda ake zargi da yin kisa na mutane d'aid'aya har mutum bakwai, inda dangin mamatan suka shigar da k'ara,, sannan yaje yamik'a ma alk'ali file d'in,
kotun kacamewa tayi da surutu saida alk'ali yad'an buga tebirinshi sannan akayi tsit,


Duk'awa yayi yafara duba file d'in ya d'auki lokaci yana dubawa sannan yad'ago yace kotu tana buk'atar ganin Jawahir wadda ake k'ara ta bayyana a gabanta.

Police d'in matan nan ne guda biyu suka fito da ita tatsaya a wajen da ake tsayawa, me karanta k'ara yace ya me girma me shari'a wannan itace Jawahir.
'Dago kai alk'ali yayi yakalleta nan yashaidata sannan yacigaba da cewa kotu tana son ganin lauyan masu k'ara da na wadda ake k'ara.

Barr MB ne yamik'e yayi sallama sannan yace sunana Barr Mahamud Bello nine lauyan masu k'ara,, sannan yakoma yazauna.

Shuru babu wanda yasake mik'ewa daga cikin lauyoyin, Barr Junaid dafe kanshi yayi tare da runtse idanunshi saboda tsananin tashin hankalin rashin abokinshi dan shi kanshi shara'ar da sukayi ta maimuna ya san ya yi k'ok'ari sosai a yadda ya iya yinta saboda tashin hankalin da yake ciki.
Me gabatar da k'ara ganin babu wanda yamik'e daga cikinsu yasa yak'ara cewa kotu tana son ganin lauyan wadda ake k'ara.

Jawahir idanu tazuba ma lauyoyin lokaci guda tasafke idanunta k'asa dan ta san babu lauyanta a ciki.

Me gabatar da k'ara ne yasake maimaitawa nan Barr MB yamik'e yakalli alk'ali yace ya me girma ne shara'a lauyan wadda ake k'ara ya gudu saboda baida bayanan da zai kare wadda ake k'ara da su.
Karaf a kunnuwan Barr Junaid lokaci guda yamik'e a harzuk'e yace k'arya ne ya me girma me shara'a lauyanta ba guduwa yayi ba akwai dalili me k'arfi da yahana bayyanarshi, kallon Barr Mb yayi yace ya kamata kadinga gyara kalamanka sannan yakoma yazauna.

Barr MB d'an rissinawa yayi sannan yakoma shima yazauna.

Alk'ali da yake kallonsu bayan sun zauna ne yace shin ko akwai wanda lauyan wadda ake k'ara yawakilta a cikinku?
Su duka shuru sukayi nan yasake cewa ko akwai wanda zai kare wadda ake k'ara?
Nan ma shuru.

Dan haka yaduk'a yayi 'yan rubuce rubucenshi sannan yad'ago yakalli jawahir yace Malama Jawahir kamar dai yadda shari'ar tamu ta baya takasance tsawon shekara d'aya har yau kin kasa amsa laifukanki akan zargin da akeyi maki shin ko a yau zaki iya kare kanki kafin kotu tazartas da hukunci na k'arshe?

'Dago kanta tayi takalli alk'ali sannan tamaida idanunta ga d'unbin jama'ar da suke zaune wajen kowa idanunshi akanta suna jira suji abinda zata fad'a, karaf idanunta suka safka akan mutum biyu.
Alhaji Mansur da Alhaji Sufyan murmushin mugunta suka sakar mata.
Idanu tazuba masu bata ko k'yaftawa musamman ma Alhaji Sufyan nan hawaye suka fara gangarowa daga cikin idanunta, tana ji kamar taje tashak'esu

Alk'ali sake maimaita mata tambayar yayi ammah bata ma san yana yi ba, saida police d'in wajen suka d'an ta'bota sannan tadawo hayyacinta.

Ganin bata ce komai ba yasa alk'ali yace shin ko Lauyan masu k'ara yana da k'wak'k'warar shaidar da zata ida bayyanar ma kotu cewa jawahir ce tayi kisan?

Mik'ewa Barr MB yayi yace tabbas ina da ita ya me girma me shara'a inaso kotu taban dama ind'anyi ma jawahir wasu 'yan tambayoyi.
Dama alk'ali yabashi nan yawuce yanufi inda jawahir take tsaye....



_____****______


Barr Faruk hankalinshi atashe yake a ranar duk k'ok'arin da yayi dan yakwance kanshi kasawa yayi yana nan zaune inda aka d'aureshi idanunshi suna a kan agogo har k'arfe tara da rabi tabuga, kallonsu yayi yaga suna zaune su biyu dan sauran ukkun basunan sun fita tare da ogansu gashi wad'anda sukafi rashin mutuncin ne suke zaune babu damar yarok'esu, runtse idanunshi yayi ahankali yace kiyi hak'uri Jawahir banda yadda zanyi in ceceki wannan itace k'addararki saidai ina maki fatan Allah yatseratar da ke,,, bud'e k'ofar da akayine yasa yai saurin bud'e idanunshi sai ganin d'aya daga cikinsune yashigo d'auke da takeaway, sauran yaji sunce ya dai bahbah wani abu aka kawo mana?
Zuwa yayi ya ajiye masu kowa takeaway guda yace wani aiki ne mukayi da oga yau mun samu kud'i sosai cikin kud'in ne yace ink'ara siyo mana breakfast tunda bamu k'oshiba, su dukansu dariya sukasa sukace dakyau, nan yakoma yazauna kusa da su, su kuma suka d'auka suka fara ci, Barr Faruk yana kallonsu suka ci abincinsu shi ko ba'ayi mashi ko tayi ba.
Faruk wasu irin hawaye ne masu gumi suka gangaro mashi saboda tsananin tausayin halin da Jawahir zata shiga yau, runtse idanunshi yayi yana cigaba da yi mata addu'a a cikin zuciyarshi.
Jin su yayi shuru dan haka yabud'e idanunshi sai gani yayi mutane biyu daga cikinsu sun hankad'e kai saman kujera suna bacci inda d'ayan yake zaune yana kallonshi.
Mamakine yakamashi cikin ranshi yace daga gama cin abinci sai bacci.

Bai ankaraba kawai sai gani yayi babu mutumin a wajen, mamakine ya ida kamashi yace ikon Allah ina mutumin nan yayi?

Murya ce yajiyo a bayanshi me firgitarwa wadda sautinta tacika d'akin gabad'aya yaji ance "barka da wannan lokacin Barr Faruk"
Yunk'urin waigawa yayi dan yaga me magana ammah yakasa saboda d'aurin da akayi mashi.

Ji yayi anbushe da wata irin mahaukaciyar dariya wadda tasa saida yad'an firgita, muryarce yaji tana cewa wannan aikina ne Barrister.
Dakewa yayi yace wanene nan? Ko ma wanene yabayyana min kanshi!! Shuru yaji nan yasake maimaitawa nan ma shuru dan haka yatabbatar da babu kowa d'akin.
Runtse idanunshi yayi tare da safke ajiyar zuciya.




**** *****

Barr MB kallonta yayi yace Malama Jawahir a iya binciken da mukayi mun gane cewa kin kashe Alhaji Mu'azu da 'ya'yanshi biyu wanda d'aya daga cikinsu mijine a gareki kinyi kisan ba dan komai ba sai dan kawai kina so kigaje dukiyar da ke gareshi.
Da mamaki tajuyo takalli Barr MB, bai damu da mamaki da yagani a fuskarta ba yacigaba da cewa, a lokacin da aka tuntu'bi Megadin ku ya bada shedar cewa daman kin dad'e kina yunk'urin kashe yayan mahaifin naki da shi da iyalanshi wannan dalilin ne yasa itama me aikin gidanku tagudu takoma garinsu saboda tsoron gargad'in da kika ta'ba yi masu a lokacin da suka ta'ba ganinki kin nufi d'akin kawun naki da wuk'a a hannunki lokacin yana bacci zaki kasheshi sai gashi 'yar aikin ta shigo ta ganki, a dalilin haka tatsorata takoma gidansu sannan shima megadinku bayan ankamaki da muka samu wannan bayanin daga wajenshi mun sake nemanshi dan musamu k'arin bayani ammah ya tsorata ya gudu ya koma garinsu chan Marad'i, shin ko zaki k'aryata wannan?

Baki tasaki tana kallonshi ganin yadda yake ta zubo mata k'arya.
Ganin batace komai ba yasa yacigaba da cewa sannan su kuma abokan mahaifinki kin kashesu ne saboda dalilin kun siyar masu da companynku wanda saboda karayar arzik'i yasa kuka rabu da shi shine daga baya kika dinga kashesu saboda kisamu kimaido companyn a hannunki, wannan bayanin mun sameshi a wajen sauran wad'anda suke da hannu wajen sayen companyn.....


Wata irin k'ara jawahir tasaki takai hannu cikin zafin nama tashak'e mashi wuya tace wallahi k'arya kake min, meyasa zakayi min k'arya.

Idanuwanshi waje sukayi saboda zafin mak'ara nan yafara neman yak'wace kanshi, police ne suka 'ban'bareshi daga hannunta alk'ali yace yakamata kisan a inda kike nan kotu ne ya zama dole kidinga ladabi.
Barr MB mik'a ma alk'ali takardun hannunshi yayi nan ya amsa yaduba sannan yad'ago yakalleta yace ga shaidar siyar da company da kukayi wanda a yanzu yake mallakin mutum biyu sannan ga duk bayani akan kisan da kikayi ko zaki iya kare kanki a gaban kotu me adalci?
Wasu sabbin hawaye ne suka gangaro mata tayi saurin runtse idanunta, Alk'ali sake maimaita mata yayi, ahankali tagirgiza kai alamun a'a.
Buga table Alk'ali yayi yace tunda bakida shedar da zaki kare kanki kotu ta yanke maki hukuncin.....tun kan alk'ali ya ida fad'a Jawahir tasulale tazauna k'asa d'irshen tare da fashewa da kuka dan ta san kisane kawai zai biyo baya gashi bata cika burinta ba.......







_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:15 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Ward Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 20*

K'ofar Kotun ce aka turo da k'arfi aka shigo wanda hakan yaja hankalin duk mutanen da suke cikin kotun suka juya dan ganin wanda zai shigo, shima kanshi Alk'ali bai ida fad'in hukuncin da yayanke ma Jawhir ba, wanda yabud'e k'ofar ne yashigo inda daga bayanshi sukaji murya ana cewa Ya Megirma me shara'a kar ayanke mata hukunci na zo da hujjoji masu k'arfi da zan bayyana ma kotu wanda zaisa agane batada laifi acikin kisan da akayi.


Jawahir na jin muryarshi saurin d'ago kai tayi tana kallonshi cike da mamaki, sanye yake cikin kayan aiki shi da nakusa da shi watau Barr Nas.

Alhaji Mansur da Alhaji Sufyan saurin mik'ewa sukayi tsaye mamaki duk ya bayyana a fuskarsu k'arara sukace kai daga ina kake ya akayi kazo nan?

Kallonsu Barr Faruk yayi yai murmushi sannan yataka yanufi wajen alk'ali yana cewa agafarceni ya me girma me shari'a.
Alk'ali gyara zaman farin glass d'inshi yayi sannan yace watau sai yanzu kaga damar zuwa, kotu zakayi ma wasa da hankali bayan a farko baka zo ba saida kotu zata zartas da hukunci sannan.

Matsowa yayi yace agafarceni ya me girma me shara'a babban daliline yahanani zuwa wanda idan kabani dama nagabatar da hujjata zan sanar da kotu dalilin.

Jinjina kai Alk'ali yayi yace kotu ta baka dama, kowa yakoma yazauna.

Nan duk aka zauna, Jawahir mik'ewa tayi tsaye daga duk'en da take tana kallonshi, shima kallonta yayi sannan yamaida kallonshi ga Alk'ali yace Allah yagafarta malam nagode sosai, a yau zan gabatar da shedun da natattara akan zargin da akeyi ma Jawahir ammah kafin nan inaso kotu tafara bani dama infara tattaunawa da wadda ake k'ara.
Alk'ali yace ta baka dama.
Juyawa yayi ga jawahir sannan yace shin malama jawahir ko zaki taimaka kifad'a ma kotu yadda kike da Alhaji Mu'azu da su Alhaji Tanimu?
Shuru tayi tana kallonshi, nuni yayi mata alamun tayi magana sannan tace Eh Alhaji Mu'azu yayan mahaifina ne su kuma abokan mahaifina ne bayan rasuwarshi suka koma tare da yayan mahaifin nawa.
Jinjina kai yayi yace dakyau sannan yajuya ga alk'ali yace Allah yagafarta malam hujjata ta farko da zan fara gabatarwa itace Marigayi Alhaji Mu'azu da Abokan mahaifinta su takwas kenan sunyi amfani da damarsu sun kashe mahaifinta da mahaifiyarta dan sugaje dukiyarshi ban fad'i hakan ba saida natabbatar da shedata.
Kotun ce tafara kacamewa da hayaniya jin abinda yafito daga bakin Barr Faruk, saida aka nutsar da mutane sukayi shuru.
Juyawa Faruk yayi yakalli k'ofa yace kushigo.
Wani buzu ne yashigo nad'e da rawani a kanshi sai wata dattijuwa tana tura wata mata a saman wheelchair, jawahir idanu tazuba ma matar ahankali tace Ummah, matar ma kallonta tayi nan hawaye suka gangaro mata.

Barr Faruk ne yanuna buzun yace wannan shine megadin gidan Alhaji Mu'azu wannan kuma uwar d'akinshi ce.

Alk'ali d'agowa yayi yakallesu sannan yace ma megadin kotu tanaso kafad'a mata gaskiya akan abinda kasani a game da gidan Alhaji Mu'azu.

'Dage kanshi sama yayi yace eh zan fad'i gaskiya ni nine megadin shi kuma wannan yarinya tun bayan mutuwar iyayenta Alhaji yake azabtar da ita yana cin dukiyarta shi da abokanshi, akwai wata rana ina zaune a wajen gate ina sauraren radio Alhaji yafito zai shiga mota yafita nan naji yana waya yana cewa zai san hanyar da zaibi yafito da ita suje banki yasa taciro mashi kud'i daga account d'in mahaifinta, toh bayan nan na ta'ba jin suna magana da wani abokinshi yana cewa zai siyar mashi da wani gida da yagano k'anen nashi yana da shi baisan da gidan ba sai bayan mutuwar d'an uwan nashi, sannan a game da mutuwar d'an uwan nashi a ranar da aka shigo aka kasheshi Alhaji Mu'azu najiyo yana magana da wasu a waje ban dai ji abinda yake cewa ba saidai na ji ya ce masu ga makullin gidan nan, toh kuma da makullin aka bud'e gidan aka shigo aka kasheshi, d'aga hannunshi yayi sama yace wallahi wannan shine abinda nasani banyi maku k'arya ba.
Alk'ali jinjina kai yayi sannan yaduk'a yacigaba da rubuce rubucenshi yace Barrister muna saurarenka.
Faruk juyawa yayi ga Ummah yace Hajiya munaso kifad'a ma kotu matsayinki a wajen Alhaji Mu'azu da duk abinda kika sani akan kisanshi.

Goge hawayen fuskarta tayi tare da motsa 'bari d'ayan jikinta da yake da lafiya sannan murya chan k'asa tafara magana ganin haka yasa aka d'auko mata lasifika aka kanga wajen bakinta fara jawabi tayi tace nice matar Alhaji Mu'azu kamar yadda kotu taso zan fad'a mata gaskiya maganar gaskiya tabbas ni da mijina mun cutawa yarinyar nan kuma ya ci dukiyarta wannan shine abinda nasani sannan itace takasheshi da 'ya'yana biyuuuuu, kyarma tafara yi tana jijjiga nan wasu nurse guda biyu sukayo saurin zuwa wajenta dan dama tare da su sukazo, alk'ali yabada izini afita da ita amaidata asibiti nan suka tafi da ita.

Barr MB me yamik'e a fusace yace ya megirma me shari'a ya kamata kotu tagaggauta hukunta lauyan wadda ake k'ara akan zuwa da yayi har asibiti yazo da marar lafiya wanda a halin yanzu ya ja ta shiga wani hali, wannan ba daidai bane.
Alk'ali d'agowa yayi yace Barr MB yace koma kazauna, komawa yayi cikin sanyin jiki yazauna


Barr Faruk cigaba yayi da cewa shedata ta gaba da zan bada itace Marigayi Alhaji Mu'azu da Abokan mahaifinta su takwas sunyi amfani da damarsu sun kashe mahaifinta da mahaifiyarta dan sugaje dukiyarshi ban fad'i hakan ba saida natabbatar da shedata, wayarshi yad'auko yakunno recording d'in duk maganganun da yatura na wayar da su Alhaji Mu'azu yayi da abokanshi d'aya bayan d'aya yakunna ma alk'ali yasaurara, gabad'aya kotun tayi tsit ana saurare, akan lokacin da suke had'a plan zasu kashe Alhaji muhammad da kuma kisan da sukayi ma mahaifiyar jawahir sannan wajen ciro kud'i dan su mallaki dukiyarta duk ya saurara

Alhaji Mansur ne yayi saurin mik'ewa yace wannan k'arya ne sharrinshi ne kawai.

Kallonshi alk'ali yayi yace kotu tana gargad'inka kar kasake sa mana baki in ba hakaba zaka fuskanci hukunci.
Komawa yayi cikin sanyin jiki yazauna sannan alk'ali yaduk'a yafara 'yan rubuce rubuce, nan Barr Faruk yacigaba da cewa wannan bayanin duk na sameshi a cikin wayar Alhaji Mu'azu saboda wayarshi tana saving d'in call recording, ga ma wayar ta shi nan yamik'a ma alk'ali yadudduba cikin wayar nan yajinjina kai, yace cigaba da bayaninka.
Cigaba yayi da cewa sannan duk ga bayanai nan akan dukiyarta da suka mallaka da takardun jabu da suka dinga bugowa shaidar sun sayi fili da gidaje daga hannun mahaifinta, ita kuma ta shigar da k'ara kotu ammah anyi watsi da k'arar wannan dalilin ne yasa tadinga d'aukar mataki da hannuwanta saidai batayi niyar kashe d'an uwan mahaifin nataba shine yafara neman kasheta sannan ita kuma dan takare kanta takasheshi, kamar dai yadda matarshi tayi bayani.
Alk'ali yace shin ko zamu iya samun bayanai agame da dukiyar Alhaji Muhammad d'in?

Eh Allah yagafarta malam ammah kafin nan inaso kotu taban dama inyi ma mutane biyu wasu tambayoyi wad'anda tambayoyin ne zasu taimaka wajen samun cikakkar sheda.

Alk'ali kotu ta baka dama su wanene mutane biyun?

Juyawa yayi yakalli Alhaji Mansur da Alhaji Sufyan da suke zaune suna zare idanu sunyi sharkaf da zufa,
Sannan yace Alhaji Mansur Maiharka da dollar sai Alhaji Sufyan me nasara.

Alk'ali ne yasake maimaita sunan yace kotu tana son ganinsu sun hallara a gabanta.
Su dukansu kusan tare suka mik'e cikin sanyin jiki suka fito suka tsaya.
Barr Faruk matsawa yayi kusa da su yace Alhaji Mansur da Alhaji Sufyan wasu 'yan tambayoyine zanyi maku ammah kafin nan ya kamata kufara sanar da kotu matsayinku a wajen Alhaji Muhammad.
Su dukansu sukace Na'am
Yace eh kar dai kumanta a kotu kuke ya kamata duk abinda zaku fad'a kufad'i gaskiya.
Gyaran murya Alhaji Mansur yayi sannan yakalli Alk'ali yace ni abokin kasuwancin Alhaji Muhammad ne a lokacin da yake raye bayan rasuwarshi ne muka koma kasuwanci da d'an uwanshi, wannan shine dalilin sanin da nayi mashi.

Murmushi Barr Faruk yayi sannan yakalli Alhaji Sufyan yace kaikuma fa me zakace?

Eh toh nima dai kamar yadda Alhaji Mansur yace nima haka nake da su.

Kana nufin kaima abokan kasuwancinka ne?
Eh haka.

Dakyau ammah a iya binciken da nayi na gane cewa ba wai abokin kasuwanci kawai bane akwai aminta a tsakaninku da su, ammah ba ma wannan ba na san kun san komai a game da mutuwar Alhaji Muhammad da me d'akinshi Khausar ko akwai abinda zaku iya cewa?

Alhaji Mansur ne cikin 'bacin rai yace kai banason zancen banza me kake nufi? Sharri zaka ja mana?

Barr MB mik'ewa yayi yace ya megirma me shara'a ya kamata kotu tagargad'i lauyan wadda ake k'ara akan irin tambayoyin da yakeyi ma su Alhaji Mansur domin suna muni agaresu.

Alk'ali kallon Barr Faruk yayi yace kagyara yanayin tambayarka.
'Dan rissina kai yayi yace nagode sannan yajuya garesu yace, kafin mutuwar Alhaji Muhammad kun ta'ba taruwa ku takwas a chan wani d'aki kukayi magana inda kowa yafurta abinda

30 / 74