Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Fansar RAI Complete 1&2 Complete Hausa Novel by SIS Nerja'art

Author :  SIS NERJA'ART Category :  African Stories & Novels

Chapter   52 / 74

153K to 156K   out of 220.3K words

doki saida tayi me isarta sannan tadogara sandarta tafara takowa ahankali inda suke tsaye jawahir saurin cewa tayi a'a kar kimatso nan kitsaya nan!
Bata musaba taja tatsaya tana me kallon Barr Faruk da yake tsaye bayan Jawahir kamar wanda ruwa yacinunashi tayi da yatsa cikin shak'ak'k'ar murya da bata fita sosai tace kai kai kana shiga hurumina dayawa, ina gargad'inka da kadaina inko ba haka ba rayuwarka zata zama tarihi.
Saurin tarar numfashinta jawahir tayi tace baidace kisake aikata kuskure ba a karo na biyu Ammi, shin shi kinga ya yi maki kama da mugayen mutane ne? Meyasa kin cika son kanki dayawa?
Bushewa tayi da dariya akaro na biyu sannan tace tunda har ya iya zuwa yad'auko memory d'innan tabbas ya aikata kuskure sannan nice kad'ai nake da ikon iya fitar da ke daga gidan nan ammah sai kinyi nadamar maganarki.
Cikin d'aga murya tace wannan ne kuma bazai ta'ba faruwa ba Ammi kece dai yakamata kiyi nadamar kashe yaya umar da kikayi!!

Bushewa tasake yi da dariyar mugunta sannan tace kisanar da shi yayi gaugawar maida Memory Card d'innan dan wannan shine umurni na.
Fitowa Barr Faruk yayi daga bayan Jawahir har ya bud'e baki zaiyi magana nan jawahir tayi mashi nuni da yayi shuru bai musaba yaja bakinshi yayi shuru, nan tsohuwar ta d'age kanta sama nan wani farin haske yabayyana wanda daga jawahir har Faruk idanunsu suka kasa jure kallon hasken dan kar yayi masu illa, su dukansu sukayi saurin runtse idanunsu har saida jawahir taji alamun bacewarta sannan tabud'e idanunta ajiyar zuciya tasafke tare da juyawa takalli Faruk da yabud'e idanunshi a daidai wannan lokacin tace yanzu aiki ya ganka sai ka yi da gaske sannan zaka iya tseratar da kanka daga Ammi daman wannan dalilin ne yasa tun farko nakasa fad'a maka komai dan nasan Ammi bazata ta'ba barinka cikin kwanciyar hankali ba ni kaina ba barina takeba kullum cikin azabtar da ni take.



Faruk da yazuba mata idanu sai a lokacin yayi magana yace ammah jawahir meyasa take cutar da ke bayan da fari tana taimakonki, miyasa tabari har aka kawo ki nan gidan kaso kina rayuwa marar 'yanci bayan ta san duk itace me laifi ba ke ba?

Juyawa tayi takalli gefe d'aya tare da yin guntun murmushi sannan tace dalili d'aya ne yasa duk take min haka ba wai komai bane sai dan kawai na furta mata kalmar tsana sannan nanuna inaso tarabu da ni ammah a maimakon tarabu da ni shine take wahalar da ni, nikuma hankalina baya kwanciya idan har tana cigaba da kasancewa tare da ni domin gani nake duk wanda yara'beni sai ta ga bayanshi, haka taso taga bayan wata ma'aikaciyar gidan nan akan matsa ma rayuwata da tayi saida nayi mata dagaske nanuna zan kashe kaina idan har tayi mata wani abu sannan tafasa saidai duk da haka saida tatsorata ta, taimako guda ne kawai nake buk'ata daga Ammina shine kad'ai yasa nake buk'atar kasancewarta tare da ni, ina jin dad'in d'aukar fansar da take tayani bana nadamar wannan domin shine hukuncin da yadace da azzalumai irinsu Alhaji Tanimu, ko a yanzu haka aka kasheni bazan ta'ba nadama ba dan na cika burina saidai abinda ba a rasaba ammah in da so samune ace na cika gabad'aya burin nawa,,, rintse idanunta tayi wasu siraran hawaye suka gangaro mata.
Faruk rasa abinda zaice mata yayi sunyi kusan minti biyar a haka sannan yace Jawahir kikwantar da hankalinki kamar yadda nayi maki alk'awali insha Allahu zan taimaka maki yanzu dai abu d'aya yarage kisanar da ni suwanene sauran mutanen da suke da hannu a mutuwar su Abbu insha Allahu ni kuma zanyi abinda yadace, sannan zanyi k'ok'arin had'a duk wata sheda waje guda kafin lokacin zaman k'arshe yayi a kotu ammah kafin nan ina zan samu Ummah? Sannan Megadin gidanku shima ina zan sameshi?

Ahankali tabud'e idanunta tasafkesu akan fuskarshi sannan tace Ummah tana chan asibiti kwance saboda tashin hankalin da tashiga jininta ya hau sosai sannan ga mutuwar 'barin jikin dama da takamu da shi (paralyse), na ji ance har yanzu batasan inda hankalinta yakeba bata magana da kowa saidai tabi mutane da kallo.

"Ammah toh wane asibiti ne aka kaita?"
Girgiza kai tayi tace nima ban saniba kawai dai abinda nasani ina nan gidan kaso wani lokaci Ammi da tazo wajena nan take nuna min abinda yafaru na ga komai a cikin tafin hannunta Ummah tana kwance bata iya komai likitoci suna ta k'ok'ari akanta saidai har tsawon wannan lokacin bata san inda kanta yakeba, saidai duk wannan abun da nagani ban gane wane asibiti bane, sannan megadin gidan mu buzu ne ainafin shi d'an k'asar Nijar ne bayan faruwar haka yagudu yakoma gida bamu san inda yake zaune ba a chan, Alk'ali ma saida yanemi akawoshi kotu dan amsa wasu tambayoyi saidai akazo aka fad'a mashi ya gudu kuma hakan ya faru ne saboda tsananin tsoratar da yayi akan kisan da akayi ma mutanen gidan kar shima abun yashafeshi.

Barr Faruk yace shikenan jawahir kikwantar da hankalinki ni na san yadda zanyi, zanje intattara duk wani bayanai da suke wajena saidai abu d'aya da ace zan sake samun wani abu da zai k'ara taimaka min da zanfi buk'atar hakan.

Shuru jawahir tayi kamar me tunanin wani abu sai kuma chan tace akwai abu d'aya da zaka iya samu saidai samunshi kamar ba abune me sauk'i ba.

Barr Faruk yace kar kidamu fad'a min shi koma menene zanyi bakin k'ok'ari kamar yadda na iya d'auko memory d'innan.

Cikin sanyin jiki tace ba wai a wajen Ammi zaka same shi ba, wannan yana a gidan Alhaji Tanimu da ace kana da damar da zaka iya shiga gidan har d'akinshi da ka samo wayar Abba da take hannunshi dan a lokacin da aka kamani sunyi amfani da wani key da suka sata sun shiga gidanmu sun yaye duk dukiyar Abba da k'addarorin shi, hatta wayarshi ma tana wajen Alhaji Tanimu saboda duk wayar da Abba zaiyi da mutum tana recording din maganar da sukayi tsawon wani lokaci kafin voice d'in yagoge indai har ba shi Abba yagoge ba toh yana cikin wayar, har sai and'an kwana biyu sannan maganar take gogewa , sannan wayar da yake kiransu da itace a wajen Alhaji Tanimu, ahakane nake gani zaka iya samun duk wasu bayanai da kake nema saboda maganganun da sukayi yana ciki wannan dalilin ne yasa yad'auke wayar ya adanata a cikin gidanshi batare da sanin kowa ba wannan itace kad'ai zata taimaka maka kagane sauran mutanen da Abba yake tare da su.

"Ammah jawahir wannan zai yi wuya gaskiya dan bana tunanin abu ne me sauk'i shiga cikin gidanshi har inje d'akinshi inyi bincike inma zan sanar da hukuma na tabbata babu wanda zai bani goyon bayan hakan gaskiya saidai kawai muyi hak'uri da wayar nan, toh ammah idan har sai cikinta zamu samu abinda muke buk'ata taya zamu iya hak'ura da ita?,,, kanshi ne yayi ma tambayar sai kuma yasafke ajiyar zuciya tare da kallon jawahir da tatsareshi da idanu yace bansan ta yadda zan iya shiga gidanba, ya kike gani ya dace?
" Nima bansan yadda za'ayi ba saidai kawai ahak'ura"

"A'a jawahir baza'a hak'ura ba zan je inyi tunani inga hanyar da yadace inbi dan inaso ingane ko suwanene suke da hannu a ciki kafin Amminki takashesu, bari intafi koma menene zaki ji ni zanyi k'ok'ari wajen ganin na samo mafita a cikin kwana biyu bazan dawo wajenki ba har sai na samo wayar na gane suwanene suke da hannu a ciki, saidai to wayar wace iri ce yadda zan ganeta?.
Tsayawa tayi tana tunani sai chan tace fara ce zaka ganta a cikin wardrope d'inshi ta gefen dama daga chan k'asan kayanshi nan zaka ganta.

Da mamaki yake kallontwa yace Jawahir duk ya akayi kika san wannan bayan ke kina nan cikin gidan kaso? Ko kema ba mutum bace!

Murmushi tayi har saida hak'oranta suka bayyana sannan tace zan sanar da kai ammah ba yanzu ba, sannan ni mutum ce kamar kowa, kaje kawai ina maka fatan samun nasara.


Juyawa yayi yatafi cikin sanyi jiki, daga nan office d'in Alhaji Mahadi yawuce yasameshi zaune ankawo mashi wasu mata sabbin zuwa guda biyu wad'anda suke da case na kashe mijinsu ganin Barr Faruk ya shigo yasa yace ma mataimakiyarshi atafi da su asasu cikin kurkukun d'akin nan k'arami wanda wasu mata ukku suke a cikin shi amsawa tayi nan taba wasu ma'aikata biyu umurni aka tafi da su.

Bayan suk sun fita Alhaji Mahadi yace bismillah Barrister kazauna.
Bai musaba yaja kujera yazauna.
Kallonshi Alhaji Mahadi yayi yana murmushi yace ya dai barrister na ga duk ka yi sanyi dayawa ko duk case d'in jawahir d'inne yake gwagwata ka?
Ajiyar zuciya yasafke yace ba ma haka ba abokina wani taimako nakeso DPO yayi min ammah ban san yanayin kirkin shi ba ko zai fahimci abinda nakeso.
Indai akan Jawahir ne bazai ta'ba fahimta ba dan ka san laifin da aka kamata da shi, kuma indai DPO ne bana tunani zai amince maka koma menene dan yana da tsatstsauran ra'ayi da ganin shi wani ne, musamman ma da yaga yadda kuke 'yar tsama akan case d'in yarinyar nan.
Ta'be baki Barr Faruk yayi yace koma menene dasannu zan wanke Jawahir daga zargin da ake mata.
Toh Allah dai yataimaka.
Ameen.



_________

Abban Nasiba ne yashigo yasameta Zaune ta tisa waya a gaba tana kallo ta shagala da kallon wayar bata ji shigowar mahaifinta ba, Alhaji Sufyan matsowa yayi idanuwanshi akan wayarta suka safka, girgiza kai yayi yace Nasiba har yanzu dai kina nan akan bakanki bazaki iya daina tunanin Faruk ba, inbakayi wasa ba sai na k'wace wayar nan tunda hotunanshi kike kallo a cikinta.
Saurin janye wayar tayi takifata a jikinta sannan tatashi zaune tare da sadda kanta k'asa.
Cigaba yayi da cewa kikwantar da hankalinki indai Faruk rabonki ne zaki sameshi kidaina sa damuwa a ranki kar kija ma kanki wani ciwon shi yana chan baima san kina yi ba.
'Dagowa tayi takalleshi tace toh Daddy insha Allahu zan kiyaye.
Amsawa yayi da yauwa 'yar lele haka nake son ji, tashi kije kikira min Hajiyarki sannan kije dining ga icecream chan na sawo maki dan nasan kina sonshi sosai.
Murmushi tayi tace toh Daddy nan tamik'e tatafi.

Bin ta yayi da kallo tare da girgiza kai yazauna saman kujera sannan yace Allah yakyauta.










_Sis Nerja'art✍🏻_[7/24, 11:13 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Award Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 11*

Tsawon kwana biyu Barr Faruk yad'auka yana tunanin hanyar da zaibi yashiga gidan Alhaji Tanimu har yasamu damar zuwa d'akinshi yad'auko wayar saidai babu hanyar da yaga zata 'bule mashi dan ranar sadakar ukku ma saida yaje gidan da sunan gaisuwa yaje masu hatta parlorn Alhaji Tanimi ya shiga yai ma 'yan uwanshi gaisuwa dan a cikin parlorn wasunsu suka zauna saidai hankalinshi ba k'aramin tashi yayi ba nan yasare yasan hakan saidai a mafarki zai iya faruwa.


A gefe d'aya ga Ammin Jawahir da tatakura mashi dan kusan kullum sai ya yi mafarki da ita ko kuma cikin dare tatasheshi daga bacci ayi ta tsorata shi.



Yau ma bayan ya gama had'a bayanenshi wajen k'arfe sha biyun dare ya gama shirin kwanciyarshi har ya kwanta nan ya
fara jiyo motsi kamar ana hawan step, ana kiran sunanshi tashi yayi zaune cikin ranshi yace tabbas nasan itace , jiyayi ana cigaba da hawa babu k'ak'k'autawa yanayin yadda ake taka benen kamar irin ansa takalmi masu tsini, sai ji yayi anfara k'wank'wasa mashi k'ofa, magana yafara jiyowa kamar ta mahaifinshi yana tambaya wanene nan?
Cikin sauri Faruk yamik'e yaje yabud'e ammah baiga kowaba dan haka yafita sai ganin Dad d'inshi yayi tsaye a chan wajen part d'insu gaban Faruk saida yafad'i ahankali yace ba dai tado su Dad tayi ba, muryar Dad yaji yana cewa Faruk wanene yake k'wank'wasa k'ofa na fito zan d'auki ruwa marassa sanyi dan na cikin freezer d'in part d'ina duk sunyi sanyi shine naji kamar ana knocking d'in k'ofa.
"Dad babu kowa nima ruwan nafito ind'auka ammah banji k'arar k'omai ba",, Cewar Faruk.

Tsayawa Dad yayi yana kallonshi yace yanzu kai baka ji ba? Ni na jiyo ana kwank'wasawa kamar ma ta part d'inka.
Murmushi Yayi yace Dad ka fara tsufa ne saisa kaji haka nidai da nake sabon jini ban jiyowa.
Girgiza kai Dad yayi yana murmushi yace kai ko faruk shikenan dai yanzu koma kakwanta k'arfe d'aya ta yi.

" Toh Dad kaje kakwanta bari inje ind'auko ruwan ammah dan Allah kadaina fitowa a wannan lokacin kaga darene".

Shikenan Faruk zan daina nima dai saboda k'ishin da nakeji yasa nafito ammah zan daina, je kad'auko ruwan bari intafi sai dasafe.
Yauwa Dad Allah yakaimu.

Saida yaga shigewar Dad sannan yafara safka daga saman step d'in ahankali yana lek'awa yaga ko zaiganta ammah baiga kowaba har yaje wajen fridge sai kuma yafara jiyo motsi achan tsakar gida har zai je yabud'e k'ofa yafita sai kuma yafasa dan ya san da ya bud'e sai su Dad sun jiyo kuma sai sun fito dan haka kawai yajuya zai koma part d'inshi sai jin k'ara yayi wajen kunnenshi wani irin shuuuuu kamar wucewar iska anbi ta bayanshi.
Juyawa yayi saurin yi tare da cewa wanene? Koma waye yabayya kanshi!!
Shurun da yaji anyi yasa yajuya yacigaba da tafiyarshi.

Yana zuwa part d'inshi shiga yayi batare da ya murza key ba yawuce yanufi bedroom tun kan yashiga sai ji yayi k'ofar parlor d'in da yarufe ta bud'e kanta da k'arfi, juyawa yayi cikin 'bacin rai yace koma wanene yabayyana kanshi mana, shuru yaji dan haka yaje yayi bismillah yarufe k'ofar sannan yaje yashiga bedroom d'inshi, yana shiga hasken d'akin yad'auke daidai da ya rufe k'ofa, jingine jikinshi yayi da k'ofar ahankali yafara karanto addu'o'i, muryace yafara jiyowa daga wajen gadon shi tana tashi da k'arfi ana cewa barka da wannan lokacin Barr Faruk.

Cikin dakiya da nuna rashin tsoro yace koma wacece na ce ya kamata tabayyana kanta.
Dariya yaji an bushe da ita kamar irin haniniyar dokin nan saboda k'arfin dariyar har saida yayi saurin toshe kunnuwanshi saida yatabbatar da dariyar ta lafa sannan yasaki kunnuwan tare da cewa wannan alama ce ta matsoraci duk jarumi bayyana kanshi yakeyi, na san kece Ammin Jawahir shin menene yakawoki wajena ko nima d'in kinzo ne dan kiga bayana?

Tun kan yarufe baki yaji wata irin murya me tsoratarwa cikin k'araji tana cewa da ace kana da hannu a ciki da sai na ga bayanka a yanzun nan, sannan ni ce kad'ai yakamata intaimaka ma jawahir tabar gidan nan aduk lokacin da naso, ikona ne wannan ba naka ba saidai jawahir tana da taurin kai sosai ta kasa yin nadama akan kalmar tsanar da tajefeni da ita, kai d'in kuma baka burgeni koda kana k'ok'ari wajen ganin ka taimaki d'iyata dan haka ina gargad'inka da kayi baya daga case d'in nan, wannan shine kad'ai abinda yakawoni wajenka,,, tana fad'in haka sai ji yayi shuru nan hasken d'akin yadawo.


Murmushi yayi ahankali yace wannan ne kuma bazai yuwu ba dan ni nasa kaina kuma babu wanda ya isa yasani injanye ban damu da koma wacece ke ba dan baki gabana da mutane irina nake da lokacin jayayya,,, wucewa yayi yadudduba ko'ina bai gantaba dan haka yaje yahau gado tare da yin addu'o'i yakwanta ko kad'an tsoro bai d'arsu cikin ranshi ba dan ya san addu'a itace takobin mumini, saidai tunda yakwanta bai samu yarintsa ba kamar kullum yana ta tunanin mafita har wajen k'arfe hud'u sannan yad'an samu bacci kafin daga bisani yatashi lokacin sallar asuba.



Hankalinshi k'in kwanciya yayi ganin kwanaki goma ne kawai suka rage mashi wata dabara ce tafad'o mashi dan haka bayan ya yi breakfast yakira wani abokinshi Barr Nas a waya tare suka yi karatu har wajen aikinsu d'aya lokacin da yake aiki a SHARI'A COURT abokai ne sosai dan koda a yanzu ba wajen aikinsu d'aya ba suna tare, bayan sun gaisa ne yatambayeshi inda zai sameshi yafad'a mashi kasancewar weekend ne babu aiki, shiryawa yayi yad'auki system d'inshi da komai wanda zai buk'ata yashiga motar shi yanufi gidan Barr Nas yana isa daidai lokacin shima yashawo kwana Barr Faruk tsayawa yayi har saida ya iso da motarshi nan yafito yanufo wajen Faruk yana murmushi yace Barrister kace dai dagaske kake zaka zo.

Hmm dole kace haka tunda ka san baka gidan kaja nazo ashe da saidai inkoma.
"A'a Wallahi ban dad'e da fitaba na kai Madam gidane ina safketa najuyo dan kar kazo ban nan, yanzu dai mushiga da mota ciki.

Barr Faruk ba tare da ya ce komai ba yatada motar shi, saida Barr Nas yashiga tashi motar yayi horn megadi yabud'e masu gate sannan suka shiga da motocin, bayan sunyi parking ne suka nufi parlorn gidan Barr Nas yana cewa yau dai kamar a mafarki sai gaka a gidana ina ji rabon da kazo tun bikkina.

"Toh ka dai san yanayin aikin mu bamuda lokacin zama bare har inzo gidanka, yanzu ma haka akan aikine yasa kaganni"

Hmm nasan haka kai kullum da aiki kake fakewa, malam muma fa duk aikin nan muke irin naka ammah a haka muna samun lokacin ziyara kai ko kullum saidai kabada wani uzuri, ko dai Nasiba ce take 'boye mana kai tun ba'ayi bikkin ba?

Murmushi yayi jin an ambaci sunan abun son shi saidai a ranshi yana tunowa da wani abu yasafke ajiyar zuciya yace Nasir muyi maganar da takawoni wajen ka.

Toh shikenan Barr ina saurarenka.

Barr Faruk yace daman wani taimako ne nakeso kayi min dan nasan kaine kad'ai zaka iya yimin yadda nakeso,

Gyara zamanshi yayi yace wani irin taimako ne wannan koma wane iri ne kafad'a zanyi maka indai baifi k'arfina ba koda ma ya fi zansan yadda zanyi intaimakeka.

Murmushi yayi sannan yace ranar sadakar ukku watau jiya na ga

52 / 74