Author : SIS NERJA'ART Category : African Stories & Novels
dubawa daidai lokacin taji anrage k'arfin shower d'in, bubbud'ewa tayi cikin sauri tana dubawa tad'auko wasu files guda biyu tamaida sauran tarufe drower sannan tad'auka, jiyo murya tayi a cikin toilet d'in ana cewa Hajiya ke ce ganinan ina wanka, mik'o min towel.
Kallon k'ofar toilet d'in tayi sannan tawuce cikin sauri tafita tarufe d'akin, dagudu tasfka daga saman benen, hayaniya tafara jiyowa a gudan d'akin na mutanen gidan dan haka cikin sauri tafita, a filin gidan tasamu megadi tsaye saita nutsuwarta tayi sannan tawuce zata fita, kallonta yayi ammah ita ko bata kalli inda yakeba tana ji yace sannu Hajiya dan ya d'auka ko k'awar d'iyar gidan ce, amsawa tayi sannan yabud'e mata k'ofa taficce.
Tana fita ajiyar zuciya tasafke dan ita kanta ta san ba k'aramin namijin k'ok'ari tayiba da har tayi kasadar shiga cikin gidan, takawa tafara yi har tasamu napep tashiga sannan tafad'a mashi inda zai kaita ranta fal da farin ciki ta yi nasarar samo abinda takeso, ahaka har suka isa asibitin, suna isa talaluba dan tabashi kud'i sai taji wayam ba jakka ajiyar zuciya tasafke cikin ranta tace da da yanzu ba d'aya bane, muryar dattijon taji ya ce d'iyata munzo.
Cikin sanyin jiki tace kayi hak'uri baba ina tunanin kud'in da zan biyaka ne ashe babu kud'i atare da ni.
Juyowa yayi yakalleta yace kamar ya bakida kud'i ai bakiyi kama da marassa kud'iba d'iyata.
Cikin sanyin jiki tace dagaske nake Baba wallahi banda su.
Gyad'a kai yayi yace toh shikenan jeki kawai na yafe.
Godiya tayi mashi cikin jin dad'i sannan tafita, tafiya tafara yi bata ankaraba sai gata ta gaban 'yansandan nan cikin sauri tajawo gyalen tasake rufe fuskarta, murya Barr Faruk tajuyo da bai dad'e da dawowa asibitin ba alamun yana waya dan haka tadake tawuce tazagaya baya babu wanda yaganeta daga cikinsu, tsayawa tayi saida taga wasu mutane sun wuce sannan tataka dakali tawurga files d'in ta cikin tagar sannan itama tasamu tahau tadira aciki, tana dirawa tayi saurin cire kayan jikinta ta ajiye a nan cikin toilet d'in tad'auko unifoam d'inta na gidan yari tasaka sannan tad'auko files d'in, saida tad'an kanga kunnenta a wajen k'ofa jin ba motsin kowa yasa tabud'e ahankali tashiga, saurin jawo 'yar k'aramar drower da take ajiye cikin room d'in tayi wadda aka ajiye saboda ajiye ma patient kaya, tasaka files d'in.
Doctor ne yatafo yana cewa bari inshiga yanzu lokacin farkawarta ya yi idan har mukaga ta farka babu wani ciwo atare da ita sai mu sallameku, d'aya daga cikin masu kula da gidan yarin ne yace tabbas hakan yakamata Doctor dan yarinyar chan tana da had'ari zamanta a gidan yari shine kwanciyar hankalinmu, shidai bai fahimci abinda yake nufiba saidai yayi murmushi yabud'e k'ofar yashiga.
Kwance yasameta ta lulle'be har fuskarta yana isa yajanye mayafin ahankali tabud'e idanunta, murmushi yayi yace ashe kin farka ai na d'auka yanzu ne yakamata ace allurar ta sakeki, shuru tayi tana binshi da kallo, kallon hannunta yayi yaga ba kanula yace ya akayi kika cire?
Kallon hannun nata tayi sannan tace am daman daman na ji yana min zafi ne.
Ohk, akwai inda yake maki ciwo yanzu?
Girgiza kai tayi, nan yasake dubata yace saidai na san har yanzu kina jin ciwon kan ammah zasu dinga maki dressing d'in ciwon naki.
Batace komai ba saima kallonshi da takeyi ganin haka yasa yarubuta mata sallama tare da magungunan da za'a siya mata bayan ya gama yafita yasanar da su dan haka wasu police mata biyu suka shigo tana a nan inda take kwance suka saka mata ankwa a hannu, kallon hannuwanta tayi sannan tatashi suka izata a gaba suka fita da ita d'akin nan duk 'yansandar suka rufa masu baya, juyawa tayi takalli Faruk da yake waya har lokacin shima ya juyo yana kallonta, motsa baki tayi alamun tana son yin magana sai kuma tafasa sai tayi mashi nuni da idanu alamun yazo yaji.
Kashe wayar yayi yatako wajen yana zuwa yatsaya yace har an sallameta sukace eh,
Bakinta takai saitin kunnenshi tarad'a mashi wani abu wanda babu wanda yaji abinda tace sannan tawuce aka tafi da ita.
Tsayawa yayi a wajen har suka wuce sannan yaje yashiga d'akin yaduba drower yafiddo files d'in, tsaye yayi yana kallon files d'in mamaki duk ya cikashi cikin ranshi yace ita kuma ina tasamosu ko dai ta fita daga gidan kason nan? Kallon d'akin yayi yace ammah kuma ai ba hanyar da zata fita batare da ansaniba, wayarshi ce da tafara ringing yasa yayi saurin fita daga d'akin tare da kanga wayar a kunnenshi yanufi wajen motarshi.
Yana komawa gida zama yayi yabud'e files d'in yana dubawa cikin ranshi duk mamaki ya gama cikashi ganin yadda akayi tasamesu, chan kuma yayi murmushi yace wannan aikin naki ya yi sosai Jawahir, toh ammah idan yazama Amminta ce tad'auko su fa? Girgiza kai yayi yace wannan ne kuma bansaniba ko ma ya akayi na ji dad'in samunsu sosai.
Wayarshi yad'auko yad'auki files d'in hoto sannan ya ajiye yashiga shigar da su acikin laptop d'inshi bayan ya gama ne yakira Barr Nas a waya suka tattauna daga nan kuma yatashi yafara shirin fita.
A chan 'bangaren Alhaji Mansur hankalinshi a tashe yake sosai akan yadda Barr Faruk yakeson ganin ya tona masu asirin da yake binne babu wanda yasan da shi dan haka yafara tunanin yadda zai 'bullo mashi.
Ranar wata talata Barr Faruk yana gida da marece Alhaji Mansur yakirashi a waya, ya yi mamakin ganin kiran nashi sosai kamar ba zai d'agaba har tatsinke yana tunanin kiran me yakeyi mashi chan sai wani kiran yasake shigowa dan haka yayi picking batare da yayi magana ba.
Jin anyi picking yasa Alhaji Mansur yakalli nakusa da shi yayi murmushi sannan yace Barrister ina fatan kana jina?
Daga chan 'bangaren Faruk yace Eh ina ji.
Mik'ewa yayi tsaye sannan yace idan babu damuwa inaso yanzu muhad'u da kai a gida akwai maganar da nakeso muyi.
Shuru Faruk yayi baice komai ba.
Ganin haka yasa Alhaji Mansur yayi tunanin ko bai yarda da shi ba dan haka yace inma bazaka zo ba toh kafad'i inda yadace muhad'u.
Cikin gadara da nuna isa yace idan zaka iya zamu had'u a chan Rahama Restuarent.
Toh shikenan nan da rabin awa zaka sameni a chan.
Batare da ya amsaba yakashe wayar.
Tsaki Alhaji Mansur yayi yace yaron nan ya cika jin kan tsiya shi gani yake kamar shi wanine ammah bakomai zan safke mashi girman kan nan nashi bari inje inshirya intafi duk yadda mukayi da shi zaka ji.
Suna gama wayar yatashi yashiga wanka yashirya yafita.
Yana isa Rahama Restuarent babu mutane sosai a ciki yaja kujera yazauna nan yabada umurni akawo mashi coffee yana cikin sha ne Alhaji Mansur ya iso yafara ware idanu yana tunanin inda zai zauna kafin Faruk ya iso da mamakinshi sai hangoshi yayi zaune, murmushi yayi sannan yanufi wajen yaja kujera yazauna yace ashe har ka iso.
Batare da ya kalleshiba yace Eh, me kake buk'ata akawo maka?
Yatsina fuska yayi yace bana buk'atar komai.
Batare da ya ce komai ba yacigaba da shan cofee d'inshi, Alhaji mansur hannu yasa a aljihu yazaro cheque ya ajiye mashi a gabanshi yana murmushi yace gashi
Batare da ya kalli cheque d'inba yace menene wannan?
'Yar dariya yayi sannan yace abokan rayuwa ne mana kakalla kagani.
Kallon cheque d'in yayi yai murmushi sannan yacigaba da shan coffeen shi.
Ganin haka yasa Alhaji Mansur yayi tunanin ya yi nasara yace wannan gabad'aya na mallaka maka su kaje kacire inma basu ishekaba kayi min magana ink'ara maka wasu.
Sai a lokacin ya ajiye coffeen yad'auko cheque d'in yaduba murmushi yayi yace 5billions, me kakeso inyi maka ne?
Bushewa Alhaji Mansur yayi da dariya yace dakyau haka akeso kud'i masu canza kowa, gyara zamanshi yayi yace yauwa ka yi tambaya mekyau abu d'aya nakeso kayi shine kajanye daga case d'in yarinyar chan, idan har kayi haka ni kuma zan k'ara maka linkin wad'annan kud'in.
Jinjina kai Faruk yayi yana murmushi yace wannan ne daman dalilin kiran da kayi min.
Eh shine kaga sai mutaru murufa ma juna asiri kai kaci dukiya ita kuma akasheta, kai kowane lokaci ma kaji kana son kud'i kakirani ni kuma zan aiko maka da su batare da 'bata lokaci ba.
K'ara duba cheque d'in yayi gaba da baya sannan yayageshi yawurga mashi.
Baki Alhaji Mansur yasaki yana kallonshi cike da mamaki yace kai kana da hankali kuwa? Ka san abinda ka aikata?
Mik'ewa yayi tsaye lokaci guda fara'ar da take fuskarshi tagushe cikin d'aga murya yace ni ko nasan abinda na aikata dan ni ba irin sakarkarun lauyoyin da ake siya bane, idan har kanaso kaga 'bacin raina toh kace zaka siyeni da kud'i, ka kalli kanka kai ba abun kunya bane kakalli kamata kace zaka siyeni da kud'i? Ko ka mance wannan Barr Faruk Sani Maishadda ne lauyan gaskiya?
K'ut Alhaji Mansur yahad'iye wani wahalallen yawu duk idanu suka raina fata dan bai d'auka zai ga haka daga wajen Faruk ba.
Girgiza kai yayi yace bazaka ta'ba samun hakan daga gareniba dan ni aikina gaskiya nake karewa bana d'aure ma k'arya gindi dan haka kawai kasaurari nan da kwana biyar zamanmu a kotu, yana fad'in haka yajuya a fusace zai tafi sai jin muryar Alhaji Mansur yayi ya ce Faruk kar ka aikata wannan kuskuren dama ce guda d'aya nabaka kaje kayi tunani cikin kwana biyu idan har baka canza tunaninka ba toh komai zai iya faruwa.
Ja yayi yatsaya har yagama sauraren maganar tashi sannan yawuce yayi tafiyarshi.
Buga teburin Alhaji Mansur yayi tare da furta shiittt!! sannan yamik'e ranshi a 'bace yatafi...
*BAYAN KWANA BIYU*
Daddyn Faruk ne zaune a parlornshi hannunshi rik'e da Jarida yana dubawa inda gefenshi matarshi ce zaune tana dannar waya, wayarshi da take gefenshi ce tafara ruri nan yad'auko ganin number ce ba suna yasa yace ko wanene yake kirana da wannan number d'in?
Hajiya Nuratu murmushi tayi tace kad'aga kaji ko wanene Alhaji.
Bai musaba yayi picking tare da yin sallama.
Wata irin murya yaji wadda babu alamun mutunci a cikinta akace ina fata ina magana da Alhaji Sani Maishadda?
Kallon Haj Nuratu yayi da itama take kallonshi sannan yace Eh shine da wa nake magana?
Sanin da wanda kake magana ba dole bane dan ba shine dalilin da yasa nakiraka ba saidai ina so kabud'e kunnuwanka kasaurareni dakyau, kaja ma d'anka kunne yafita daga harkarmu inko ba haka ba zaya gane cewa ya ta'bo tsuliyar dodo dan zamu farauci rayuwarshi.
A kid'ime Dad yamik'e tsaye cike da tashin hankali yace Hello ina ji dan Allah me d'an nawa yayi maku?
Bushewa akayi da dariya sannan akace bakaga komai ba daga cikin tashin hankali indai har bai zare hannuwanshi daga case d'in Jawahir ba dan indai har yace zai cigaba da kareta zamu kasheshi.
Dad ida rud'ewa yayi cikin rawar murya yace dan Allah kuyi hak'uri kar kukashe shi wallahi shi kad'ai namallaka na yi maku alk'awali zai janye.
Kar ma yajanye mudai mun fad'a maku kugargad'eshi dan yaron nan naku ya cika taurin kai saidai ba irinmu ake ma taurin kai ba dan zamu iya rabashi da rayuwarshi....ana fad'in haka aka tsinke kiran, Daddy nan yafara cewa hello hello ammah yaji shuru sai lokacin yagane cewa ankashe wayar, wurgi yayi da wayarshi saman kujerar tashin hankali k'arara yabayyana, Hajiya Nuratu da take tsaye gefenshi itama hankalinta a tashe ganin yadda mijin nata hankalinshi yatashi sosai tace Alhaji lafiya me yafaru.
Alhaji Sani da yafara kwarara zufa kallonta yayi sannan yakoma yazauna nan itama tazauna gefenshi tace dan Allah kayi min bayani menene yafaru.
Girgiza kai yayi yace Nuratu muna cikin matsala dan anfara farautar rayuwar Faruk akan aikinshi.
Saurin dafe k'irji tayi cike da tashin hankali tace me? Rayuwar d'ana ake farauta? Me yatsare masu?
Ajiyar zuciya Dad yasafke sannan yace akan wai case d'in Jawahir sukace idan har bai janyeba sai sun kasheshi.
Fashewa da kuka Haj Nuratu tayi tace na shiga ukku d'an nawa zasu kashe? Inko har hakana ya zama dole ya ajiye aikin nan gabad'aya dan wallahi inason d'ana banason inrabu da shi.
Cikin sanyin jiki Alhaji Sani yace wannan dolene Hajiya mik'o min wayata yanzu inkirashi.
Mik'ewa tayi cikin sauri tad'auko mashi wayarshi tamik'a mashi tana cigaba da kuka cike da tashin hankali gabanta yana dukan ukku ukku akan kalmar kisa da aka furta za'a yi ma tilon d'anta.....
_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:14 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*
*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Ward Together]
_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_
_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_
_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_
*PAGE 17*
....Lalubo number d'in Faruk Daddy yayi yakira ammah har tatsinke ba'ayi picking ba, dan haka yasake kira, saida yayi mashi 5 missed bai d'aga ba, lokacin Faruk yana gidan kaso wajen Jawahir ya bar wayarshi a cikin mota dan bai shiga da ita yanzu saboda a tsarin dokar gidan ba'a bari ashiga da waya shine ma ake d'aga mawa yana shiga da ita saboda kusancinshi da shugaban gidan saisa.
Kallon Jawahir yayi da tunda yazo take zaune ta yi shuru jikinta ya yi sanyi sosai yace wai jawahir me yake faruwa da ke ne haka na d'auka abin farin cikine tunda kwanaki ukku kawai suka rage mana.
Girgiza kai tayi tare da yin d'an guntun murmushi sannan tace Barrister bazaka fahimta bane ina tsoron halin su Alhaji Mansur su d'in mugaye ne sannan ina bak'in cikin abinda yafaru da kai da budurwarka duk a kaina.
Murmushi yayi yace indan wannan ne kikwantar da hankalinki insha Allahu babu matsala sannan maganar Nasiba kibarta kawai na san fushi take da ni ammah da sannu zata safko dan muna son junanmu sosai.
Gefe d'aya takalla tana murmushi ahankali tace Yaya Umar d'ina sai kuma tafashe da kuka.
Hankalin Faruk tashi yayi yace Jawahir lafiya kukan me kikeyi haka?
Girgiza kai tayi tace nima ban saniba saidai kawai ina son Yaya Umar tabbas Ammi ta cutar da rayuwata taya zan iya yafe mata wannan laifin da tayi min na rabani da rabin rayuwata? Shin ita batasan mecece soyayya ba? Shin ta mance yanayin da tashiga a lokacin da tarasa Abbuna?,,, mik'ewa tayi tsaye cikin muryar kuka tace na san bata mance hakan ba kawai dai ta yi amfani da son zuciyartane wajen rabani da masoyina.
Mik'ewa shima yayi yace Jawahir kidaina tuna abinda yawuce.
Taya zan daina tunawa bayan ta dasa min ciwon da bazai ta'ba warkewa a cikin zuciyataba, saurin sa hannu tayi tagoge hawayen fuskarta sannan tajuyo takalleshi tana murmushi tace ka ga katashi katafi azahar ta yi.
Kallon agogon da take manne a tsintsiyar hannunshi yayi yace hakane bari intafi ammah bazan dawoba yau.
Murmushi tayi tace ba damuwa Barrister hakan ma nagode a kowane lokaci ina maka fatan alkhairi a cikin rayuwarka, musamman akan jajircewarka a lokacin da kuka had'u da Alhaji Mansur ba kowane za'a ba wad'annan mak'udan kud'in ya iya barinsu ba.
Da mamaki yake kallonta yace ya akayi kikasan hakan?
Murmusai tayi a karo na biyu sannan tace wannan ba abun mamaki bane, yanzu dai katafi kar karasa jam'i.
Jinjina kai yayi sannan yawuce yatafi.
A nan cikin masallacin gidan kaso yayi sallah sannan yashiga motarshi bayan ya fita daga gidan ne yad'auko wayarshi sai ganin 5 missed call yayi yana dubawa yaga Dad ne mamaki yakamashi yace lafiya kuwa Dad yayi min wannan missed call? Dialing d'in number d'in Dad yayi, lokacin Dad yana tsaye yana kaiwa da kawowa hankalinshi a tashe yana add'ua Allah yasa ba wani abu yasamu d'an nashiba itako Mom zaune take tana fitar da sautin kuka ahankali adaidai lokacin wayarshi da take hannunshi tafara ringing, jikinshi yana rawa yaduba sai ganin Faruk yayi ajiyar zuciya yasafke sannan yad'auka ko sallama baiyi ba yace Faruk kana ina?
Daga chan 'bangaren yace ganinan a mota Dad zan dawo gida lafiya dai ko?
Muryar mom yajiyo tana cewa kace mashi yayi sauri yadawo gida yanzun nan, nan Dad yafad'a mashi.
Amsawa yayi da toh duk sai jikinshi yaji ya yi sanyi ganin hankalin iyayenshi yadda yatashi dan haka yagane akwai dai wani abu, duk da yanaso yawuce gida saidai kuma yaji ya fiso yafara yin abinda zaiyi kafin yaje gida dan haka ya yalalubo wata number yakira yana gama wayar yak'ara ma motarshi gudu cikin k'ank'anin lokaci ya isa inda zaije.
Baifi minti sha biyar ba yafito yatafi gida yana isa a parlor yasamesu cirko cirko suna ta kaiwa da kawowa ja yayi yatsaya yace Dad Mom lafiya naganku haka?
Mom ce tayi saurin isowa wajenshi tare da fashewa da kuka, nan hankalinshi yatashi yace me yafaru Mom?
Muryar Dad d'inshi yajiyo yana cewa dole katambayi me yafaru Faruk ka ja and'aga mana hankali toh wallahi bazamu iyaba ya zama dole ka ajiye aikin nan naka.
Cikin rashin fahimtar abinda yafaru yace Dad me yasa? Me yafaru da har zakayi wannan furucin?
Jinjina kai yayi yace Faruk komai ma ya faru akan aikin nan ake barazana da rayuwarka har ake kiranmu waya ana gargad'inmu idan har baka janye daga wani case ba za'a kasheka.
Murmushi yayi yace haba Dad wai dan wannan ne kukwantar da hankalinku babu abinda zasuyi min kawai dai sun fad'a ne dan sutsorata ku.
Mom ce tadaka mashi tsawar da bata ta'ba yi mashi irinta ba tace kai shashashan ina ne? Ina kata'ba jin anyi irin wannan? toh wallahi baka isaba Faruk ya zama dole ka ajiye aikin nan akan wani banzan case ka rasa matar da zaka aura ka 'bata da surukinka sannan kuma a yanzu wasu suna barazana da rayuwarka ai ba dole sai ka yi aikinba.
Girgiza kai yayi yace a'a Mom dan Allah kar kuyi min haka.
Muryar Dad ce takatseshi yace Faruk bamu shirya kwana zaune ba ka san dai bamuda wani d'a bayanka dan haka ya zama dole ka ajiye aikin nan gabad'aya dan gudun had'arin da yake cikinshi.
Gaban Faruk saida yafad'i ahankali yace na shiga ukku menene yake faruwa da ni? Su wanene suka kira iyayena, tabbas nasan bai wuce mutane biyu,,, matsawa yayi wajen mahaifin nashi yace dan Allah Dad kuyi hak'uri kar kurabani da aikina wallahi sunyi hakane kawai dan injanye daga case d'in jawahir suna so sutauye mata hak'k'inta kuma janyewata daidai yake da