Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

RANAR NAKA Complt Complete Hausa Novel by Fareeda Abdallah

Author :  FAREEDA ABDALLAH Category :  African Stories & Novels

Chapter   3 / 53

6K to 9K   out of 157.3K words

waWannan kwanaki uku, duk abubuwan da suka biyo baya ha?uri kawai take yi tana kawar da kai.

Zulaikha da ta kasance mara ha?uri kamar fitar zawayi kuma tun dama can ba'a shan inuwa Waya da matar Hafizun ita take ta cika tana batsewa kan abubuwan da suke gani na rashin kyautawa. Har zuwa yau da tayi gaban kanta ba tare da saninta ba ganin har ?arfe huWu na yamma ba'a kawo musu abinci ba tun bayan karin safe, ta shiga har can cikin gidan har wannan abun ya faru.'

"Auta?"
Ta kira sunan Zulaikha bayan ta katse tunanin da take yi ta mayar da hankalinta kanta.

"Na'am Innaye."
Ta amsa tana cigaba da zuba farfesun naman kaza kan soyayyar shinkafar da ta zuba cike dam da faranti.

"Kin ga matar gidannan? Ki fita daga harkar ta. Duk abinda take yi kanta take ma. Ro?o na gare ki don Allah don Annabi ki lallaSa ki kawar da kai kamar yadda Yayyenki suka yi a kanta har mu koma can inda muka fi wayau ba tare da mun janyo ma kanmu abin magana ba. Ko so kike a fara ya-maWiWi da mu a jakar magori ana cewa Uwar miji da ?anwar miji sun zo daga ?auye sun zama sanadiyyar mutuwar aure?"

"To ayi mana Innaye. Wa yake tsoron a mutu? Saboda Allah irin abubuwan da matar gidannan take yi mana ita tana kyautawa kenan? Ki duba fa yadda take Waukarmu a wula?ance. Shi Yaya haka yake ma Iyayenta da ?an'uwanta? Innaye ko kin san har yau ban kai matsayin da matar nan za ta dinga kiran sunana kai tsaye ba sai dai ta ce min Ke jahila, ko ke ba?auyiya, ko ke dabba? Saboda Allah Innaye don Allah yasa an haife ta a cikin babban birni Abuja ni an haife ni a ?auyen-?ayau Fa?o sai ta dinga tozarta ni tana wula?anta ni? Na rantse da Allah idan su Aunty Rakiya sunyi ha?uri da ita ni kam bazanyi ba, daga yanzu bazan sake Waga mata ?afa ba. Tunda dai ita ba ta da mutunci. Sai dai duk abinda zai faru ya faru."
Ta ?arasa maganar idanunta ciccike da hawaye na gaske ba na taSara ba kamar yadda take yi a mafiyawancin lokuta. Gefen hijabin jikinta ta kama ta fara sharar ?wallah, da alamun tozartata da Bintu take yawan yi ya daWe yana ci mata tuwo a ?warya.

Ita kuwa Innaye shiru tayi, ta rasa ta cewa. Zuciyarta cunkushe da matsanancin damuwa, domin sai a yanzu da ta ?ara karantar halayen Bintu duk wasu maganganu da ?a?anta suka sha faWa na ?orafi a baya ke dawo mata daki-daki a cikin zuciyarta. Kamar dai a lokacin abubuwan suke faruwa.

Da?yar ta iya yakice tunanin da take yi ta fara rarrashin Zulaikha da hawaye suka kasa tsayawa a idanunta, tana sharce wasu suna sake gangarowa.

Duk ?amshi da kyawun abincin a idanun Zulaikha ta kasa yi mishi mugun ci kamar yadda ta ?udurtawa zuciyarta da farko. Daga ita har Innaye tsakuran abincin suka yi. Da gangar ta ?i mayar da kulolin ko bayan sun gama cin abincin.

"Ko na mayar ma ba ci za suyi ba. Wata ?ila zubarwa za tayi saboda ?an ?auye sun Wiba sun rage. Da tayi wannan almubazzarancin kuwa gara mu ajiye da daddare mu ci, abinda ya rage da safe mu ?arasa cinyewa sai in mayar mata da kulolin da take ta sauke zafafan numfarfashi kamar za ta haWiyi zuciya a kansu."

"Ko da safen ma ai sai dai ke ki ci. Kin manta ta ce gobe za ta kaini asibiti da safe kafin in ci komai ayi min gwaji?"
Innaye ta faWa hankalinta na kan Zulaikha da take sakacen ha?orinta da tsinken-tsinyiya.

"Allah ya kaimu goben. Sai kiyi ?o?ari ki cika cikinki dam anjima da daddare, tunda goben bamu san iya wane lokaci za ki Wauka kafin ki karya ba. Ai wallahi gara dai a gama komai na asibitin nan a baki magunguna mu koma gida. Da birnin da komai na cikinsa Wallahi sun gundure ni, ?auyen nan dai da take yiwa kallon banza da ?yama ni shi ne abin alfaharina. A guri na ya fi Abuja sau miliyan Wari."
6)





Shi ba yaro bane. Ya san ya kamata ya tuhumi Bintu akan abubuwa da dama da take yi ma ?an'uwansa da mahaifiyarsa. Abubuwan da tun tana yi a fakaice ba ya lura, a yanzu gaba-gaWi take aikatawa ba tare da shakkar idanunshi ba. Kawai yana yi mata uzuri ne saboda dalilai mabanbanta da shi kaWai ya barwa zuciyarsa.

Marin da tayi ma Zulaikha ba abinda ya shafe shi bane, saboda ya san halinta kamar yunwar cikinsa. Ba Bintu da take matsayin matarsa ba, ko shi Zulai ta daWe tana shiga mishi hanci da ?udundune, aduk sa'adda yayi yun?urin fyatota sai Innaye ta taka mishi burki. Da wannan dalilin yasa ba ?aramin farin ciki yayi ba da Bintu ta tsinkawa Zulaikha mari, a ganinsa, hakan zai rage kaifin rainin yarinyar a gare shi da matarsa.

Amma duk da haka, ya san ya kamata yayi ma Bintu ?wa??waran tuhuma akan sakaci da abincin mahaifiyarsa. Ya kamata ya tuhume ta akan yadda ya faWa mata yana so mahaifiyarsa tayi watanni a gidan, amma ta?i yi ma Innaye dabarar cewa binciken lafiyarta zai Wauki lokaci mai tsawo. Ya kamata ya tuhume ta akan yadda ta nuna Sacin ranta don kawai ya Wauki kulolin abincinsa da abincin ciki ya kaiwa mahaifiyarsa... Tuhume-tuhumen suna da yawa, amma a yanzu dai, waWannan su ne abubuwan da suka faru akan gaSa. Saboda shi Win ba mutum ne da ya cika ri?e abubuwan da za su janyo mishi jin babu daWi a zuciyarsa ba.

Ko da ya shiga cikin falonsu, zuciyarsa cike take da niyyar zai yima Bintu waWancan tuhume-tuhumen. Amma yana yin tozali da ita zaune akan kujera tana sharar ?wallah. Sai yaji duk abinda ya ?ullo a ransa ya bi rariya da gudu ya wuce, babu abinda ke gaban idanunsa da zuciyarsa sai Bintu da damuwar da ya saka ta kuka. Wani abu da bai taSa gani ba tun da suka zama mallakin juna tsawon shekaru biyu.

"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!!! Sweetheart? Subhanallahi! Me ya faru? Wa ya rasu?"
Ya jera mata tambayoyin hankalinsa a tashe ainun. Da sassarfa ya ?arasa kusa da ita, sannan yasa hannuwa biyu ya tattagota zuwa jikinsa gaba Waya ya ru?un?ume yana sake jera mata tambayar me yake faruwa? Waye ya rasu? Domin duk a tsammaninsa rasuwa kaWai rasuwar ma na makusanci sosai shi zai sa Bintu zama tana risgar kuka.

Sai dai wani abu da ya sake Waga mai hankali zuwa ?ololuwar tashi duk irin maganganu da tambayoyin da yake mata bata amsa shi ba. Hallau kuma bata tsayar da kukan ba. A yadda yake ji, kamar ya Wora hannu biyu aka ya fara rusa ihu. Kawai sai ya fara tattaSa jikinta da tunanin ko ba ta da lafiya ne?

Yanayin jikin na ta daidai ne, babu zafi ko kaWan. Don haka ya kawar da tunanin ko rashin lafiya ke damunta. Can-cak ya Wauke ta kamar jaririya ya nufi cikin Wakinsa, ba tare da ya san taka-maimai abinda zaiyi mata ya tsayar da kukan da take yi kuma ya kore mata damuwar zuciyarta ba.

Kamar Wanyen ?wai sabon sakawa, haka ya ajiye ta sannu a hankali akan faffaWan gadonsa ?irar italiya da ya mamayi fiye da rabin Wakin. MaSallan rigar jikinsa ya fara cirewa sauri-sauri har ya zare rigar daga jikinsa. Kan gadon ya koma, jikinsa babu inda ba ya rawa ya sake tarairayota zuwa jikinsa, baiyi wata-wata ba ya haWe bakinsu waje guda, hannayensa biyu tallabe da fuskarta, ya saka idanunsa cikin nata yana aika mata da wasu zafafan sa?onni waWanda ita kaWai za ta iya fassarawa.

Tun tana mutsu-mutsun ?wacewa har ta bada kai bori ya hau. Tun hawayen suna sauka da gudu, har suka koma sauka sannu a hankali, daga bisani ma suka tsaya da zuba, sai ajiyar zuciya take saukewa akai-akai. Bai saki fuskarta ba sai da ya tabbatar jikinta ya mutu murus, sannan ya kwantar da kanta a ?irjinsa yana shafa yalwataccen gashin kanta da yake fitar da daddaWan ?amshi.
"Wa ya taSa min zuciyata?"

"Kai ne!"
Ta amsa mishi ba zato ba tsammani da wata siririyar murya mai Waukar hankali.

"Ni kuma? Me nayi?"
Ya sake jefa mata tambayoyin yana Wan ware idanunsa kaWan, alamun amsar na ta ya bashi mamaki ?warai da gaske.

A karo na barkatai ta sake jan nannauyar ajiyar zuciya ta sauke. Shiru tayi kamar baza ta amsa shi ba, a zuciyarta take ta jujjuya maganganun da za ta karanta mishi ba tare da ya zarge ta da ?yamar mahaifiyarsa ba.

"Ina jin ki Sweetheart! FaWa min laifin me nayi miki da har yasa kika zauna tsawon lokaci haka kina sharSan kuka. Abinda bai taSa faruwa ba a tarihin zamantakewar aurenmu. Abu Waya dai da nake so ki dinga tunawa ako da yaushe shi ne, Hafiz, mutum ne mai tsananin ?aunar matarsa Bintu. Da gangar bazai taSa yin abinda zai taSa zuciyarta ba. Kina sane da haka ko?"

A hankali ta Waga mishi kai alamar ta sani. Cire kanta tayi daga ?irjinsa, ta Waga fuskarta tana kallon tasa. Sannu a hankali ta saka idanunta da suka canja launi saboda kuka a cikin nasa idanun. Ta ri?o hannayensa biyu a cikin na ta, sannan ta buWe tsukakken bakinta a tausashe ta fara magana har lokacin bata cire idanunta a cikin nasa ba.
"A irin koyi da tarbiyar da Mummyna ta ba ni, ta nunar mini miji yana da ?ololuwar daraja a gurin matarsa fiye da komai da kowa a rayuwarta. Idan na ce komai kuwa ina nufin komai, cikin komai da kowa Win nan kuwa har da iyayenta. Kuma idan ba na manta ba har a addinance ma haka ne, right?"

"Haka ne Beby"
Ya amsa mata yana jin wani shau?i da girma na ?ara lulluSe zuciyarsa.

Ko kusa bai fahimci inda maganganunta suka dosa ba, don haka ya ?ara buWe kunnuwansa na basira yana sauraren inda za ta kai shi. Abu Waya dai da zai ?aras da maganganunta ba na zafi bane shi ne, yadda tun a saWarar farko na fara maganarta zuciyarsa ya ?ara cika da tumbatsa da alfaharin samun mace ta gari kuma mai tarbiya irin Bintu. Irin matar da hadithi ingantacce ya tabbatar duk namijin da ya same ta an bashi rabin addininsa, sai kuma ya ji tsoron Allah a sauran rabin.Ta sake Sata wasu da?i?u masu Wan dama tana ?ara tsara irin maganganun da za ta faWa masa, waWanda take da tabbacin za suyi kwanciyar girma da muhimmanci a zuciyarsa. Kuma zai ?ara yarda da gasken gaske ita Win fa mai son shi da ?aunarshi, muhimmanci da girman da yake da shi a gurinta yasa sam ba ta iya haWa al'amarinshi da na kowa.

"Ina jin ki Sweetheart"
Ya sake faWa a tausashe don dawo da ita daga duniyar tunanin da ya lura tana ?o?arin lulawa.
7)




Lumshe manyan idanunta tayi a hankali, can kuma sai ta buWe sannan ta saki wani nannauyan numfashi.
"A gidanmu, na taso na ga Mummy ba ta haWa al'amarin Daddy da na kowa. Al'amarin Daddy da duk wani abu da ya shafe sa ako da yaushe kuma ko wani lokaci yana kasancewa na musamman ne a gurinta.

Da irin wannan tarbiyar ta raine mu, wannan yana Waya daga cikin dalilin da yasa duk wani al'amari na ka yana da matu?ar muhimmanci a gurina. Amma na lura kamar dai kai ba na maka gwaninta, ba na burge ka, kamar ma ka raina yadda nake ?o?arin sauke nauyin hakkinka da Allah ya Wora min..."

Tayi Wan shiru tana mayar da numfashi a raunane. Ya buWe baki zaiyi magana da sauri ta girgiza mishi kai, ta ?ara da Wora yatsarta manuniya akan laSSansa.

Tayi mar-mar da ?wayoyin idanunta sai ga wasu siraran hawaye sun ziraro daga cikinsu.
"Don Allah Dear ka faWa min, ta ina ne nake kuskure maka? Zuciyata baza ta iya jurar ganin yadda nake tattalinka da ?o?arin faranta maka kai kuma kana gwasale ?o?arina ba. A tunanina, Sangaren iyaye daban na matarka daban! Duk mu biyun muna da girman ha??i a kanka. Me zai sa ka dinga ?o?arin nuna musu ni Win ba kowan kowa bace a gurinka?"
Ta ?arasa mishi da tambayar wani raunataccen kuka na ?wace mata. Kifa kanta tayi a ?irjinshi, ta cigaba da rera kukan da ya ?arasa kassara duk wani Wan sauran karsashi da ?warin gwuiwa da suka rage masa.

Ya nemi kalamai a bakinsa ya rasa Wif! Kamar Waukewar ruwan sama. Tsawon wasu da?i?u ya kasa ce mata komai, duk kuwa da yadda yake jin zafi sosai a zuciyarsa saboda yadda take rera kuka, kuma ya tabbatar wannan hawayen suna fita a dalilin wani abu na rashin kyautawa ne da shi da kanshi yayi mata.

Bayanta yake Wan bubbugawa sannu a hankali alamun rarrashi.
"Kiyi ha?uri."
Ya iya faWa da?yar bayan tsawon lokacin da ya Wauka yana kokawa da bakinsa kafin ya samu zarafin buWewa har kalmomi biyun suka fita.

Sun Wauki tsawon lokaci suna a haka, kafin daga bisani ya Wauketa can-cak a jikinsa ya nufi banWaki da ita. Ba yau ne karo na farko da ya fara yi mata wanka ya naWo ta kamar ?ar jaririya ba, don haka a yanzu Win ma bai sha wata wahala ba, haWin kai ta bashi Wari bisa Wari tun tana kukan har ta koma sauke ajiyar zuciya, duk inda yayi da ita haka take bin shi da ido har ya gama komai ya sake Waukarta ya mayar da ita gefen gado ya shimfeWeta. Lallausan bargo ya rufa mata a jikinta ya Wauki remot ya daidaita mata yanayin sanyin A.c, sannan shi ma ya shige banWaki da niyyar yin wanka, ko kafin ya fito, har wani nannauyan barci yayi awon gaba da ita.

Gefen gadon ya zauna, ya tsura mata idanu yana kallonta a tausashe. Kamar dai yau ne ya fara ganinta. Maganganun da ta gama rattaba masa ne yake sake bitarsu yana musu karatun dalla-dallah.

A iya hange da zurfin tunaninsa, bai ga ta inda ya kuskure mata ?arara a tsawon yininsu na yau da har ta kasa danne Sacin ranta ba sai akan sabbin kulolin nan da ya kwashi abincin ciki da yake mallakinsa ya kai ma mahaifiyarsa.

Daga shi har ita basu yini a gida ba balle wani abu na saSanin fahimta ya gifta a tsakaninsu. Ko da sun yini tare ma, samun saSani ko banbancin ra'ayi ba abu ne da ke yawan faruwa a tsakaninsu ba.

Soyayya da ?auna mai tafe da yarda tsaftatacciya suka gina a tsakaninsu tun kafin kasancewarsu ma'aurata. Bayan sun dun?ule ta hanyar zamowa abu guda ?ar?ashin inuwar aure kuma, musamman suka zauna suka sake sabunta sabbin tsare-tsare akan waWancan turaku uku da suke ri?e da igiyar soyayyarsu har ta kai su ga zama ma'aurata.

Da waWannan dalilan yasa sam ba sa faWa, saSanin fahimta kuwa zai iya ?ididdige sau nawa suka same ta a iya zamantakewarsu na shekaru biyu.

Da gaske kamar yadda ta faWa, Sangaren mahaifiyarsa daban tata a matsayin matarsa daban. Ya zama dole ya ?ara yin tsayuwar daka wajen ganin ya ba kowa a cikinsu ha??inta da Allah ya Wora mishi.

Zulaikha da yake kallonta da matsayin mai ?ara ma wuta fetur sannu a hankali zai bi da ita ya koya mata hankali cikin ruwan sanyi ba tare da Innaye ta zargi wani ba. Lallausan murmushi ya sakar ma Bintu da take barci, yasa hannu sannu a hankali ya shafi gefen fuskarta, sannan ya mi?e tsam daga gefen gadon.

Idanuwansa ne suka faWa kan Wan madaidaicin agogon da ke gefen gadon, ?arfe shida har da minti biyu na yamma. Gaf ake da kiran sallar magriba, banWakinsa ya koma ya Wauro alwala, bayan ya fito kuma sai ya nufi gaban madubi ya fara shafa mai. Cikin ?an?anin lokaci ya shirya cikin jallabiya ya fice daga Wakin zuwa falo.

Sai da idanunsa suka sauka akan teburin cin abinci sannan ya tuna a yinin yau gaba Waya bai ci wani ?wa??waran abinci ba. Kuma wani abin mamaki shi ne sam ba ya jin yunwa, bayan Wan tunani da yayi sai ya ala?anta hakan da rashin nutsuwar da ya samu bayan dawowarsa gidan.

"ShaiWaniya Zulai."
Ya faWa a fili. Sai kuma yayi ?wafa mai ?arfi ya ?ara da cewa
"Zanyi maganinki. Ke baki isa ki zo ki hargitsa min zaman lafiya da kwanciyar hankalin da na Wauki tsawon shekaru ina ginawa tsakanina da iyalina ba."
KaWa kai yayi yana cije laSSa ya fice daga gidan zuwa masallacin cikin layinsu da yaji an fara kiran sallar magriba.


***** *****


"Innaye sai kin dawo. Allah ya ?ara lafiya yasa mu ji alkhairi."
A karo na huWu Zulaikha ta sake faWin haka fuskarta a marairaice. Kamar za ta saka kuka.

"Amin Auta. To shi kuma Sata fuskar ta mece ce? Ca nake kina ji Fatima ta ce da an gama gwajin za ta saka a dawo da ni gida?"
Innaye tayi maganar da sigar rarrashi hannunta ri?e da na Zulaikha.

"Innaye..."

"Ke dallah ki rufe mana baki anan gurin sakarya kawai. Sallama da addu'ar sun isa haka, ko an faWa miki ke kaWai ce kika damu da lafiyarta?"
Hafiz ya katse maganar da tayi niyyar yi cikin wani irin gigitaccen tsawa da yasa babu shiri ta saki hannun Innaye, a Wimauce ta juya zuwa Sangaren da aka sauke su da saurin gaske kamar za ta kifa a ?asa.

Da kallo Innaye ta bi ta, sai kuma ta dawo da idanunta kan Hafiz ?arara take nuna mishi rashin jin daWin tsawar da yayi ma Zulaikha. Ta kasa daurewa, sai da ta ce
"Haba Hafizu. Saboda Allah menene aibun bankwana da kyakkyawar addu'ar..."

"Kiyi ha?uri Innaye. Kin ga fa tun Wazu Bintu take jiran fitowarki. Kamata yayi ace yau ?arfe bakwai na safe tana asibiti amma saboda ke kinga yanzu bakwai da rabi, kuma duk ba kowa ne ya janyo Sata lokacin ba sai Zulai. Yi ha?uri ki hau mota ku tafi, na san in Allah ya yarda

3 / 53