Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

DA ME AKE ADO Complete 1 4 Complete Hausa Novel by Aunty Fauziyya D Sulaiman

Author :  Aunty Fauziyya D Sulaiman Category :  African Stories & Novels

Chapter   20 / 47

57K to 60K   out of 139.6K words

ka kasance shege ba wani abu bane ba to ni kam ALLAH ya sani babbar matsala ce, ba zan so na haifi 'ya'ya adinga cewa"

ubansu shege ne maras asali ba. maganar mun gina soyayya kuwa daman can akan tubalin toka da karya

muka gina ta don lallai dana san kai shege ne da ban bata lokacina akanka ba. na soka ahmad ashe kai maras asali ne ka boye min ka cuce ni wallahi ka yaudare ni' sai ta fashe da kuka.

ahmad yaji duk ya tsani kansa da rayuwarsa tabbas ummi tayi gaskiya waye zai so hada zuri'a da shege

"maras asali. da an bashi zabi tun farko da yaso sun cika da mahaukaciyar mahaifiyarsa da yafi komai yi masa sauki da dadi. ina ma bai dandani wannan duniya mai cike da bakin ciki da takaici ba, bawayen da yake ta hadiyewa suka ci gaba da biyo kuncinsa, ya kasa cewa komai domin bashi da sauran abin fada"

din.

"ta kalleshi afusace tace 'idan abinda ya kawo ka kenan ni zan koma domin ina da abin yi agida, kuma"

wallahi dana san kaine ma ba zan fito ba' ta juya da azama tana fadin 'sai anjima ba kuma na fatan zaka kara zuwa kofar gidanmu don ko ka zo ba zan fito ba'

"yayi dum yana kallonta da tsananin damuwa da tashin hankali, ji yake kamar ya bita ya kamota. shi"

"kenan ummi tayi masa nisa bayan ita wace zata iya auransa kuma yanzu? ya dinga kallonta har ta kulewa ganinsa, zuciyarshi taci gaba da tafasa da daukar zafi, yana jin kamar kamar zata faso kirjinsa ne tayo waje, ya tabbatar daga yau ya rasa ummi masoyiyarsa abar sonsa."

*

*

*

to malam ahmad IDAN SO CUTA NE HAKURI MAGANI NE

DA ME AKE ADO?

15

Aunty Fauziyya D Sulaiman

(Matar Bello Q for Q)

Typing

ALBISHIR NOVELS

Whatsapp number 08163840712

Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu.

"Haka ahmad ya juya gida bai san yadda aka yi yaje ba, yasan dai kawai ALLAH ne ya kai shi, ya kulle kansa"

a daki ya dinga kuka ya dauko hoton mahaifiyarsa da aka dauka sanda take mace a police station ya kura

"masa ido, dama tum sanda ya dawo ya laluboshi cikin kayan ummansa don ya kula ba zata bashi ba, y kurawa hoton ido cikin kuka yana fadin."

"'don ALLAH innata waye babana waye yayi miki cikina, me ya sanya baki haye kaina ba bayan kin haife ni,"

"kika mutu kika barni, dama kin ci gaba da rayuwa da na yi ta miki magana har ki warke ki fada min"

"asalina, tabbas ba don kada na mutu na tabbatar da azabar ALLAH akaina ba dana kashe kaina na huta' haka nan ya dinga kuka cike da tashin hankali."

a cikin gida ma duk wanda aka sanar da shi abinda ya faru cikin yan uwansa sai hankalinsa ya tashi

"abinda suke tambaya shin uban waye yaje ya fadi wannan magana, duk yadda suka so ganin ahmad su lallasheshi abin ya citira tunda ya garkame kansa a cikin daki."

"malam sulaiman kam ya jima akan dakali yana tunanin mafita, har zuwa lokacin da ya cimma tunanin"

"nasa, ya sanya yaro ya kira masa dan uwansa malam jibril. ba da jimawa ba ya fito ya zauna kusa da yayansa yace 'malam gani naji ance kana kirana' ya kalle shi tsahon lokaci sannan yace 'kaji abinda ya faru da ahmad kuwa?"

"da sauri yace 'naji wallahi dazu dana shiga gida lami take sanar dani abin kam bai yi dadi ba sam, ALLAH"

ya bashi wata daman ina shirin da safe na shiga nayi muku jaje' malam sulaiman ya nisa yace 'tunda abinnan ya faru nake tunani mafita har ALLAH ya sanya tunanina ya fado kan diyarka raliya' da hanzari

ya dube shi yace 'raliya kuma malam?

ya gyada kai yana fadin 'ita kuwa kamar yanada ka sani ni ma na sank raliya ta zama gagararriya. wacce

"duk wani kokari namu dana 'yan uwanta ya gagara gyara ta sai dai addu'a gashi tayi girman da ya dace ace ta fidda miji amman an rasa wanda zai fito da gaske yace yana sonta saboda sanya shashanci da tayi a gabanta, hakan yasa nake ganin abune mawuyaci raliya ta samu miji nutsattse. don haka tunanina ya sanar da ni tunda anyi haka a maida ranar ahmad kanta, kada a canza.komai ayi nan da wata gudan"

amma kai yaya ka gani domin ka fini hakki akan raliya jibrilu?

yayi shiru tsahon lokaci yana nazari can ya daga kai ya kalli yayan nasa yace'yaya duk abinda ka yanke

"yayi saidai kana ganin shi ahmadun bashi da wata illa da zata yiwa rayuwar raliya illa? malam sulaiman ya kalle shi da sauri yace 'kada kace min kana cikin mutane masu jahilci da kama wani da laifin wasu, WALLAHI ba gori zan yiwa kaina ba ahmadh yafi duk 'ya'yan da muka haifa nagarta balle raliya da kai kanka kasan irin abubuwan kunyar data daukowan gidan nan, auren nasu shi zai zama rufin asiri agare"

mu baki daya'

malam jibril ya girgiza kai yana fadin 'wannan haka yake. to ALLAH ya sanya hakan shine alkhari. saidai

"yaya ka san fa bani da karfi ban tanadi komai na auren raliya ba, bani da kuma da hanyar da zan iya lalubo kudin da zan yi cikin wannan lokacin' malam sulaiman yayi murmushi cike da jin dadi yace 'amincewarka tafi komai agare ni, kuma koda hakan bata faru ba kayan dakin raliya daman akaina suke tunda dai nine waliyinta balle kuma haka ta kasance, kaidai na gode da wannan amincewar da kayi' don"

haka suka rabu ran malam ya haskake ya san yana da damar kara kyautatawa ahmad da mai dakinsa.

"a daki ya tadda umma tanata lazimi da alama addu'a take yiwa danta, ya sami guri ya zauna yana"

murmushi yace 'ALLAH dai ya amsa addu'arki sai ki kwanta kuma ki soma bacci' umma ta dube shi da

mamami fuskarta babu yabo ba fallasa tace 'malam kenan. kana zaton hankulanmu zasu kwanta cikin sauki kuma cikin wannan kankanin lokacin?

ya kura mata ido yana karantar yanayinta yace 'amma ai tunda abun nan yafaru ALLAH muke gayawa ba

kya zaton zai kawo mana mafita cikin gaggawa' tayi saurin yadda da batunsa har daga fuskarta ya fahimci hakan ta hanyar yin murmushinta tana fadin 'duk abinda aka ce ALLAH magana ta kare tabbas na yadda da batunka amman taimake ni sanar da ni wannan abin dadin'

yayi dariya yana kokarin tattaro farin cikinsa su yi rabonshi tare yace 'danki dai ya sami matar aure kuma

"a wannan ranar dai za a yi ba fashi' ta kalle shi da tsananin murna da mamaki wacce ta gaza boyuwa akan fuskarta tace 'na jima ban ji labari mai dadin wannan ba, alhamdulillah don ALLAH malam wace ta"

sadaukar da kanta da farin cikinta ga ahmad haka cikin sauri?

yayi dariya 'shi lamarin ALLAH haka yake a yanzu muka rabu da dan uwana ya amince da baiwa ahmad

"auren diyarsa raliya kinga asiri ya rufu ko? gabadaya annurin fuskarta ya dauke 'yan sakwanni, takaici da jimami ya mamaye fuskarta har malam sulaiman ya fahimta cikin mamaki yace 'naga kamar bakiyi"

"farinciki da jin wannan labarin ba, wanda nayi zaton ke zai fi yiwa dadi fiye da kowa'"

"tayi yake tana fadin 'tabbas abin farin ciki ne, amman kana ganin idan muka yi wannan hadin mun yi"

adalci malam? yarinyar nan ta gama yawo a kwararo gurin bin maza har ana raderadin anyi mata ciki sun

"zubar shi kuwa ahmad yaro ne nutsattse da bai taba gauraya rayuwarsa da shedana ba, sai nake ganin kamar tafiyar ba zata zo daya ba halin zai zama gambiza'"

"'duk wannan tunanin saida nayi kafin kiyi, amma ki tuna ahmad yana da wani fenti wanda duk kyan"

"halayyarsa al'ummarmu ta hausawa basa yafiya a kansa, idan har ba raliyar ba zai jima bai sami macen aure ba tunda aka fara da haka kin san komai zai iya faruwa a gaba ko fiye da wanda ya faru a baya ma, don haka a ganina auren raliyar shine rufin asirinsa da namu, ki sani duk abinda mace take tana da rangwamen ra'ayi idan ya aure ta zai ita sauya mata ra'ayi zuwa irin wanda yakeso, ki yi kokarin sanya"

albarka kawai'

"dogon bayanin mijin nata ya ratsa ta matuka, har ya sanya ta amince da kudirin nasa, cikin sanyin murya"

"tace 'ALLAH ya sanya haka shi yafi alkhairi. ALLAH ya basu zaman lafiya da zuri'a dayyiba amin' farin ciki ya cika malam yace 'yauwa abinda ya dace ki fada kenan umman ahmad' tayi dariya cike da jin dadi da kunya saidai acan kasan ranta ALLAH ya sani bata son wannan hadin, amman ba zata ja da ikon ALLAH"

"ba, zatayi ta addu'a watakila wata rana zata wayi gari taji tana son auren."

"acan gidan su lami rikici ne ya barke sanda mijinta ya sanar da ita abinda yake faruwa, tayi tsalle ta dire"

"tace 'wallahi wannan ba abune da zai taba yiwuwa ba, yaron shege dan mahaukaciya da ba a san asalinsa ba wanda bashi da abin ado za a baiwa diyar tawa gaskiya ban yadda ba sam' malam jibril yayi kasake yana kallonta tabbas shi ma irin ra'ayintane ra'ayinsa, saidai yana tsoro da shakkar ja da yayan nasa don haka ya tattaro dauriya ya hade fuska yace 'kinga lami wannan fa wani hukunci ne da muka"

riga muka zartar ni da dan uwana ba wai neman sbawara nazo gurinki ba'

ta kalle shi da tsananin mamaki tace 'amman mafi kowa sanin yaron nan shegene mahaumaciya ce ta

haifeshi a soron gidannan ko? sannan kuma duk inda yaje neman ba a bashi ko?

malam jibril kada kai yana fadin 'duk nasan da wannan amman ki tuna idan shi shegene to raliya ma tayo

"cikin shegen wanda ALLAH ya taimaka muka zubar dashi, idan kuma har ba wannan damar ba babu sauran wata dama da zamu iya katangeta ko hanata yin wani shegen, kin manta tsahon shekarunta kuma har yau babu wanda yazo da zimmar aurenta na gaskiya saidai abokan iskancinta, ni kam ina ganin wannan ce kadai damar da zamuyi amfani da ita gurin maganin matsalar raliya, kada ki manta tana da kanne mata wadanda muddin suka kara girma suka ga abinda take yi babu abinda zai hanasubin sahunfa su ma' ta kuma hasala matuka 'kawai kace min an zugoka ka tsani 'ya'yanka malam banda haka ta yaya"

zama hada darajar raliya da shege maras dangi. duk lalacewar biyu ai tafi daya wallahi'

banko kofar dakin raliya da shigowarta babu ko sallamane ya katse su daga doguwar tattaunawar da

"suke yi mai zafi. raliya ta kalle su far da idonta sai ta kada kai ta nufi cikin uwardaki ba tare da cewa kowa komai ba, malam jibril ya doka mata tsawa yana kallon agogo yana fadin 'ke raliya daga ina kike sai yanzu kika dawo gida a matsayinki na mace yanzu fa karfe sha daya da rabi nadare' raliya ta juyo a tsaye"

kerere tana kallon mahaifin nata tace 'baba daga zance nake fa'

'zancen ubanki' ya katseta da zafin rai 'duk diya tagari idan goma ta wuce ta kammala zance amman ke

"kikai wannan lokacin baki dawo gida ba, ai ta kusa yin kai ALLAH ya kusa raba yari da barawo, ki sani saura sati guda a daura aurenki na gaji da wannan mugun halin naki' ta kalli mahaifin nata a tsorace tace 'baba aure fa naji kace zaka min nan da sati guda, da wa kuma? sai da ya fara galla mata harara sannan yace 'da ahmadu na gidan nan tunda kin ki fitar da miji kin zauna kina watsewa gwara na aurar dake na"

huta da abin kunyar da kike ja mini'

"kayan dake hannunta ledoji guda biyu suka zube a kasa wanda da alama kayan dadi ne wani ya sai mata,"

"ta dafe kirji gami da kwalalo idanuwa waje tana fadin 'baba ka ji abjnda bakinka yace kuwa, ahmad na gidannan fa ko ka manta shege ne bayan yana matsayin shege mutum mugu azzalumi da baya kaunarmu, anya kuwa baba kaine kake fadin wannan kalamin da bakinka?"

mikewar da yayi a zabure ya kai mata duka ce ta katse ta daga doguwar rshin kunyar da take masa saidai

"tsallan da ta doka tayi gefe da kuma shiga tsakani da lami tayi ne ya hana duka usa ga raliya, ta koma gefe ta fasa ihu kamar wacce aka yiwa shegen duka."

"lami cikin fushi tace 'wallahi ba zaka dokar min diya akan wani shege ba, wanda tunda yazo gidannan"

"dukkan albarkar dake gidan aka dauke ta ba, tun bayan bayyanarsa agidan nan banga komai na alheriba sai bakinciki, yaron da saboda shi har saida aurena ya mutu, ka tabbatar ba ita kadai ke ja da auren ba har da nima bana kaunar wannan auren kuma in dai ina raye wallahi ba za a yi shi ba' malam jibrul yana huci ya kalleta yace 'wallahi karya kike yi ni kuma nace sai anyi shi idan kuma kin ga ba a yishi ba wallahi.saidai ko ni ko raliya wani ya mutu mu zuba ni da ke' ya juya ya fice daga dakin yana huci ransa a"

bace matuka.

raliya ta kuma sanya ihu tana fadin 'na rantse da ALLAH wallahi ko baba zai kashe ni ba zan yadda na auri

wannan shegen mutumin ba. haka kawai saida ya nemi auren wata aka gano shege ne aka hanashi

"sannan ya dawo kaina, me zanci dashi bashi da komai sai tsananin fatara da talauci da suka isheshi, mutumin da bai wuce zama dan wankin gidana ba'"

lami ta dafa kafadarta 'kwantar da hankalinki muddin ina raye babu wanda ya isa yayi miki auren dole

koda hakan yana nufin komai kuwa' da wannan ta samu ta rarrashi diyar tata har ta kwantar da

"hankalinta, suka zauna suka kama cin kayan dadin da ta shigo musu da shi, wanda ta saba kawowa kusan dul dare."

"shi kam ahmad bawan ALLAH bai san wainar da ake toyawa ba, yana can shagonsa cikin tsananin bakin"

"ciki saidai daga baya zuciyarshi ta bashi shawara sanar da ALLAH halin dayake ciki domin shine kadai zai kawo masa mafita, don haka ya fito kofar shagon nashi cikin dare ya daura alwala ya koma ya fara sallah."

*

*

*

haka ake so malam ahmad saboda na tare da ALLAH baya tabewa.DA ME AKE ADO?

15

Aunty Fauziyya D Sulaiman

(Matar Bello Q for Q)

Typing

ALBISHIR NOVELS

Whatsapp number 08163840712

Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu.

"Haka ahmad ya juya gida bai san yadda aka yi yaje ba, yasan dai kawai ALLAH ne ya kai shi, ya kulle kansa"

a daki ya dinga kuka ya dauko hoton mahaifiyarsa da aka dauka sanda take mace a police station ya kura

"masa ido, dama tum sanda ya dawo ya laluboshi cikin kayan ummansa don ya kula ba zata bashi ba, y kurawa hoton ido cikin kuka yana fadin."

"'don ALLAH innata waye babana waye yayi miki cikina, me ya sanya baki haye kaina ba bayan kin haife ni,"

"kika mutu kika barni, dama kin ci gaba da rayuwa da na yi ta miki magana har ki warke ki fada min"

"asalina, tabbas ba don kada na mutu na tabbatar da azabar ALLAH akaina ba dana kashe kaina na huta' haka nan ya dinga kuka cike da tashin hankali."

a cikin gida ma duk wanda aka sanar da shi abinda ya faru cikin yan uwansa sai hankalinsa ya tashi

"abinda suke tambaya shin uban waye yaje ya fadi wannan magana, duk yadda suka so ganin ahmad su lallasheshi abin ya citira tunda ya garkame kansa a cikin daki."

"malam sulaiman kam ya jima akan dakali yana tunanin mafita, har zuwa lokacin da ya cimma tunanin"

"nasa, ya sanya yaro ya kira masa dan uwansa malam jibril. ba da jimawa ba ya fito ya zauna kusa da yayansa yace 'malam gani naji ance kana kirana' ya kalle shi tsahon lokaci sannan yace 'kaji abinda ya faru da ahmad kuwa?"

"da sauri yace 'naji wallahi dazu dana shiga gida lami take sanar dani abin kam bai yi dadi ba sam, ALLAH"

ya bashi wata daman ina shirin da safe na shiga nayi muku jaje' malam sulaiman ya nisa yace 'tunda abinnan ya faru nake tunani mafita har ALLAH ya sanya tunanina ya fado kan diyarka raliya' da hanzari

ya dube shi yace 'raliya kuma malam?

ya gyada kai yana fadin 'ita kuwa kamar yanada ka sani ni ma na sank raliya ta zama gagararriya. wacce

"duk wani kokari namu dana 'yan uwanta ya gagara gyara ta sai dai addu'a gashi tayi girman da ya dace ace ta fidda miji amman an rasa wanda zai fito da gaske yace yana sonta saboda sanya shashanci da tayi a gabanta, hakan yasa nake ganin abune mawuyaci raliya ta samu miji nutsattse. don haka tunanina ya sanar da ni tunda anyi haka a maida ranar ahmad kanta, kada a canza.komai ayi nan da wata gudan"

amma kai yaya ka gani domin ka fini hakki akan raliya jibrilu?

yayi shiru tsahon lokaci yana nazari can ya daga kai ya kalli yayan nasa yace'yaya duk abinda ka yanke

"yayi saidai kana ganin shi ahmadun bashi da wata illa da zata yiwa rayuwar raliya illa? malam sulaiman ya kalle shi da sauri yace 'kada kace min kana cikin mutane masu jahilci da kama wani da laifin wasu, WALLAHI ba gori zan yiwa kaina ba ahmadh yafi duk 'ya'yan da muka haifa nagarta balle raliya da kai kanka kasan irin abubuwan kunyar data daukowan gidan nan, auren nasu shi zai zama rufin asiri agare"

mu baki daya'

malam jibril ya girgiza kai yana fadin 'wannan haka yake. to ALLAH ya sanya hakan shine alkhari. saidai

"yaya ka san fa bani da karfi ban tanadi komai na auren raliya ba, bani da kuma da hanyar da zan iya lalubo kudin da zan yi cikin wannan lokacin' malam sulaiman yayi murmushi cike da jin dadi yace 'amincewarka tafi komai agare ni, kuma koda hakan bata faru ba kayan dakin raliya daman akaina suke tunda dai nine waliyinta balle kuma haka ta kasance, kaidai na gode da wannan amincewar da kayi' don"

haka suka rabu ran malam ya haskake ya san yana da damar kara kyautatawa ahmad da mai dakinsa.

"a daki ya tadda umma tanata lazimi da alama addu'a take yiwa danta, ya sami guri ya zauna yana"

murmushi yace 'ALLAH dai ya amsa addu'arki sai ki kwanta kuma ki soma bacci' umma ta dube shi da

mamami fuskarta babu yabo ba fallasa tace 'malam kenan. kana zaton hankulanmu zasu kwanta cikin sauki kuma cikin wannan kankanin lokacin?

ya kura mata ido yana karantar yanayinta yace 'amma ai tunda abun nan yafaru ALLAH muke gayawa ba

kya zaton zai kawo mana mafita cikin gaggawa' tayi

20 / 47