Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

DA ME AKE ADO Complete 1 4 Complete Hausa Novel by Aunty Fauziyya D Sulaiman

Author :  Aunty Fauziyya D Sulaiman Category :  African Stories & Novels

Chapter   15 / 47

42K to 45K   out of 139.6K words

irin halin da nana ta shiga, idonta yayi jawur hawaye ne kawai ke zuba daga cikinsa.

Ko da ya isa ofis kasa komai yayi sai tunanin halin da nana ke ciki da ace zai iya taimakonta da yayi, amman bazai iya bari rayuwar nana ta lalace ba dole zai san abin yi. Kwanaki hudu tana cikin asibitin amma babu sauki sai abinda ke karuwa, musamman hawan jininta gashi anyi anyi ta fadi abinda ke damunta ta ki sai kuka. Shi kansa Ahmad tun zuwansa na farko ya kasa kara komawa, don bai son ganin nana cikin halin da ya san bazai iya taimakonta ba. Bayan kwana uku Abangaren nana dai hankalin iyayenta atashe yake kullum yau kam Alhaji nura kwangila ya tabbatarwa kansa da sai yasan abinda ke haddasawa diyarsa wannan halin da take ciki, don suna jin kukan da take kusan kwana tanayi indai ba,ayi mata allurar barci ba. Tana zaune atsakiyar gado tana shan ice-cream ya taso daga inda yake ya dawo kusa da ita ya zauna agefen hadadden gadon dake kama dana gidan wani hamshakin sarki don ya sha gyara. Cikin sanyin murya Alh nura ya kirawo sunanta ta dago kai ta kalleshi gabanta yana faduwa ta amsa. Ya sake kwantar da murya yace nana ki taimakeni ki sanar dani gaskiyar abinda ke damun ranki? Nana ki tuna bani da kowacce diya a duniya sai ke, ke kadai Allah ya bani dan uwana guda daya ne yana kwance cikin jinya ke kadai nake kallo adangina kuma yata, idan kika bari na rasaki bazan yafe miki ba, don babu makawa nima karshen rayuwata yazo...... Yayi dan shiru yana kare mata kallo sannan ya cigaba Nana ki taimaka ki sanar dani abinda ke damunki, ina da kudin da zan siyo miki dukkan abinda kike bukata awannan duniyar, idan kuma ya fi karfin siya zan tayaki da addu,a Allah ya baki shi ko kuma ya sanya sanyi da salama azuciyarki ki fadamin abinda ke damunki nana.. Nana ta sunkuyar da kanta kasa hawaye na zubowa daga idonta tace. Daddy idan na gaya muku abinda ke damun zuciyata zakuji haushina da abin watakila hakan ma ya sanya ku daina tausayamin. Injiwa yagamiki? Dukkan abin da zai sanya ki cuta irin wannan ya wuce mu d'aukeshi k'arami. Ki gaya min Nana ko kin manta nine Daddy d'inki da kike gayawa dukkan damuwarki?" Ta d'ago kai ta kalleshi kamar ba za ta fad'a ba, sai ta ce, "Daddy tun randa na yiwa Ahmad wulak'anci a Gidan mai na fara kamuwa da sonsa, nayi zoto wasa ne ko zan rabu da son a hankali, amma sai abin ya cigaba da hauhawa, cikin raina har ta kai na zamto bani da buri bayan ganinsa kullum, don haka kullum sai naje Gidan Man su, daga baya nayi hanyar da ya sami aiki kusa dani, wannan ya sanya na sami sanyi cikin raina, ban ta6a zaton idan na bayyanawa Ahmad buk'atata zai juya mini baya ba, sai dai na gano halin Ahmad bai sanya akan komai don na gwada masa dukkan abin da zai sanya ya gane ina k'aunarsa amma ya kauda kansa, daga k'arshe da naga sonsa yana neman hallakani ya sanya na sanar da shi amma sai ya gaya mini bai sona bai kuma ta6a sona ba....." Ta fashe da kuka maganar ta kasa ciga da fitowa. Hajiya batula da Alhaji nura kwangila suka bita da kallo da tausayawa basu taba zaton abinda ke damun yarsu kenan ba. Wato hakan na nuna musu ta warke daga cutar dake damunta tun tana da kuruciyarta, wacce suka kashe makuden kudade gurin ganin sun samar mata lafiya. Alhaji nura kwangila ya riko hannunta ya dora kanta akan kafadarsa yace. kwantar da hankalinki diyata nasan illar da soyayya ke yiwa zuciyar dan adam dan ta taba illata rayuwata amma indai akan Ahmad ne kukan ki ya kare da damuwa zan samar miki shi da ikon Allah. Ya mike da sauri yanzu zanje gareshi insha Allahu damuwarki sun kare. Idon nana na zubar da hawaye tana kallon baban nata daya nufi kofa kai tsaye zai fita cikin sanyin murya tace. Daddy don Allah idan yaki yarda kada kace zaka koreshi daga aiki, ganinshi kadai abin jin dadi ne agurina kada ayi masa dole akan sai ya soni. Alhaji nura kwangila yayi shiru bai juyo ba amma tabbas maganar diyar tashi ta shigeshi tausayinta ya kara kamashi ashe akwai wani abu da diyarsa zata iya rasawa awannan duniyar yana raye? Lallai iko yana gurin ubangiji ya kada kansa ya fice. Hajiya batula ta matsa kusa da nana don rarrashinta. Ahmad yana zaune a ofis wayarsa ta fara kira ya dago da sauri ya na kallon screen din wayar lambar Alhaji nura kwangila ya gani gabansa ya fadi amma dai dole ya daga, yana shirin gaida Alh nura sai ya katseshi da cewa kana ofis ne Ahmad? Da hanzari Ahmad yace ina nan Alh. Alhaji nura kwangila, ok to ganinan zuwa. Gaba daya hankalin Ahmad ya gama tashi ji yake kamar ya gudu kada Alhajin ya sameshi amma babu halin yin hakan dole ya zauna ya jira zuwanshi. Lokacin da Alh nura kwangila ya turo kofa ya shigo Ahmad ji yayi kamar akan kirjinsa aka mako kofar saboda wani bugu da yaji kijinsa nayi. Da sauri Ahmad ya mike tsaye yana wa.



12 October 2015 at 13:56 · Public

Save · More

Like

React

Comment

Share

Like27

Write a comment...



·

Hauwa Muhammad

Friends y Kke d ftn kowa Lfy dn Allah angama tattalin so ne wlh baba na ne y rasu bana Hawa online ngde

Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015

Jamila Umar Tanko BooksJamila Umar Tanko Books

Allah ya jikansa da rahama, mu kuma intamu tazo... More

Al-Rayyan... replied · See all 4 replies

Sumayya Nasir Abdullahi

mungode acigaba

Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015

Dahir Uthman

Tend

Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015

Khadijah Aliyu

Tnx

Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015

Al'amin Khalid Sulaiman

Mungode, Dan Allah acigaba Dakyau,

Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015

Usman Aliyu Taller

Muna godiya

Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015

Nafisa Danladi Danladi

Allah jikan sa.ya.jikan iyaye mu ,ya jikan alumar musulmi

Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015

Abban Husnat replied · 1 reply

Bakoji Lamara Misau

Gud

Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015

Ahmad Sabo

Dai dai kenan!

Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015

Hauwa Muhammad

Ameen nagode sosai

Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015

View more comments&

Free Mode See Photos

Facebook logo

Go To Home

Jamila Umar Tanko Books

DAME AKE ADO...4**11



Gaba daya hankalin Ahmad ya gama tashi ji yake kamar ya gudu kada Alhajin ya sameshi amma babu halin yin hakan dole ya zauna ya jira zuwanshi. Lokacin da Alh nura kwangila ya turo kofa ya shigo Ahmad ji yayi kamar akan kirjinsa aka mako kofar saboda wani bugu da yaji kijinsa nayi. Da sauri Ahmad ya mike tsaye yana wa Alhaji sannu da zuwa. Alhaji Nura ya dubeshi yana murmushin yak'e yace, Zauna Ahmad inason yin magana dakai ne, kuma magana ce mai mutuk'ar muhimmanci a garemu. Ahmad ya koma ya zauna cikin sanuyin jiki, gabansa na dukan d'ari- d'ari. Alhaji Nura ya janyo Kujera dake fuskantar wandda Ahmad ke kai azaune shima ya zauna ya tsare Ahmad da ido yana fad'in, Ba sai naji komai daga bakinka ba na san Nana ba ta yin k'arya, ko yaudara, abinda na ke fata daga gareka kawai shi ne ka amince Ahmad, bani da Kud'i ko ikon da zaniya siyan soyayya, domin da zan iya da tuntuni na siyuwa wani soyayyar Nana na aurar daita. Tunda Nana ta taso ta k'i jinin kula Saurayi har zuwa girmanta, hakan ya jagoranci tunaninmu da kuma fad'hn wasu Malamai cewar wai aljani bak'i ne ya aureta, yanzu kuma sai gashi allah ya kawo mana maganin abin rana d'aya, nana ta furta da bakinta cewa tana sonka Ahmad. Ahmad kayi duba da kyau ga wannan lamari, nana yarinya ce mai kyau da tsari kamar nana ace ta tunkari namiji tace masa tana sonshi ka san ba k'aramin abu bane,

Kamar nana ace ta tunkari namiji tace tana sonshi ba karamin abu bane, ka taimakeni Ahmad ka auri nana don Allah. Ahmad kansa yana kasa tunda alh nura kwangila ya fara magana, da ace akwai mutumin da zai iya yiwa wani abu ko da ranshi bai so ba to bai wuce Alh nura ba, amma bazai iya yiwa ma,un shi kishiya ba dan yiwa ma,u kishiya kamar yiwa ummansa ne, mutanen da suka raineshi suka bashi mace yaya zai iya yi musu haka? Bashi da amsar da zai iya baiwa Alh nura kwangila dan haka ya dukar da kansa kawai. Alh nura kwangila ya zuba masa ido da mamaki sannan yace. Ahmad ko akwai wani abu da nana take wanda ranka bai bukata ko kuma tana da wata illah ne gaya mini don banyi zaton wani namiji zaiki diyata ba a wannan lokacin. Ahmad ya girgiza kai yana fadin, ko daya babu wani abinki dana gano a wajen nana amman..........Sai kuma yayi shiru ya sara ma mai zaice. Lallai Ahmad ka nunamin kai namijin duniya ne, hakan kuma ya sanya na kara yarda nana tayi zabi, don nayi imanin wani zai so nana ko don arzikinta ko kyanta ko dan nasabarta amma ko daya bai burgeka ba daga cikin wadannan abubuwan. Ahmad ya kada kai tunda nake ban taba sanya kwadayin abun kowa araina ba na wadata da abinda nake samu, amma kayi hakuri Alhaji ina cikin halin da ba zan iya aurar wata ba. Alhaji nura kwangila ya sake kallon Ahmad da tsananin mamakin karfin halinsa amma hakan kara birgeshi yake da kuma nuna masa shine mijin daya dace da diyarsa nana.Cikin kwantar da murya yanzu Alh nura kwangila ya cigaba da magana. Yanzu kam alfarma nake nema ka dubi halin da nana take ciki, bani da kowacce diya sai ita kadai zan iya rasata saboda sonka ka ceci rai Ahmad, ka ceci rayuwarta daga cikin bakin cikin dake damunta. Jikin Ahmad yayi sanyi lallai yakamata yayi wani abun akai, amma kuka bazai iyayin abun kai tsaye ba don haka yace da Alh nura Alhaji ka bani dan wani lokaci zan yi shawara tukunna. Ran Alhaji nura yayi dan sanyi , ko ba komai ya samu magana mai dadi amma cikin ransa mamaki da tu,ajjibi ne ke cikashi yau kuma haka Allah ya kaddara masa kamar shi ya buge da rokon wani akan wani abu da bai da iko akansa, bayan da shi kullum ake roko. Wannan kadan kenan daga ikon Allah. Alhaji nura kwangila ya girgiza kai ya mike yana fadin. Hakan ma yayi, amma bazan baka dogon lokaci ba gobe kamar wannan lokacin zan dawo dan jin shawarar daka yanke nagode. Alh nura ya juya ya fice, Ahmad ya bishi da kallo da fargaba da tsoron abinda zai biyo baya. Yau kam ransa asake ya isa gida, halin daya ga ma,un ya kara sanya ransa yin dadi, ita da yayansa suna cikin kyakkyawar shiga gwanin sha,awa. Ma,u ta mike ta taroshi da jin dadin yadda ta ganshi cikin farin ciki, ya mannata akirjinsa yana sumbatarta suna dariya, tayi masa duk abinda ta saba yi masa suka wuce daki. Yau suna cikin farin ciki gurin cin abinci take bashi labarin zuwan amina gidan dayake tayi aure shekaru hudu da suka wuce, Allah ya hadata da wani dan kasuwa akantin kwari da yayi mata karyar shi mai kudi ne yana da katon gida da mota. Akayi aure sai gashi ta kare a daki falle biyu a gidan, hakanan ta tarar zaman da zatayi ita da kishiya ne da kuma tarin yaya guda shida tayi kuka da bakin ciki amma ba ta da zabi bayan zaman auren. Malam sulaiman shi yayi komai na auren nata tare aka hada da musa wanda yanzu yake zaune a gidan Ahmad daya bashi aro saboda yawon haya ya ishesu, kuma tunda taje gidan mijin Allah ya jarrabeta da haihuwa ga babu don kuwa karya yayi irin mutanen nan ne yan kayi nayi masu tsayawa abakin hanya,



13 October 2015 at 15:22 · Public

Save · More

Like

React

Comment

Share

Like27

Write a comment...



·

Salisu M. Mu'azu Dankado

Gud

Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015

Hajaru Sani

tnx alot

Like · React · Reply · More · 25 Feb 2017

Hauwa Muhammad

Aunty j muna gdia

Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015

Hajaru Sani

tnx alot

Like · React · Reply · More · 25 Feb 2017

Abubakar Ibrahim

Tnx

Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015

Aisha Ahmad Dayyab

Thanks

Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015

Hauwa Abdullahi

Godiya muke

Like · React · Reply · More · 25 Feb 2017

Usman Aliyu Taller

Thanks

1 · Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015

Firdaus Feedy Paradise

Plz aci gaba mana

Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015

Umar Abdulkadir Múwadda Malik

good but typing erro

Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015

View more comments&

Free Mode See Photos

Facebook logo

Go To Home

Jamila Umar Tanko Books

DAME AKE ADO 4**12



mutanen nan ne yan kayi nayi masu tsayawa abakin hanya, wadanda suke tsayawa idan mutum zaiyi siyayya su nuna masa shago wataran ma sai aje a wuni ba,a samo komai ba, ga iyayenta suma babu ta ko,ina su abarsu suji da hidimar diyar dake gabansu wacce suke kiranta da yar raliya saboda ba,ayi mata radin suna ba balle ragon suna ko wani abu. wannan kadai ya zamewa lami ishara. Sai da yakai loma bakinsa sannan ya kalleta yace ina jinki ma,u, yaya tazo nan gidan kuma ita da tace har abada babu ita babu mu? Ma,u tayi murmushi tace bari kaidai yaya yunwa da bala,i ne suka isheta taje can gidansu babu shine tayo nan tana zubar da hawaye da fadin na taimaka mata bayan ni babu mai bata cikin dangi tasan tayi abubuwa marasa kyau ita da mahaifiyarta garemu amma hannunka bai rubewa ka yanke ka yar don kwanansu biyu babu abinci sauran yan hayar gidan dama basa shiri sam da ita kishiyar sun hade mata kai don haka dole tayo nan. Kai bakaji zance ba sai kace ta sami tabin hankali. Kai talauci baiyi ba sam aduniya haka na harhada mata kayan abinci harda na sawa dana yara ta dinga kuka tana godiya. Duniya kenan. Ahmad ya gyada kai, kadan ma suka gani, duk wanda bazai iya kallon ikon Allah yayi shiru ba sai ya tofa tashi ko yayi kazafi akai ai yana tare da jin haushi da bakin ciki indai awannan duniyar ne.

Suna ta cin abinci yana tunanin ta inda ya kamata ya bullo mata da abinda ke ransa can ya daure yace wai ya ya naji shiru ne anyi watanni da yaye malam fa? Ta dafe kirji Don Allah yaya kada kaja mini ina zaman zamana Allah ne yace na huta ka barni kawai. Yayi yake hakane idan kin gaji basai na kawo miki kanwa tayi ba. Ta kalleshi da sauri da mamakin abinda yace amma ta kasa furta komai sai kada kai da yake kawai. Ganin haka ya sanya yace ma,u yanzu ace ga wata mace tana shirin rasa rayuwarta saboda ni da kaunata har ta dinga shiga cikin mawuyacin hali na jinya zaki iya yarda na aureta? Gabanta ya kuma faduwa duk da tasan wasa yakeyi tace watakila na iya watakila kuma bazan iya ba. Dadi ya cikashi jin ta dan sakko har tana murmushi yace. Wani abu ne ke faruwa mai ban mamaki ma,u wai kamar ni Alhaji nura kwangila ke roko har da durkusawa kamar zai yi kuka, ko da yake yana da gaskiya. Akan me yake rokonka kuma? ta fadi da fargabar jin abinda zai fada. Ya kalleta ganin har lokacin babu wani tashin hankali ko bacin rai akan fuskarta ya sanya ya cigaba da magana. Bazan boye miki komai ba ma,u nana ta nuna tana sona naki bata fuska har ta gaji da nuni ta sanar dani da bakinta. Ma,u tayi mutuwar zaune akan kujera sai taji kamar ya faskara mata gatari ne akan tsakiyar kanta ta kasa motsawa. Ganin bata ce komai bane yasa Ahmad ya cigaba da magana. Ban boye mata ba na fada mata gaskiya ban sonta, hasalima bazan iya hada matata da kowacce mace ba, bazan iya mata kishiya ba, ranar da bacin rai tabar ofis dina ashe wau faduwa tayi a gida bayan anyi bincike aka gano tana dauke da ciwon zuciya daya kamata cikin dan lokaci. Bayan mahaifanta sun gano dalilin faruwar hakan suka tsirani da magiya kamar zai mini kuka akan na auri diyarsa na rasa mai zance masa tunda na fada masa gaskiya bana son diyarshi amma ya tsaya yimin magiya daga karshe nace ya bari nayi shawara da iyalina tukunna.

Har ya kammala bayaninsa ma,u tana jinsa kamar cikin gajimare yake mata ihu cikin kunnuwanta. Ta daina fahimtar komai, bugun zuciyarta ya sauya abinda ta jima tana zargi ya tabbata kenan ta kuma tabbatar karya Ahmad ya shirya mata yanzu don ya sami auren nana don haka sai tayi murmushi cikin ranta tace zaka iya rubuta littattafan hikaya lallai amma a fili cewa tayi. Amman bai kamata ka bar nana ta rasa rayuwarta ba bayan dumbin alkhairan data aikata maka. Tana gama fadin hakan ta mike ya bita da kallo baki bude ya gaza gano inda zancen nata ya dosa shin da gaske takeyi ko kuwa gatse ta masa yakamata yaji cikakken bayani daga gareta. Taku uku ma,u tayi ana hudun juwa ta debeta ta fadi kasa tim! Ahmad ya tashi da gudu a gigice ya nufeta yana kurma salati, ya tallafota yana jijjigata gami da kiran sunanta amma ma,u ta suma. Ya mike da sauri ya samo ruwa ya tallafota ya zuba mata afuskarta ta bude idonta da sauri tana ganinta a rike ajikinshi ta fashe da kuma ta fara kokarin kwacewa daga jikinshi amma ta kasa domin jikinta ya mutu lubus! Cikin kuka take fadin me ya sanya baka barni na mutu ba Ahmad? Mamaki ya kamashi har ya kasa boyewa ya waro ido yau shi ma,u ke kira da Ahmad kai tsaye abinda bata taba fadi ba tsawon rayuwarta. A fili yace

15 / 47