CUTARWA COMPLT BY AYSHERCOOL

Author :  AYSHERCOOL Category :  African Stories & Novels

Chapter   56 / 74

165K to 168K   out of 219.4K words

me up in romantic way"""

"Ta ce ""Like how? Ba gashi yanzu ka tashi ba"""

"Ya juyo ya kalleta ya janyota jikinsa, yayi kissing Win ta a goshi ya ce ""Wake up sweetheart"" irin haka nake so."

"Ta ce ""Ashe ba zaka tashi ba idan haka zan yi maka, yadda nake fama da kai ka tashi, da ™yar ka ke tashi fa"""

"Ya ce ""A'a idan ki ka yi mini haka sai na fi saurin tashi ai"" ya ™are mata kallo ya ce ""Ni gaskiya a daina tashina da irin"

"wannan kayan, ni dressing zaki din ga yi mini yadda ba za ace ki na jin hausa ba ma"""

"Ummi ta ce ""Innalillahi, wai dama haka ka ke, mutum sai tsaurin ido, duk a ina ka san wannan ne?"""

"Wata irin dariya ta bashi, ya ce ""Ai tsaurin ido ya riga ya ™are tsakaninmu, tun da ni da ke yanzu kin san waye boss, fita fa zan yi"""

"Ta Wan Sata fuska ta ce ""Cewa fa ka yi a gida zaka wuni"""

"""To ya zan yi fita ta kamani, ki yi ha™uri kin ji baby"""

"Ummi ta kalli fuskar sa ta ce ""Yaushe zaka kai ni gida na gaida su mami ne? Kuma ban je na yi wa Kawu da su anty"

"bangajiya ba""."

"Ya Wan sosa kai ya ce ""Haka ne, amma for now ban ji zan iya bari ki fita ba"""

"Ta marairaice ta ce ""Dan Allah"""

"""Na ji amma da sharaWi"""

"Da sauri ta ce ""Menene sharaWin?"""

"""Sai kin ce mini baby"" tayi turus tana kallon sa."

"Ya ce ""Yauwwa ai na san lagonki, and ki ro™e ni in a romantic way, a guje zan barki""."

"""Dan Allah baby ka bar ni na je na gaida su mami, na je gida na yi wa kawu bangajiya"""

"Ya girgiza kai ya ce ""Ba haka ba, idan kin koyo sai ki tambaye ni, yanzu dai tashi mu je ki tayani wanka"" sai da ta Wan"

"matsa daga kusa da shi ta ce ""Wanka kuma?"" Ya Waga mata gira."

"""A'a zance maka babyn dai"" sauka yayi daga kan gadon ya ce ""Kina da sauran aiki Salma, ina son soyayya sosai ban"

"sani ba ko dan ban taSa yi ba sai a kanki, amma ina son gidana ya fi ko ina samar mini farinciki, kar ki saka na fara le™e-le™e"" ya ™arasa maganar yana shigewa toilet, a daidai lokacin da ™irjin ummi ya buga da maganar sa ta ™arshe."

"Shi ya ma manta da ya faWi maganar, ummi kuwa duk ta shiga damuwa, ya gama cin abincin sa ya fice."

"Ummi ta zauna ta yi shiru tana tunani, abun duniya ya isheta, tana son yin abun da za ta faranta wa raihan rai, sai"

"dai haryanzu tana tsananin jin kunyarsa. Ta buWe wayarta ta shiga YouTube, tamkar sun san halin da take ciki, ta ci karo da wani video, malamar tana ta bayani a kan kula da miji."

"Malamar take cewa ""³an mata nawa ya tsallake bai aure su ba, ke ya auro ki ya kai ki gidansa, ko da ya kasance mai kule-kule ke Win dai ke ya zaSa, dan me zai kai ki gidansa ki din ga yi masa gidadanci, ba ko yaushe kunya take da muhalli a aure ba"" ummi ta shagala tana kallo, malamar har da demonstration na yadda za a yi wa miji kissa."

"Ji ta yi ana danna bell Win ™ofar falon, ta ajiye wayar ta tashi ta buWe."

"Ta faWaWa murmushinta, ganin wata babbar mace da wata."

"Tayi musu maraba zuwa cikin falon, tana ta jera musu sannu da zuwa."

"Matar ta kalleta ta ce ""Kin gane ni ne?"""

"Ummi ta yi murmushi ta ce ""Na gane ki, maman bauchi ce, ai ya nuna mini a hoto"""

"Hajiya Aisha tayi murmushi ta ce ""Lallai kin yi kyan kai, ina can ya aike ni bana ™asar, ban samu zuwa bikinku ba, na je umara daga nan na tafi aiken raihan"""

"Ummi ta yi murmushi ta kawo musu ruwa, da lemo."

"Ta ce ""Daga baucin ku ka taho?"""

"Hajiya Aisha ta ce ""Daga can muke, tun safe muka taho ai"""

"Ummi ta ce ""Be gaya mini ba, ai da na Wora muku girki tun kan ku ™araso"""

"""Be san zamu zo ba shi ma, amma yana gida ai ko?"""

"Ummi ta ce ""A'a ya fita tun Wazu"""

"Ta kawo musu kayan tea, ta shiga kitchen ta Wora tukunya."

"Siyama ta kalli Hajiya Aisha ta ce ""Mummy, ga fa kairun nisa'i in ji raihan, ki ga rashin mutuncin da yake yi mini a kan"

"matar nan, wai duk matan ™arshen zamani ita suka rako"""

"Hajiya Aisha ta yi dariya ta ce ""Raihan ne fa, haka nima yake ce mini duk ranar da na zo gidansa na ci girkin ummi,"

"wai sai na koma bauci ba yatsu saboda daWi, hannunta akwai maggi"""

"Suka yi ta dariya, nan da nan ummi ta din ga yi musu hidima, ta kawo wannan ta kawo wancan."

"Duk rashin son sakewa da mutane irin na ummi, ta Wan sake da hajiya Aisha, suna ta hirar duniya."

"Hajiya Aisha ta kira raihan a waya tana faWan ina ya tafi weekends, ta zo baya nan."

"Ya ce mata yana gida, ta ce ita ba zata kwana a kano ba, ya dawo za ta tafi."

"Dama duk a takure yake, kiransa kawai ta yi ta zaunar da shi, Safiyya na ta kaiwa tana komowa tayi kwalliya, sai dai"

"ko kallo ba ta ishe shi ba, hankalinsa yana kan wayarsa yana kallon hotunan ummi."

"Idan ya kalli safiyya sai ya ganta wani iri, shi dai a wurinsa ya fi ganin kyan ummi nesa ba kusa ba, ita ba™inta ke hana"

"a ga kyawunta, kuma yanzu ta washe ta ™ara kyau."

"Duk da yana complain da kunyarta ta yi yawa, amma yana jin daWin wuninsa a gida tare da ita, ya ci abinci da ita, ya"

"sha™i daddaWan ™amashin turarukan ta, uwa uba lallausar fatarta da ba ya gajiya da taSawa, jikinta tamkar jikin tarwaWa, ko kuma wata fulawa."

Shi komai na ta burgeshi yake yi.

"Raihan ya kalli mami ya ce ""Maman bauci tazo tana gidanmu tana jirana"""

"""Saura ka je ka gaya mata wani abu, ta zo ta cika mini kunne da masifa""."

Mintuna arba'in sai ga raihan ya dawo.

"Aikuwa hajiya Aisha ta din ga masifar weekend ya zauna a gida da matarsa, amma ya fita yawo, idan ya je wurin"

mamin shayar da shi take ko kuwa?.

"Shi dai bai ce komai ba ya ce ""Ayi ha™uri na daina, amma kar a juya mini baya a koma wurin ummi"""

"Ta ce ""A'a ni fa na yi ´a, ga iya girki ga mutunci, kalli yadda ka yi ™iba fa, ummi ta iya kiwo, ya ma sunan da ka ke gaya"

"mata"""

"Ba kunya raihan ya ce ""Khairun nisa'i"""

"Ummi kuwa kamar ta nutse, ta tashi ta tafi kitchen tana wanke kwanuka."

"Ya sameta a kitchen ya ce ""Madam sannu da ™o™ari, Mummy na ta yaba miki, ina godiya sosai da sosai"""

"Hararsa tayi ta ce ""Ba™ina ne ai ba naka ba"""

"Ya ce ""To ai shikenan, zo ku yi sallama"""

"Ummi ta ce ""Har tafiya za su yi?"""

"""Wallahi kuwa, ta ce ko gidanmu ba zata ba bauchi zasu koma, gashi ba su taho da direba ba, kar su yi dare""."

"Ta ce ""To yi gaba zan taho"""

"""Saboda me?"""

"""To kawai sai kuma a ga mun jero tare?"""

"Dan™o hannunta yayi suka yi waje, turus ummi ta yi ganin iyayen akwatuna a falo."

"Hajiya Aisha ta ce ""To ga kayanku nan, ku duba abun da bai yi miki ba, sai a canzo, ko kuma ma yi waya kawai, tafiya"

"zamu yi"""

"Ummi ta ce ""Mummy ki bari ki kwana mana"""

"Hajiya Aisha ta ce ""TaS mijina yana gari, wa zai kula mini da shi, sai mun yi waya"""

"Cikin sauri ummi ta tafi Waki, ta Webo turaren wuta, na gashi da na jiki, ta din ga haWo kaya a leda, ta bawa Siyama ta"

ce musu ba yawa.

"Hajiya Aisha ta yi musu nasiha, tare da fatan alkhairi suka tafi."

"Nan raihan ya zauna a falon, yana bubbuWe akwatunan, ummi kawai ta zuba masa ido tana kallon uban kayan da ko a mafarki ba ta taSa tunanin mallakar su ba."

"""Ki saukko ki gani mana sweetheart"" ta saukko ta zauna a kusa da shi tana kallon kayan."

"Ganin tayi saroro kamar sokuwa ya sanya ya ce ""Ko kayan ba su yi miki bane ba?"""

"Kawai ya ga hawaye na bin idonta, gaba Waya ya rikice ya ce ""Menene kuma? Ko Mummy sun yi miki wani abun da ya Sata miki rai ne?"" Ta girgiza masa kai alamar a'a."

"""To menene? Bana son kukanki ummi, gaya mini"""

"Ta ™ara matsawa kusa da shi, ta rungume shi tana kuka."

"Ya saka hannunsa ya tallafo fuskarta, cikin kulawa ya ce ""Gaya mini menene?"""

"""Na gode"" tayi maganar wasu hawayen na zubo mata."

"Raihan ya ce ""Ha™™inki ne fa ummi, meyasa zaki yi kuka?"""

"Ta sake kwantar da kanta a jikinsa, ta ce ""You mean a lot to me, na tuna lokacin da na shekara biyu babu kayan kirki,"

"yau ka gwangwaje ni da wannan uban kayan, ni wallahi ban san ma me zan ce ba, kamar kalmar godiya ta yi kaWan, Allah ya suturta ka duniya da lahira, ya yalwata arzikinka, na gode MD"""

"Jikinsa yayi sanyi sosai, duk da bai san cikakken tarihin ummi ba, amma alamu sun nuna ta sha gwagwarmaya da"

rayuwa.

"""To ki daina kukan haka, in sha Allah in dai ina raye, sutura sai dai ki Wauka ki bawa wani, sutura ba zamu yi ta Winka"

"ta muna sawa""."

"""Na gode MD, amma dan Allah kar ka takurawa kanka yi mini abun da ba ka da shi, ni dai na gode sosai"""

"""To ba zaki kirani da wani suna na soyayya ba, sai MD"""

"""MD my dear"" ta faWa tana murmushi."

"""Wow ashe duk tsawon wannan lokacin, am your dear ban sani ba, barakallahu fik baby"""

"ŠaWWaga mata kayan ya cigaba da yi, kaya sun haWu masu tsada har da gwal."

"Sai da ya zo kan akwatin ™anan kaya, ya din ga WaWWagawa yana cewa ba ™aramin kyau zaki yi a ciki ba."

"Ummi ta ce ""Ai kai a nan ka fi kauri, ni bari na je kitchen abincina kar ya kama""."

"Idan ummi ta kalli raihan ta kalli kayan nan, sai ta rasa me ma za ta ce masa, ya baje yana ta aiki a system gefen sa ga"

biro da takarda.

"Dogon matashi cikakke, dai-dai gwargwado raihan kyakkyawa ne, kuma duk kyawawan mata babu wadda ya gani ya"

"ce yana so, sai ita kuma yake ta wahala da ita."

"""Ya dai madam?"""

"Ta tashi ta ce ""Bakomai, zan je wancan falon na gyara shi kan magariba""."

"Ya ce ""Yauwwa, ni kuwa na ce ko ´ar aiki za a samo miki ne? Ta din ga taya ki aikin nan, yayi miki yawa""."

"Ummi ta ce ""Aikin gidan nan guda nawa yake, zan iya abuna"""

"""FaWi gaskiya dai, ko abun ne ya motsa, dan kar a aure ni"""

"""To a aurekan mana, duk wadda za ta iya zama da ni ta shigo"""

"Ya kwashe da dariya ya ce ""Eh lallai kin yi baki baby""."

"Ummi ta Wauki hoton kayan, ta turawa su Yaya maryam, suka din ga murna tare da sanyawa raihan albarka."

"Iya ™o™ari ummi take yi, wurin rage kunyar raihan da take ji."

Dan haka a yau tayi iya yin ta tayi irin shigar da yake so.

"Aikuwa daga kallon da ya din ga yi mata, ta gane ya ji daWin hakan sosai da sosai."

"Ya sha mamaki sosai da sosai, dan kuwa tayi masa kyau sosai da sosai, Allah ya taimaki ummi raihan ba shi da"

abokan da zai yi zaman majalisa da su.

"Duk a kunyacen take, amma ta dake kar sokoncinta ya sanya shi fara kalle-kallen."

"""Baby zaka kai ni gaida su mamin da su kawu""."

"Ya ce ""Wow, shagwaSar nan taki tana burgeni ummi"""

"Maganar Iya ta tuna, da take ce mata 'Tana shagwaSa da fuska kamar kashi'"

"Ya amince da zuwanta gaida su mami, amma ya ce sai ranar juma'a da daddare. Washegari ranar asabar kuma sai ya"

kai ta gidansu.

"Ummi ta yi ta murna, raihan ya ce ""Ai in dai zaki din ga abun da nake so, zan zama mijin hajiya Salma."

"Wata irin soyayya raihan yake nuna wa ummi, da take fatan ta Wore har abada."

"Ranar juma'a tun safe, ummi take aikin yin sinasir da miyar agushi, wanda za ta kai gidan su raihan."

"Tun sallar magariba ta shirya take jiran raihan, ya dawo ya ™are mata kallo ya ce ""Gaskiya kin yi kyau da yawa, ba zan"

"tafi da ke a haka ba, sai ™amshi kuma ki ke yi, am jealous ki rage kyan nan"""

"""Daga ni sai kai fa zamu tafi a mota mu dawo, dan Allah ka shirya mu tafi"""

"Sai da ummi tayi da gaske, sannan ya shirya suka tafi."

Tambayarta ya din ga yi a kan wannan kulolin restaurant za ta buWe ne?.

"""Eh in dai zaka yi patronizing Wina"""

"""To Wan buWe ki san mini abun da ki ka dafa Win"""

"""Aikuwa ba za ka ci ba"""

"""Suna tafe suna faWansu irin na masoya""."

"KarSar da mami tayi mata kawai jikinta yayi sanyi, ko kallo ummi ba ta isheta ba."

"Safiyya kuwa tun da ta ga ummi jikinta yayi sanyi, ana ta ummi mummuna ce, amma ta ga ummi dirarriyar mace,"

"muryarta kawai idan ta yi magana sai ka so ganin waye yake yin maganar, gashi komai na ta a nutse. Duk da dare ne amma duk wanda ya ga ummi ya santa a da, ya san ta canza sosai, fatar nan ta ™ara kwanciya tayi fresh sai ™amshi take yi."

Ko gaisuwar ummi ta™i amsawa.

"Raihan ya ce ""Mami zuwa muka yi ta gaishe ki, ta yi muku bangajiya"""

"""Na ce maka ina nemanta ne, tun a farko ban gaya maka babu yawuna a maganar aurenka ba? Ka nema mata wata"

"sirikar bani ba. Muguwa kawai, sumi-sumi da ke na zata ta Allah ce, ashe mutuniyar banza ce, kuma da ni ki ke zancen. Ša na ne dai wallahi sai kin bar shi, zan yi masa irin auren da nake so, kuma ina nan dawowa kanki"""

"Raihan ya tashi ya ce ""Ummi mu je mu gaida su Alhaji mu tafi kar dare yayi"""

"Ta tashi kanta a ™asa, ta Wauki kwandon da suka zo da shi, ta ajiye wa mami na ta food flask Win."

"Mami ta ce ""Kwashe tsiyarki, ba abun da zan yi da abincinki"""

"Raihan ya dur™usa ya Wauka ya ce ""Bari a ™arawa mami da shi"""

Ta buWe baki tana kallon raihan.

"Bayan fitarsu Nihal ta ce ""TaS mami dama haka matar yayan take? Gaskiya babu lallai ya saurari safiyya, kin san halin sa ba komai yake burge shi ba, amma idan ya ce yana son abu ya dage, canza shi sai Allah. Kalli dirarriyar mace ga"

"iyayi""."

"""Ke dalla rufe mini baki, tashi ki bar falon nan"""

"Can kuwa ummi jikinta yayi sanyi, amma karSar da ta samu a wurin Alhaji da Hajiya, sai ya mantar da ita abun da"

mami ta yi mata.

"Sai gashi sun shantake, har goma na dare suna gidan, sun sha nasiha da sanya albarka daga bakin Hajiya da kuma"

Alhaji.

"Alhaji da kansa ya kira Salim da Sagir a waya cewa yana nemansu, bayan sun zo, ya sake gabatar musu da ummi."

"Tun ummi na nan suka fara cin abincin su, suna santi ana koWa girkin nata, wanda hakan ya yi wa ummi daWi sosai."

"Goma da rabi, sannan suka tafi gida, raihan bai yi mata maganar abun da mami ta yi ba, ita ma ba ta yi masa ba, sai"

"dai ta damu da ganin safiyya ya Waga wa ummi hankali, ganinta yarinya kuma kyakykyawa."

"Haka ta kwana tana wasi-wasi daban-daban, ta ™uduri aniyar sake zage damtse a kan raihan, yadda ko zai yi wani"

"auren, ba za ta rasa soyayyar sa ba."

"Ta nemi iznin sa, tana son Waukar wani abu daga lefenta tayi kyauta da shi, ya ce nata ne, babu bu™atar ta tambaye"

shi.

"Washegari ta yi girke-girken ta, ya kaita gidan dr."

"Suna hanya take ce masa ""MD, yakamata ka koya mini mota, sai in din ga kai ka wurin aiki, ina Waukko ka"""

"Yayi dariya ya ce ""Matata direbata"""

"""Eh mana, kaiman ka din ga hutawa"""

"""Kawai ki ce a saya miki mota"""

"Ta waro ido ta ce ""Wace ni? Ba haka nake nufi ba da wasa nake yi maka""."

"A ™ofar gidan yayi parking, ya ciro 10k ya mi™a mata ya ce ""Wannan ki bawa dr. Ki ce in ji ki amma, ni idan na zo"

"Waukar ki, zamu gaisa da shi"""

"Kissing Win raihan ta yi a kumatunsa ta ri™e hannunsa ta ce ""Thank you baby.. ya kalli idonta ta ™arasa babyna."

"Dariya yayi yayi kissing Win ta a baya, yana maimaita mata i love you."

"Farida kasa Soye mamakinta tayi, ta bi ummi da ido, ummi kuwa ta shagala suna murnar ganin juna ita da noor."

"Kallo Waya zaka yi wa ummi, ka san hankalinta ya kwanta, leshin jikin ummi kawai take kallo, da yake wasu kayan a"

"Winke a ka kawo mata, ta sha kwalliya duk da mayafinta a ka ta Wora shi."

"Dr. Ya fito yana faWin ""Oyoyo mamana, amarya ba kya laifi"""

"Ummi ta dur™usa tana gaishe shi, ya amsa mata cikin kulawa."

"Ya ce ""Mamana, kin ga yadda ki ka yi kyau kuwa? Lallai aure ya karSe ki, kin ganki kuwa? kunya ta rufe ummi."

"Da kausar ba tayi niyyar fitowa ba, amma dai ta fito ganewa idonta ikon Allah, ummi an sha to match, har da wani"

agogo mai Wan karen kyau.

"Noor ta bubbuWe kwanukan da ummi ta zo da shi, miya ta sha kaji zu™u-zu™u ga snacks, abun da inteesar ba ta taSa"

yi ba.

Sun yi hira sosai da dr. Har take gaya masa cewar raihan ya yi mata lefe.

Dr. Ya din ga sanya masa albarka.

"Da azahar da zai fita, ummi ta kawo kuWin nan ta bashi dubu bakwai, ukun kuma ta ™ara biyu ta bawa farida biyar."

"Sai dai farida ba ta so yadda ta ga ummi ba, ta kasa Soye hassadarta ba™in ciki ya bayyana ™arara a kan fuskarta,"

kausar ma sai wani zumSura baki take yi tana hura hanci.

"Ummi ta ce wa noor ""Yaushe zaki zo ki ga kayan da MD ya saya mini, ki zo ki Wauki abun da ki ke so"""

"Noor ta ce ""rana ita yau, zan diro ko ta katanga ne, zan zo ki haWa mini akwatu guda"" ummi kamar wurin noor ta zo,"

tare suke ta hirarsu.

"Ummi ta mi™e ta hau gyare-gyaren gidan, duk gidan yayi ™azanta saboda ba ta nan."

"Tana nan Abdul ya dawo, shi ma ya yi farinciki sosai da sosai da ganin ummi, sabuwar shadda ta bashi yadi goma, ta"

ce ya Winka musu shi da dr.

"Ana sallar magariba raihan ya zo tafiya da ummi, suka gaisa da dr. Yayi wa dr. Alheri, ya sha sanya

56 / 74