Author : Aisha Aliyu Garkuwa Category : Free Novels Online (Read & Download)
cewa yana tare da mutane na hannun damansa suna tattauna akan al'amarin Moddibo da yanda zasu bayyanar dashi a Masarauta ga yan uwansa.
Ganin yanda ya gurfana ne yasa Sarkin zagi cewa.
“Hattara dai Sarkin Ƙofa, mene tafe da kai?”.
Cikin rawan murya tare da tsantsan farin ciki yace.
“Al'amarine mai girmane yake tafe dani”.
Duk idanu mutanen Fadan suka zuba masa ganin yanda fuskarsa ke ɗauke da tarin zumuɗin isar da labarin.
Sarkin Fada kuwa cike da kulawa yace.
“Shin wannan wani al'amari ne?”.
Aƙage Sarkin ƙofa ya sake risinar da kansa kana yace.
“Ina so abani izini ne nayiwa Innare Tsohuwar Jakadiyar Gimbiya Ruƙayya iso wacce ta ɓace tare da Alieeyu tsawon shekara talatin”.
Wani irin murmushi Sarki Youseef Mouley ya saki mai cike da zallan farin ciki da jin daɗi acikin ransa yace.
Alhamdulillah ta amsa kiranmu kenan lallai wannan ya nuna ta riƙe mana ɗanmu da amana da aminci bata kuma wofintar da al'amuran sa ba tana bibiye dashi, yanzu tsawon kwanaki biyar bataji labarinsane ta bibiyi al'amarin sa gashi ta nufo nan ne kuma da yaƙinin cewa tabbas daya shigo ƙasar nan zai dawo Mahaifarsa.
Afili kuma murmushi ya sakarwa Sarkin Ƙofa kana cike da nutsuwa da kamala kana da ƙasaita irin na sarauta ya masa alama da hannu ta shigo...
Cikin sauri Sarkin Ƙofa ya miƙe kana ya fita kallin Innayi dake tsaye jikin mota yayi tare da faɗin.
“Bismillah”.
Innayi kuwa juyawa tayi tare da kallon su Abban Jameel kana tace.
“Ku ɗan yi haƙuri ina zuwa”.
Su kuwa baki ɗaya cike da ɗumbin mamaki suke kallonta.
Cikin sauƙe numfashi Hajja Nana ta gyaɗa kai tare da cewa.
“Toh mu dai munfi karfin saiduwa, koda an kawo mu nan da za'a sayar damu ne bazamu saiduba”.
Sai kuma ta juya ta kalli Khausar dake zaune gefenta wacce idanunta suka kumbura sukayi ja jawur gashin idanu suka jiƙe yayin da suka ƙara tsayi kallo ɗaya zaka mata ka tabbatar tasha kuka tamkar mai isarta cikin taɓe baki tace.
“Toh kuma kukan me kikayi tunda, ai burinki ya cika, ba dai auren wanda ba'asa asalinsa ba, ai gashi dai kinga kuma wata duniyar da aka kawo mu, ko mai za'a ce mana ko mai za'a mana kuma oho domin wannan al'amari dai yafi kama da almara”.
KhausarMouleey ya jinjina tare da faɗin.
“Ai nan Fada ce mai mutunci da karrama baƙo”.
Sake sunkuyar da kanta tayi kana tace.
“Ranka ya daɗe baƙin suna da yawa”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Koda ace baƙi ɗaya Yan yanki da kuke kika ɗebo ba zasu rasa muhalli acikin wannan Masarautar tamu ba”.
Lallausan murmushi ta saki tare da jinjina kai kana tace.
“Toh abani jagora wanda zai kai mu masauƙin baƙin namu.
Kai ya jinjina kana yace.
“Toh shikenan babu damuwa”.
Kallon Jakadiyar sa yayi tare da faɗin.
“Jakadiya Bismillah akai su sashen Yamma a saman za'a sauƙi”.
Bi'ana saman inda Modibbo yake kenan
Sake sunkuyar da kai Innayi tayi tare da faɗin.
“Ranka ya daɗe Akwai maza tare kuma damu mata”.
“Baki da matsala”.
Ya faɗa tare da kallon Sarkin Ƙofa kana yace.
“Kai kuma ka kai Mazan Ƙofan Gabas”.
Kai ya gyaɗa cike da girmamawa yace.
“Toh”.
Kana suka fice yayin da Jakadiya ta yiwa Innayi, Hajja Nana, Ummi, Hajiya Bunayya, Asma'u, Asiya, Dija, Khausar, Aunty Hawwa da Hajja Umma Baki daya bayan Jakadiya suka bi tayi musu Jagora.
Yayin da Abban Jameel, Baffa Jimeta, Lamiɗo, Haiydar suka bi bayan Sarkin ƙofa wani babban Hanya suka bi kana suka hau Upstairs
Suna haura wa saiga wasu Ƙofofi biyu ɗaya aɓarin dama ɗaya aɓarin hagu Jakadiya takai su Innayi ƙofar dama yayin da Su Abban Jameel aka kaisu ƙofan hagu ta can gefen yamma wanda bata cikin falon da Modibbo yakeba suka ɓula ba sai dai in zadu sauƙo in sunbi ta ƙofar tsaki ta cikin falon zasu bulla...
Jakadiya kuwa tana fita daga masauƙin su Innayi kai tsaye ɗakin Didi ta nufa tana shiga falon ta zube agaban Didi tare da faɗin.
“Albishir”.
Fuska ɗauke da murmushi Didi tace.
“Goro”.
Sake risinar da kai Jakadiya tayi kana tace.
“Fari ko Ja?”.
Still Didi na murmushi tace.
“Faro soll Dan ƙwalele”.
Washe baki Jakadiya tayi tare da cewa.
“Toh Innare na cikin Fadar Masarautar Mouley ta iso tare da al'umma baki, daga cikinsu akwai masu tarin kamala da Alkunya kana tazo mana da kyakykyawan furanni masu haska gida”.
Didi kuwa cikin matsanancin farin ciki da jin daɗi ta miƙe kana tace.
“Masha Allah Alhamdulillah ta ina take, muje ki kaini gareta”.
Kai Jakadiya ta girgiza cike da ladabi tace.
“Amma da kiyi haƙuri ki koma ki zauna yanzu dai, farko a fara Marabtansu da abubuwan motsa baki saboda sun ɗebo hanya sannan asanar da hadimai afara yi musu girki na musamman domin maraba”.
Cike da gamsuwa Didi ta jinjina kai kana ta kalli Hadimanta dake durƙushe ƙasa tace.
“Maza kuje ɓangaren Hadiman dake Kichen kuce maza ashirya abinci na alfarma yanzu”.
Cike da ladabi suka amsa kana suka fita.
Didi kuwa cikin wani irin farin ciki da annashuwa kana da jinjina girma da mutuntaka irin na Innayi ta kalli Jakadiya tare da faɗin.
“Maza ashirya musu drinks, Fruits, Snack's,da ɗan gashshen nama sannan akwai nono mai sanyi da kwakwa ahaɗa musu”.
Ta ƙare mgnar tare da kallon Lalla Khadijah sai kuma tace.
“Khadija keda Hafsat ku jagoranci aikin”.
Kai suka jinjina kana atake suka haɗa suka kai sashen su Innayi da kuma sashen su Abban Jameel...
Acan ɓangaren su Hajiya Bunayya kuwa tunda tashiga tangamemen Falon da yaji komai na more rayuwa take kallon komai cikin ƙunan zuciya mamaki da kuma tarin takaici....
Innayi kuwa suna zama ta kamo hannun Khausar da har zuwa lokacin take shesh-sheƙan kuka kana ta riƙo Asma'u yayin da Ummi ke biye dasu suka nufi ɗaya daga cikin ɗakin da yake 3bedrooms ne.
Ƙofar da shine na tsakiya suka shiga.
Suna shiga ta saki sassayyan numfashi tare da sakin hannun Khausar sai kuma ta zaunar da ita gefen gadon kana ta juya ta fita.
Fitanta yayi daidai da shigowar Hadimai mata suka shigo da Fruits suka ajiye cike da girmamawa suka gaishesu kana suka ce...
Gimbiya tace ayi muku sannu da zuwa sannan ga abubuwan motsa baki kuci kafin ta iso.
Godiya sukayi kana sukuma suka fice ba daɗewa suka sake dawo wasu hannunsu riƙe da drinks,wasu Snack's wasu dambun dabbi da soyayyu.
Yayin da Lalla Khadijah da Lalla Hafsat ke riƙe da wasu Bowls manya da yaji Kindirmo da kwakwa da ayaba suka ajiye.
Cikin tsura musu ido Innayi ta kalli Lalla Khadijah kana ta juyo ta kalli Lalla Hafsat.
Sai kuma ta saki murmushi gani sun ruggumeta cikin bege da kewarsu Innayi tace.
“Allah mai iko da buwaya Khadijah kune kuka girma haka”.
Sai kuma ta kalli Lalla Hafsat dake faɗin.
“Innayi ashe dai rai kanga rai, baki wani canza ba”.
Cikin mamaki dai Hajja Nana Hajia Bunayyah da dukkan su suka zuba masu ido.
Gaisawa sukayi bayan sun zauna.
Cikin kula Lalla Khadijah tace.
“Hafsat muje ko, mu barsu susha ruwa".
Kai Hafsat ta gyaɗa kana suka juya suka tafi hadimansu na taka musu.
Kana acan ɓangaren su Lamiɗo suma haka aka kai musu.
Cikin sauƙe numfashi Baffa Jimeta ya kalli Abban Jameel bayan fitar Hadiman kana yace.
“Toh Alh Bashir wannan al'amari dai da ban mamaki da kuma ɗaure kai yake toh shi wannan yaro na rasa tantance inda al'amarinsa ya nufa”.
Murmushi Abban Jameel kana ya yace.
“Nan shine gidansu Modibbo kamar yadda kakarsa ta labarta min shi ɗan wannan ahlin ne, gidansu ne kuma tsatso kuma jigo sannan kuma tushen sa mahaifarsa kenan”.
Kai Baffa Jimeta ya gyaɗa cike da gamsuwa yace.
“Ikon Allah wannan al'ajabi da yawa yake,ita kuma daga wannan ƙasa ta tashi ta koma Nigeria har Lungunmun can taje ta zauna dashi.
wannan wani irin al'amari ne yasa ta ficewa daga nan ta koma can”.
Zazzafan ajiyar zuciya Abban Jameel ya sauƙe kana ya gyara zamansa tare da cewa.
“Al'amarine mai girma mai kuma ban mamaki”.
Numfashi Lamiɗo ya fesar wanda tunda aka fara magana bai ce komai ba ya muskuta kana yace.
“Ai wato sha'ani Masarauta sai ahankali idan bakayi Sa'a ba sai a saubata maka rayuwa! A banza”.
Abban Jameel na taunar Inabi yace.
“Hakanne ma yaso kasancewa shiyasa ta gudu da Moddibo domin tseratar da rayuwarsa”.
Baffa Jimeta na kurɓan drinks Mai sanyi yace.
“Allah mai iko”.
Daga nan kuma sai suka rufe maganar tare da cin kayan maƙulashen da aka kawo musu bayan sun gamane Dr Ahmad da sauran masu jan motocin suka sakkamesu suka tafi.
Ɗaya daga cikin Hadiman dake sashin ne ya shigo cike da ladabi ya kallesu kana yace.
“Ga banɗaki sannan ga ɗakuna akwai duk wani abin buƙata da zaku buƙace”.
Murmushi Lamiɗo yayi kana yace.
“Mumgode”
Daga haka ya juya ya fice.
Bayan awa ɗaya, sun ci sun sha Hajiya Bunayya ta kalli Hajja Nana dake goge baki da Tissue tace.
“Wannan al'amari dai da ɗure kai yake”.
Cikin taɓe baki Hajja Nana tace.
“Toh Ni dai fatana dai Allah yasa basayar damu akazo yi ba ehee”.
Dariya mai sauti Innayi ta sanya ganin yanda Hajja ke magana tsakaninta da Allah cike da kamala tace.
“Babu Sai dawa sai karramawa wanda gadon mune, kuma ma in banda abinki a saidaku a nemi me, ki dai dubafa duk wata ɓukata da ɗan Adam yake dashi muna dashi a masarautarmu”.
Ummi kam murmushi kawai take, dan talura Hajja Nana da innayi har yanzu ba'a shiryaba.
Suna cikin haka sukaji sallama, tare da ganin jagorancin Hadiman Didi
Cike da zaƙuwa ta tashigo tare da Jakadiyar ta da kuma Kakar Moddibo Niyna sai kuma su Rahama bakinsu ɗauke da sallama.
Innayi na ganin Didi tayi saurin miƙewa tare da durƙusawa agabanta kana ta sunkuyar da kanta ƙasa batare da tace Uffan ba.
Didi kuwa cikin yalwataccen farin ciki ta tsugunna tare da sanya hannunta akafaɗar Innayi kana ta ɗagota ta tsayar da ita suna fuskar juna, sai kuma kawai ta ruggumeta tare da faɗin.
“Kin gama min komai Innayi kiyi min duk kan abinda ɗan Adam zai yiwa abokin zamansa na halacci, daga yau na ƴan taki kin tashi daga Baiwa kin zama ƴa ƴan tacciya kuma Uwa amintacciya kuma kamila kuma cikekkiyar jakadar sarki mai jirangado”.
Dariya mai sauti Innayi ta sanya wanda ke nuni da zallan farin ciki kana tace
“Alhamdulillah Nagode wa Allah ina tahowa zuciyata na tsinkewa ina tunanin shin ya rayuwa ta kasance shin ana raye ko kuma anbar duniya zuciyata ta cika da fargaba”.
Baki ɗaya mutanen falon kallonsu suke cike da tsantsar mamaki musamman Hajiya Bunayya da wani irin zufan hasada ke fita agoshinta.
Innayi kuwa cike da annashuwa ta cigaba da faɗin.
“Amma Alhamdulillah nayi katari da Youseef akan karagar mulki kana kema nayi katarin dake acikin shigar Gimbiyya amma banga Ubangida naba Sarki Muhammad Aliyu Mouley”.
Kai Jakadiya ta girgiza kana tace.
“Allah yayiwa Sarki Muhammad rasuwa yanzu ɗanki ne Youseef akan Mulki”.
Cikin sanyi Innayi tace.
“Allah sarki, Sarki Muhammad Mouleey. Ubangji Allah yajiƙan sa da Rahma”.
Amin suka amsa a tare,
Ita kuwa innayi juyawa tayi tare da kallonsu Hajja Nana da suka zubo musu idanu sai kuma ta maida idanunta kan Didi tace.
“Yanzu dai idan na fahimta Moddibona Aliyuna shine Yariman Masarautar nan? kuma Sarki Mai Jiran gado?”.
Yalwataccen murmushi Didi ta Saki kana tace.
“Tabbas kuwa shine ɗa Namiji babba A masarautar nan kuma ɗa Mai jiran gado Ahamdulillah kuma ya dawo alokacin da Masarauta ke jiranshi”.
Kai Jakadiya ta jinjina kana tace.
“Sosai kam”.
Didi kuwa cike da nutsuwa ta nufi kujeran dake tsakiyarsu kana ta zauna murmushi ta sakar musu da lallausan murmushi tare da faɗin.
“Jaɓɓama Moɗon”.
Ga Mamakinsu sai sukaji tayi musu magana cikin Harshen Fullanci.
Cikin yanayin mamaki Hajja Nana tace.
“Allah bauɗo be Fulfulde voli, kamar da fulatanci kike yi mgn fa ko?”.
Murmushi ta saki kana tace.
“Sosai ma kuwa Asalina Bafulatanar Adamawa ce ni ɗuyace ga Sarkin Joɗah Sheiykh Jabeer”.
Kai Hajja Nana ta jinjina kana tace.
“Ai kuwa lallai gashi Yaren da kike mana dashi ya tabbatar mana da hakan”.
Wani irin zufa mai kamar tafasasshen ruwan zafine ke tsats-tsafowa Hajiya Bunayya abaki ɗaya ilahirin jikinta acikin ranta take mgn kamar zautacciya.
“Toh shin Me hakan yake nufi, kenan haka nufin Khausar tayi katari ta tsinci dami a akala? Ko shegiyar yarinyar da wayo kamar dala, ko dai dama ita tasan Modibbo ɗan manya ne, kaji shegiyar yarinya da iya bada kafa, yoh da na sani ai wlh shi Amina zata aura.
Ashe Samira da abinda ta hanga.”
Gaba ɗaya tayi kasake ta tafi dogon tunanin.
Ƙanwar Mommy Aunty Hajara. cike da farin ciki tace.
“Khausar Lelelwal asheko da gaske Lelelwal ɗince ke”.
Murmushi Aunty Ruƙayya tayi kana tace.
“Tabbas kuwa abu yayi yadda ran masoya ke so. Dama wani hanin ga Allah Baiwa ce”.
Hira suka cigaba dayi cike da farin ciki da mutunta juna saɓanin Hajiya Bunayya dake cikin tashin hankali da ƙunan zuciya.
Acan ɓangaren su Abban Jameel kuwa Sarki Youseef Mouley da Sheik Jabeer ne suka nufi masauƙin su.
Sheikh Lamiɗo na kallon Sheikh Jabeer ya faɗaɗa murmushin fuskarsa cike da kamala yace.
“Allah nhokke sabugo Sarkin Joɗa kana shagaban ƙungiyar TABITAL POOLAKU, da mi yetti Allah da kansa ne a nan?”.
Kai Sheykh Jabeer ya jinjina kana cike da girmamawa yace.
“Ikon Allah Allah yayi mun haɗu kenan?”.
Murmushi Lamido yayi tare da zamewa gefensa dan shi kansa yasan idan ana batun sarauta toh in su Sheiykh Jabeer na kusa shi dole a ƙasa zai zauna.
Shi kuwa Sheykh Jabeer cikin kamala da kulawa yace.
“Ikon Allah sai kuma muka haɗu anan, amma yanzu dai ku huta in Allah ya kaimu gobe sai muji meke tafe daku?”.
Cikin gamsu Lamido da Abban Jameel sukace to.
Su kuwa daga nan suka fice...
Acan ɓangaren su Didi ma Sallama suka yiwa su Innayi tare da faɗin su huta gobe zasu ci gaba da tattaunawa Godiya sukayi musu kana suka fice.
Washe gari da safe misalin ƙarfe 9:00am Innayi, Hajja Nana, Jakadiya Sheikh Jabeer, Sarki Youseef Mouley, Galadima, Waziri, Didi Abban Jameel, Ummi, Baffa Jimeta Lamiɗo jakadiyarta zaune suke wuri na musamman kuma keɓantaccen palon Abualeey wato sarki Youseef Mouley kenan. yayin da baki daya idanunsu ke kan Innayi.
Innayi kuwa cikin sauƙe numfashi ta cigaba da basu labarin tun randa ta tafi da Modibbo ta wuce Nigeria dashi kana ta nufi Taraba yankin Gembulan sabida sanin yanki fulanine domin Didi na bata labarin, kuma ta iya fulatanci tun a lokacin domin Modibbo shine ɗa na shida a wurin iyayensa daga Khadijah da Hafsat sai da akayi ya'ya uku maza duk basa gama arba'in ake nemansu a rasa sai bayan kwanaki sai a tsinci gawarsu. A wannan lokacin kuma Khadijah da Hafsat sunyi girma da bazasu mance kamannin innayi ba shiyasa sunka ganeta.
Fesar da numfashi innayi tayi kana taci gaba da labarta musu, yanda ta rayu da Moddibo yanda ya taso da yanda yayi karatu, da irin ƙalubalen daya fuskanta, da amintakarsa da Jameel har zuwa mutuwar M Jameel da kuma dalilin zuwansa Morocco da kuma irin ƙalubale da baƙaƙen magana da kuma hantara da suka samu awajen mutane kana ta ɗora kuma da wasiyyar da M Jameel ya bar musu akan Modibbo, haɗin da basu labarin Khausar da dole in dai za'a bada labarin Modibbo da Jameel toh dole cikaton na uku Khausar ce.
Didi Kam lumshe idanunta tayi wani abin idan taji tayi murmushi wani ta zubda hawaye saboda tausayin halin da ɗan ta yakasance cikin na rashin aminisa da kuma rashin su a kusa dashi da ya zame masa sanadin da ake shegantashi.
Cikin sanyin murya tace.
“Allah sarki ɗana Jameel Allah baiyi zamu ganka ba bare muyi maka godiyar kekkyawar amintakarka da gudan jinin, sai dai Alhamdulillah Innayi tunda Jameel bai mutu da rashin sanin iyayen amininsa, in Sha Allah mukuwa zamu kasance mashinyi mishi addu'a a tsawon rayuwarmu. Ummin Jameel Ngd MATUƘA Abban Jameel babu abinda zance daku sai addu'a. tabbas Aliyu na kuma yaga jarrabawar rayuwa wanda nasan ya samu darussan rayuwa masu tarin yawa acikinsu Innayi na gode kinyi min halarcin da bazan taɓa mantawa ba kin tseratar da rayuwar ɗana alokacin da ake neman hallakasa kamar yadda akayi ta hallaka yan uwansa da suka gabata”.
Murmushi Innayi tayi kana tace.
“Wannan yiwa kai ne sannan babu godiya tsakanin mu domin kin cancanci fiye da haka sabida matsayin uwa kika riƙeni ba Hadimarkiba, shiyasa nima nayi miki abinda zan iya yiwa ƴaƴana na cikina”.
Kai Didi ta jinjina tare da juyowa ta kalli Ummin Jameel dake sharce hawaye cikin sanyi tace.
“Ummin Jameel kada kiyi kuka ga Aliyu na in Sha Allah ya ishemu nidake baki ɗaya”.
Cikin gamsuwa Ummu tace.
“In sha Allah kuwa”.
Innayi kuma gyara zamanta tayi tare da cewa.
“Toh Alhamdulillah bayan ta howarsa nan.
Muka gama mgnar komai akan Khausar da bai sani ba. toh Alhamdulillah dama acikin labarin dana baku na faɗa muku wasiyyar da amininsa Jameel ya bari toh Alhamdulillah a makkoni biyu da suka gabata an Aura masa Khausar”.
Cikin wani irin Didi ta kalli innayi tare da cewa.
“Aliyun akayiwa aure!”.
Da sauri innayi ta gyaɗa mata kai kana tayi ƙasa da kanta.
Sai kuma innayi tayi saurin ɗago kanta jin Didina faɗin.
“A....!
Ba editing kam
*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki kenan*
Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.
Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta