Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Sakayya Complete Hausa Novel by Aisha Aliyu Garkuwa

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Free Novels Online (Read & Download)

Chapter   47 / 140

138K to 141K   out of 417.8K words

cikin sauran tsoron tayi lamo a jikinsa.
Buɗe idanunsa yayi da kyar murya a harɗe yace.
“Zaki kasheni fa”.
Haka nan taji raunin muryar da yayi mgn da ita har tsakiyar kanta.
Cike da tsoro da kuma sanyin jiki ta janye jikinta daga garesa kana ta sauƙe ajiyar zuciya cikin rawan murya tace.
“Ni dai ka sauƙe ni anan zan shiga Napep”.
Harara ya watsa mata kana ya cigaba da Driving ɗin sa batare daya tanka taba yana isa ƙofar gidansu yayi Parking cikin sauri ta buɗe Murfin motar ta fita Shikuwa kai tsaye gida ya nufa, zuwa lokacin har anfara kiran sallar maghariba yana Parking ya fito cikin nutsuwa ya nufi sashen sa tare da wucewa yashiga toilet kana ya ɗaura alwala ya fito dai-dai lokacin da M Jameel ma ya fito daga ɗaya ɗakin da alamun shima alwala yayi.
M Jameel na Kallonsa ya zuba masa ido yana murmushi kana yace.
“No wonder A.J Ashe ƙwarjininka ba halitta kaɗai bace gadone jinine mai ƙarfi ke yawo a jikinka”.
Anutse Moddibo ya juya tare da kallon M Jameel daya tsaresa da Ido kana yace.
“Meye kake kallona haka?”.
Murmushi M Jameel Yayi kana yace.
“Ina kallon kane tamkar...!




*Al'bishirunku Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.


Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*


*By*
*GARKUWAN MARUBUTA*SAKAYAH

22

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇



Idrneɗɗ. Cikin sauri Moddibo ya katsesa tare da cewa.
“Kana kallona kamar me?”.
Murmushi M Jameel yayi tare da shafa sajensa kana yace.
“Ina kallon ka kamar Ayu uban Jarababbun duniya”.
Harara Moddibo ya watsa masa tare da cewa.
“Mtssss kai dai baka da aikin yi”.
Ya ƙare mgnar tare da yin ƙasa da kansa yana kallon yanda Jallabiyar, lumshe Idanunsa yayi lokaci ɗaya tsikar jikinsa ya tashi cije labɓansa na ƙasa yayi kana yaja siririn tsaki tare da komawa Bedroom ɗin sa buɗe durowarsa yayi tare da ɗaukar boxes ya sanya kana yaƙara dogon wando sannan ya fito still. Yana jin tudun A ɗin sa M Jameel na ganin fitowarsa ya juya suka fice kai tsaye Masjid suka nufa tare da gabatar da Sallar Maghariba basu fita ba sai da suka idar da Sallar Isha'i sannan suka fito.

Bayan sun isa bakin gate M Jameel ya nufi jikin motarsa dake fake Kallonsa Moddibo yayi kana yace.
“A'a Baza mushiga muci abinci ba?”.
Cike da kulawa M Jameel yayi murmushi tare da cewa.
“Aini naci tunda zafinsa, kasan tun yaushe muke tare da Innayi kuwa? tun bayan sallar la'asar muna tare fa sai da aka kira maghariba nashigo nan nayi alwala”.
Wara Ido Moddibo yayi kana yace.
“Iyee gulmar me kuka yi?”.
Murmushi M Jameel yayi tare da faɗin.
“Ta faɗa min komai ta faɗa min duk kan abinda baka sani ba”.
Gyara tsayuwa Moddibo yayi tare da harɗe hannunsa aƙirji kana ya juya ya kallesa tare da cewa.
“Kamarya abinda ban sani ba?”.
M Jameel kuwa murmushi yayi tare da cewa.
“Zuwa yanzu nafi ka sanin kan ka ma nafi ka sanin wanene kai duk yanda kasan kan ka to yanzu na fika sanin kan ka”.
Lumshe idanu Moddibo yayi tare da shafa sashensa kana ya buɗe idanun nasan tare da kallon M Jameel yace.
“Iyeeeeh toh zo ka fesa min mana tunda angumtsa maka na hannun damana”.
Tsayuwa M Jameel ya gyara tare da cewa.
“Sirrine sai da nayi al'ƙawari bazan fesa maka ba kafin ake fesa min”.
Moddibo kuwa murmushi yayi tare da shafa sajensa kana yace.
“Toh yanda kayi lallaɓa nima zanje inyi lallaɓan afaɗa min”.
Cikin dariya M Jameel yace.
“Toh kaje ka gwada sa'arka, amma yanzu kam kasani bana cikin duhu”.
Taɓe baki Moddibo yayi kana yace.
“Iyyeeee wato gulmana nema kuka tayi”.
Agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa ya kalla ganin da ɗan sauran lokacin salla ne ya juyo ya kalli Moddibo tare da faɗin.
“Ba wani gulmarka da muka tayi na dai faɗa mata cewa kana ɓuƙatar aure yanzu”.
Cikin sauri Moddibo ya juya tare da watsa masa Harara Dariya M Jameel yayi tare da buɗe motarsa yashiga mazaunin Driver key yayi wa motar tare da saita hancin motar ya fara tafiya.
Shi kuwa Modibbo da ƙafa ya nufi masallacin.
A hanya ya tsaya yayi salla kana ya ƙarasa cikin gidan.

Parking aharabar gidan cike da nutsuwa ya fito tare da nufar falon bakinsa ɗauke da sallama ya shiga.
Ahankali yake bin cikin falon da kallo batare daya shiga ba cikin hasken fari gloves ɗin da suka haska falon kana da murmushi afuskarsa yace.
“Ina Umminaaaa?”.
Ummi dake zaune kan 3sitter idanu ta zuba masa batare da tace komai ba.
Malam Ahmad dake zaune kan 1sitter ya kalli M Jameel dake tsaye ƙofar falon tare da cewa.
“Ƙara so mana Jamilu”.
Juyawa yayi ya kalli Ummi kana yace.
“Kin tsaresa da ido kuma baki ce masa ya shigo ba”.
Murmushi M Jameel yayi tare da cewa.
“Ummi nayi kyau ko?”.
Jinjina kai Ummi tayi still Idanunta na kansa tace.
“Sosai ma Babana”.
Murmushi yayi tare da Wara ido kana yace.
“Iyyeee naji daɗina yau kuma nine Babanki ko da yake Baban miji ai baba ne?”.
Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace.
“Sosai ma”.
Ummi kuwa still Idanunta na kanshi.
Bashir daya fito daga Bedroom ne ya kalli Ummi kana ya kalli M Jameel data tsirawa Idanu matsawa kusa da Ummin yayi tare da cewa.
“Yaya Jameel wallahi Ummi na sonka kamar me”.
Sai asannan Ummi ta ɗauke Idanunta daga kan M Jameel ta mayar kan Bashir tare da yi masa daƙuwa kana tace.
“Haka naka Bashiru”.
Asma'u data fitowarta kenan daga Bedroom tayi murmushi tare da zama gefen M Jameel.
Miƙewa Malam Ahmad yayi tare da nufar ɗakinsa bayan sun gaisa da M Jameel.

Kallon Asma'u M Jameel Yayi tare da cewa.
“Asmeey”.
Cike da ladabi ta ɗago kanta kana tace.
“Na'am Yaya”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da cewa.
“Zuwa yanzu kaso 85% cikin 100% na nauyin ku dake araina nake tunawa 85% sun sauƙa min saura shabiyar nake tunawa 15% ɗin nan kuma sune manya masu wuya”.
Ajiyar zuciya yauƙe tare da cewa.
“Ina so inga kinyi karatu kin gama, sannan na miki zaɓi da miji na gari Mumini, Salihi, Mai tsoron Allah, na Aura masa ke, sannan na danƙa masa Amanar ki.
Hakazalika Ina so inga Bashir ya gama karatunsa ya fara aiki ta yanda ko bana kusa zai kula da Ummin mu ba zata nemi komai ta rasaba”.
Cikin yanayin damuwa Asma'u tayi ƙasa da kanta lokaci ɗaya Idanunta suka ciko da hawaye yayin da taji zuciyarta yana masifar bugawa da ƙarfi Allah ya sani in ta tuna zatayi aure ta rabu da Unminta tanajin ba daɗi.
Cikin raunin murya tace.
“Bare ma Yah Jameel kai zaka yiwa Ummi komai kafin mu”.
M Jameel kuwa murmushi yayi tare da kallon Asma'u kana ya cije labɓansa na ƙasa tare da lumshe idanunsa yana sauraron bugun zuciyarsa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da buɗe idanunsa akan Asma'u kana yace.
“To ai ita rayuwar dama ta gaji haka watarana ayi farin ciki watarana ayi baƙin ciki!”.
Girgiza Kai Bashir yayi tare da kallon M Jameel cikin yanayin tsinkewar zuciya ya gyara zamansa tare da cewa.
“Yah Jameel Meyesa kake karyar mana da zuciya ne!?”.
Girgiza kai M Jameel Yayi tare da kallonsu wani irin tausayinsu da kuma ƙaunarsu na ratsa dukkan zuciyarsa, bashi da wani ƙunci a rayuwarsa fiye da yadda ya kasance baya tare da Umminsa da ƙannensa a inuwa ɗaya, ciwon sakin mace ba iya kanta kawai yake tsayuwa ba, har kan ƴaƴan data haifa yake shafa.
Iska mai zafi ya fesar daga bakinsa kana yace.
“Ba karya zuciya bane Bashir burina ne, akan ku inaji kuma har yanzu akwai kason da ban idaba,
sabida ban zaɓawa Asma'u mijin aure a shine babban abinda yafi damuna sannan kai kuma kagama makarantar ƙuruciya ce sai jami'a gidan kazo nazo”.
Numfashi yaja tare da fesarwa Idanunsa nakan Bashir yace.
“Acan ne ake samun tarbiyya daban-daban da halayyar al'ummar matasa kashi-kashi ina tunanin kada ginin da mukayi nida Ummi wani yaje yayi yaɓe akai ya lalata kyakkyawan gini da kyakkyawan tubalin da mukayi maka”.
Da sauri Bashir ya jujjuya kai tare da cewa.
“In sha Allah haka bazai faruba”.
Cikin jin sanyi yace.
“Bashir kayi min al'ƙawarin zaka kasance nagari, kayi min alƙawarin zaka kasancewa Ummi farin cikinta”.
Lokaci ɗaya hawaye suka cika idanun Bashir cike da tsoron kalaman Yayan nasa.
Cikin wata razananniyar murya ya kalli M Jameel da Idanunsa ke lumshe kana yace.
“Nayi maka al'ƙawari Yah Jameel Nayi alƙawari zan kasancewa Ummi ɗa nagari zan kasance me share mata hawaye, zan kasance mai sata farin ciki idan Allah yayi duniya dan Manzo (S.A.W) ”.
A hankali ya ɗaga idanunsa tare da kallon Ummi da ta tsirawa M Jameel idanu cikin wani irin yanayi ko ƙyaftawa bata yi ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.
“Zan kasance mai sata farin ciki, nayi alƙawari Ummi ba zata taɓa shiga ƙunci ko damuwa ba in dai a kai nane in sha Allah”.
Ahankali M Jameel ya maida kansa jikin kushin ɗin ya jingina kana ya miƙe ƙafafunsa tare da riƙe hannun Bashir aciki nasa kana ya cije lips ɗin sa.
Ummi kuwa wani irin sanyi jikinta da zuciyarta keyi cikin wani irin yanayi ta zubawa M Jameel Idanu.
Anutse M Jameel ya buɗe Idanunsa dake lumshe ya sauƙe akan Ummi Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da furzar da iska daga bakinsa kana yace.
“Ummi ya dai kike kallona haka kamar na ƙarshe!?”.
Cikin saurin Ummi ta dafe ƙirjinta daya buga da ƙarfin gaske cikin raunin murya irin na wanda ke gab da zub da hawaye ta kallesa karo na farko arayuwarta data fara kiran sunan sa tace.
“Haba haba Jamilu”.
Cike da mamaki ya ɗago idanunsa da suka sauya launi ya kalleta, Asma'u ma da sauri ta kalli Ummi haka ma Bashir karo na farko kenan arayuwar su da suka ji Ummi ta kira M Jameel da sunan sa.

Ummi kuwa lokaci ɗaya wasu hawaye masu masifar zafi suka fara bin kuncinta Shar-shar.
Cikin yanayin tashin hankali M Jameel ya sauƙa tare da ƙara sawa gabanta ya durƙusa tare da riƙe hannun ta cikin sanyin murya yace.
“Ummi kiya femin Ummina kiya femin kada ki zubar da hawayenki akaina Ummi me nayi miki!”.
Damƙe hannunsa Ummi tayi cikin raunin murya da alamun tashin hankali tace.
“Meyesa kake zuwa kake karya mana zuciya nida ƙannenka, kasani ayanzu kaine Inuwata kaine mafakar da muke samu nida ƙannen ka muke fakewa. Meyesa wasu lokutan idan kazo kake min wasu maganganu masu wuyar fahimta”.
Ta ida maganar hawaye nabin kuncinta.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da yin murmushi yayin da Idanunsa ke sheƙi kana yace.
“Toh Ummi inada ikon canza ƙaddarata ce? Idan son samu ne Ummi zan kasance me Kula dake har iya ƙarshen numfashi na, kuma zan kasance me saki acikin farin ciki da walwala har numfashina na ƙarshe”.
Girgiza kai Ummi tayi still Hawaye nabin fuskarta tace.
“Ko yanzu ka sanya ni farin ciki duk kan wani farin ciki da jin daɗi ka bani shi Jamilu”.
M Jameel kuwa cike da mamaki ya ɗago Idanunsa dake jiƙe da ruwan hawaye yace.
“Ummi me kika ce?”.
Cikin Muryan kuka tace.
“Jamilu nace”.
Kallonta yayi cikin rawan murya yace.
“Ummi Meyesa?”.
Hawaye na zuba daga idanunta yayin da jikinta ke tsuma tace.
“Toh me zance maka? Kana tunanin bana jinka araina ne? Kana zaton bana jinka ajikina ne?
Ban taɓa ganin wani ɗa kafin kai bafa Jamilu, kaine ɗana na farko tsatsona, jinina, mallakina, kafin inga Asma'u da Bashir da dai abu ya sameka a ace ina da ikon canza ƙaddara da zan dawo dashi kaina, domin nasan ko bayan raina zaka kula da ƙannen ka fiye da yanda zan kula da su”.

Sauƙe ajiyar zuciya tayi tare da share hawaye masu zafin gaske da suka zubo mata kana tace.
“Kaga ma min komai Jamilu, kayi min komai Jamilu. Ubangiji Allah Yamaka albarka Allah Ubangiji ya rufa maka asiri duniya da lahira Allah yasa kagama da duniya lafiya”.
M Jameel kuwa sake Matsawa jikin Ummi yayi tare da ɗaura kansa akan cinyarta hawaye masu zafin gaske suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar.
Ganin haka yasa Asma'u dake gefe ita hawaye suka shiga bin kuncinsa.
Kusa da Asma'u Bashir ya matsa tare da sanya hannu ya shiga share mata hawayen cikin raunin murya yace.
“Kiyi haƙuri Asma'u kada kiyi kuka kinga zaki ƙara karyarwa Ummi zuciya”.
Kai ta gyaɗa yayin da hawaye suka cigaba da zubowa daga Idanunta cikin sheshsheƙan Kuka tace.
“Ka gani fa Yah Jameel ma kuka ya keyi”.
Jin haka yasa M Jameel da Idanunsa ke jiƙe da hawaye ya ɗago kansa tare da sakar mata da murmushi kana yace.
“Hmmm Asma'u kinsan meyake sani kuka?”.
Kai ta girgiza still Hawaye na bin kuncinta.

Lumshe Idanunsa yayi tare da taune lips ɗin sa kana yace.
“Kada kiyi kuka saboda ke baki da abinda zai saki kuka”.
Cikin sheshsheƙan kuka ta kallesa still hawaye na zuba daga Idanunsa cikin wata raunan'niyar murya tace.
“Toh Yah Jameel me yake saka kuka Idan muna da iko zamu raba ka dashi”.
Girgiza kai yayi tare da rintse idanunsa kana yace.
“Ba zai rabu ba Asma'u tun tasowa ta aduniya bayan shekara goma sha huɗu bani da damuwar data wuce ganin Ummi bata gidan mahaifina, hankalina yana tashi akan hakan, kuma ina tunanin hakane badan faɗa da ƙaddararta ba, a'a saidai inajin maraici inajin kewar ta, inajin ciwon rashi mahaifiyata a cikin gidanmu, ina so ko yaushe Idan na tashi naga Ummi kusa dani haka zalika idan zan kwanta ya zama naje gareta taimin addu'a muyi saida safe”.
lumshe idonsa yayi yana mai jin wani irin yanayi azuciyar kana ya buɗe su tare da cewa.
“Ina so kafin naje na kwanta akowani dare in ganta kafin naje nayi bacci ina jin kamar nayi rashin komai na duniya da Ummi bata kusa dani ina jin mai zan mata na sauƙe hakkinta na uwa akaina”.
Shafa kansa Ummi tayi still hawaye nabin fuskarta kana cikin raunin murya tace.
“Toh wai meye rage da bakayi min ba? Ka kaini Makka, Ka kai ni Madina ka gina min kyakkyawan muhalli ka zuba min Kyakkyawan kayan ƙawa, ka riƙe cina shana suturata jinyata nawa dana ƙannen ka harma mijin da nake tare dashi har maƙotan dake tare dani baka barsu sun zubda hawayeba kanai musu dukkan abin buƙata”.
A hankali ta danne kukan dake ƙoƙarin sufce mata kana tace.
“Jamilu har maƙota nafa kagama yi musu komai”.
Murmushi M Jameel yayi still Hawaye na bin kyakkyawar fuskarsa kana yace.
“Har yanzu ban gama ba Ummi, sai dai ki tayani da addu'a Allah yasa in gama Allah yabani ikon gamawa”.
Sai kuma ya maida kallonsa kan Asma'u dake zubda hawaye har zuwa lokacin

47 / 140

Chapters