Author : Aisha Aliyu Garkuwa Category : Free Novels Online (Read & Download)
Idanunta Hawaye masu zafi suka zubo mata ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe kana yace.
“A lokacin sai mahaifinsa yace.
“In sha Allah a gaban idon ka nema Jameeluna ina zakaje”.
Sai yayi murumshi tare da sunkuyar da kansa murya a sanyaye yace.
“Wata ƙil kafin nan na tafi Marocco ko wata duniyar. Dan haka ga mata na zaɓawa Moddibo koda bayan bana nan Abba ayi ƙoƙari ahaɗa auren Moddibo da Khausar sai Abban sa yace to Meyesa kace haka sai yace wa Mahaifinsa shi dai yana fata kuma yana buri ahaɗa auren Moddibo da Khausar domin Moddibo yana ɓuƙatar Aure fiye dashi shiyasa ya fara yi masa zaɓin mata”.
A hankali Lamiɗo ya fesar da numfashi mai zafi kana ya cigaba da cewa.
“Sannan Marigayi Jameelu ya sanar da mahaifiyarsa maganar kana ya sanar da Kakar Moddibo maganar har ta kira Malam Arɗo ta sanar dashi maganar domin wasiyya ce alokacin yake cewa ayi ƙoƙari ayi auren cikin gaggawa domin Moddibo yana bukatar aure shiyasa yake so ayi kokari ayi auren cikin gaggawa koda baya nan babu wanda baisan da maganar ba sai Moddibo shiyasa shekaran jiya suka zo akan neman alfarma ga Uzurin da suka zo dashi”.
Sai kuma ya numfasa kana yaci gaba da cewa.
“Akan wasiyyar da yabari toh na faɗa musu lallai Nine mariƙin Khausar Kuma Khausar tamkar ƴa take awajena, saidai bani da iko da kuma ƴan cin da zan bada Auren Khausar garesu batare da izinin Yayan mahaifinta ba da kuma sahalewar kakarta”.
Gyara zama tayi tare da kallon Mommy da tayi sanyi hawaye na zuba daga idanunta numfashi ya fesar kana yace.
“Toh nace suje bayan kwanaki zasu jini, toh dana niyyata zamu je Jauro yaya muyi wa Hajja Nana bayani sannan mu faɗa mata wasiyya ne duk abinda ake ciki dama nace idan muka dawo zan faɗa musu”.
Kallonsa kawai Mommy take bako kyaftawa tana sake jin tsoron Allah Mabuwayi gagara Misali aranta cikin sanyin murya Abba ya cigaba da cewa.
“Kuma tunda kika ji Khausar ta furta haka wataƙil itama akwai abinda ta sani acikin wannan al'amarin”.
Dogon numfashi Mommy taja tare da fesarwa kana ta lumshe Idanunta hawaye masu zafi suka zubo ahankali ta sunkuyar da kanta cikin raunin murya tace.
“Allah sarki toh Ubangiji Allah ya jikansa da rahma idan al'khairi ne Allah ya tabbatar idan kuma ba al'khairi bane Allah ya sauya musu da mafi al'khairi”.
Jinjina kai Lamiɗo yayi tare da sauƙe numfashi kana yace.
“Yawwa Aysha yanzu kika gane addu'ar da zaki yi kenan, sannan kada kiyi fushi da Khausar fadan nan dakike yi bashi da amfani zama zakiyi da ita ki fahimci Meye dalilinta na fadar haka”.
Kai ta gyaɗa kana cikin sanyin murya tace.
“Toh shikenan Insha Allah zan kiyaye”.
Sai da aka kira sallar azahar Lamiɗo ya fita ya tafi masallaci kana Mommy ta miƙe ta nufi sashenta tana shiga falon ta fara jiyo sheshsheƙan Kukan Khausar abakin ƙofar Bedroom ɗinta ta tsaya tare da ɗaga labulen ta kalli Khausar ba yabo ba fallasa tace.
“Idan kin gama kukan ki tashi kije kiyi al'wala kiyi sallah”.
Cikin sanyi ta gyaɗa mata kai kana ta miƙe tashiga toilet ta ɗaura al'wala ta fito Anutse ta gabatar da sallah.
Mommy ma na shiga Bedroom ɗinta ta ɗaura al'wala sannan ta gabatar da sallah.
Bayan Khausar ta idar da Sallah kai tsaye ɗakin Mommy ta nufa.
Acan ɓangaren Hajiya Lami kuwa zaune take akan kujera taji ƙa garin magani da tsamiya da kuma ruwan zafi ta kalli Samira dake zaune gefenta ta zabga ta gumi cikin sanyi tace.
“Gashi ki karɓi maganin kisha dama wannan yace sai da rana-rana zaki riƙa sha wanda kika sha jiya da daddare kuma dare-dare zaki sha”.
Karɓan kofin Samira tayi tare da tsira masa Ido ganin yanda ta tsirawa kofin Ido yasa Hajiya Lami cewa.
“Kisha mana”.
Cikin raunin murya Samira tace.
“Mommy nifa na jiya da daddare nan ma dana sha babu abinda ya ragu saima zubar ruwan daya ƙaru”.
Ahankali Hajiya Lami tace.
“Toh Sokuwa wataƙil ruwan ai zai zube ne ya gama ƙarewa idan ya gama zuba shikenan magana ya ƙare”.
Cikin raunin da tashin hankali Samira ta kalli mahaifiyar ta da Idanunta dake cike da ruwan hawaye kana tace.
“Toh Mommy ruwan fa da ƙarni da wari yake zuba yanzu ma bakiji yanda nake ƙarni ba?”.
Cikin tsinkewar zuciya ta kalli Samira sai kuma ta basar domin bata son bawa ƴartata tsoro amma baki ɗaya hankalinta ya tashi kar dai ƴarta ta samu wata matsala numfashi ta fesar tare da kallonta kana tace.
“Ni dai banji wani wari ba hancin kine dai da shegen jiye-jiye kina nan da hanci kamar na kule ke dai kisha magani tunda yace kisha na tsawon sati biyu kafin mu koma”.
Zare ido tayi cike da tashin hankali tace.
“Mommy har sati biyu kuma?”.
Kai Hajiya Lami ta gyaɗa kana tace.
“Eh saboda zaiyi tafiya so koda munje baza mu same shiba”.
Ajiyar zuciya Samira ta sauƙe tare da cewa.
“Toh bari in sha”.
Aɓangaren Naseer kuwa zaune suke afalon Mahaifiyar sa da Addarsa Hindu da kuma Mahaifiyar su Hajiya Kubra yayin da akwatuna ke jere agabansu cikin su sanye da Atamfofi, Leshuna, Shadda, English wear, Turaruka, Mayuka,Takalma.
Gyara zama Naseer yayi tare da kallon Addah Hindu murmushi ya sakar mata tare da ɗage mata gira ɗaya kana yace.
“Insha Allah Addah Hindu burina ya kusa cika”.
Murmushi tayi tare da jinjina masa hannu kana tace.
“Ƙwarai kuwa nan da ƙanƙanin lokaci ma kuwa”.
Gyara zama Hajiya Kubra tayi tare da kallon Naseer tace.
“Toh yanzu me yarage acikin kayan Auren nan ba asaba!?”.
Ajiyar zuciya Naseer ya sauƙe tare da cewa.
“Kayan Aure kam yanzu ai kusan an gama komai kawai yanzu gishiri da goro za asiya sai kuma sadaki i think suka ɗaine suka rage”.
Kai Addah Hindu ta gyaɗa tare da faɗin.
“Eh saura kayan rufi ba ahaɗa ba”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Toh badamuwa yaushe za akai?”.
Kallon akwatunan tayi kana ta kallesa numfashi ta fesar ta da sakin murmushi tace.
“Idan Allah ya yarda nan da sati za akai saura gyalullulka dana aika akawo min daga Kano basu iso ba tukunna”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Toh ba matsala sai sun iso”.
Bayan Moddibo da Abba sun idar da sallar Azahar Amasallacin Kofar gidan Abba kai tsaye gidan Ummi suka nufa bayan sun isa Moddibo yayi Parking suka fito daga motar kana suka tsaya daga coumpund ɗin Moddibo yayi sallama daga ciki Malam Ahmad ya amsa kana ya fito ganin Abba yasa ya faɗaɗa Murmushin fuskarsa tare da cewa.
“A'a Alh Bashir yau har da kaine agidanmu sannu da zuwa sannu da zuwa maraba lale ku iso mana”.
Kai Abba ya girgiza kana yace.
“A'a nan ma yayi”.
Ahankali malam Ahmad yace.
“A'a bakomai Abban Jameel mu shiga mana ai an zama ɗaya haba dai mushiga dan Allah”.
Murmushi Abba yayi cikin sanyin murya yace.
“Toh shikenan Nagode”.
Sannan suka nufi falon Ummi Asma'u dake zaune ta miƙe tare da yi musu Barka da zuwa kana ta koma kichen ta dauki Plate ta kawo musu ruwa da drinks da kuma Fruit ta ajiye masu kana ta Gaishe su cike da ladabi.
Ahankali Moddibo ya jingina bayansa da jikin kujera ya lumshe idanunsa baki ɗaya ya tsani garin Gembulan da jahar Taraba ji yake tamkar ana yayyafa nasa garwashin wuta ajiki baiƙi ace ko yaushe yana ɗaki baya fita ko ƙofar takashi ba.
Ummi dake Bedroom zaune kan Sallaya ta miƙe ta fito jin muryan Asma'u na gaishe da Moddibo kana tace.
“A'a Moddibo ne”.
Ganin Abba zaune yasa ta tsaya cike da Mamaki tace.
“A'a Alhaji Bashir”.
Cikin sanyin murya Abba yace.
“Na'am Fatima”.
Kallonta Malam Ahmad yayi sanye take da hijabi har ƙasa hannunta riƙe da Carbi cike da kulawa yace.
“Ki ƙara so mana ku gaisa”.
Kai ta gyaɗa tare da ƙarasawa ta zauna daga gefe.
Anutse Moddibo ya daga kai ya kalleta kana yace.
“Ummi ina yini”.
Kallonsa Ummi tayi ba tare data amsa gaisuwar ba tace.
“Babana jiya duk baka leƙoni ba”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.
“Eh Ummi”.
Cikin sanyin murya tace.
“Kuma na kira wayarka baka ɗaga ba sai nayi tunanin ko kana bacci ne?”.
Kai ya girgiza tare da sunkuyar da kansa ƙasa yace.
“Kuma Ummi ban kulaba ban miss call ɗin ba”.
Jinjina kai tayi tare da fadin.
“Ayyah”, Kana suka gaisa.
Anutse Abba ya kalleta tare da cewa.
“Fatima ina yini”.
Ahankali ta gyara zamanta tare da faɗin.
“Lafiya”.
Cikin sanyin murya yace.
“Ya muka ƙara ji da haƙuri”.
Lumshe Idanunta tayi kana tace.
“Haƙuri ya zama dole”.
Jinjina kai yayi tare da cewa.
“Toh Allah yajiƙan Jameelu Ubangiji ya masa rahama”.
Baki ɗayan su suka amsa da Ameen ya Allah.
Gyara zamansa yayi kana yace.
“Fatima kada ki yiwa Jameelu kuka ki tayi masa addu'a shine abinda ya dace kinji ko?”.
Kai ta gyaɗa tare da sunkuyar da kanta ƙasa tace.
“Insha Allahu bazan yiwa Jameelu na kuka bai Insha Allah zan ta binsa da addu'a”.
Kai ya gyaɗa tare da faɗin.
“Hakan yafi”.
Anutse ya gyara zamansa tare da kallon Moddibo da kansa ke ƙasa kana ya kalli Ummi da itama still Kanta ke ƙasa ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.
“Dama nazo da Moddibo ne inne ma masa uzini awajenki”.
Cikin sauri ta ɗago kanta tare da Kallonsa tace.
“Izinin me kuma?”.
Numfashi ya fesar tare da cewa.
“Dama Abune da yashafi kasuwanci na acan Company mu na Marocco wanda Jameelu ne yake komai na Company nin toh kuma yanzu kin gani Allah ya dauke mana Jameelu”.
Cikin sauri Ummi ta lumshe Idanunta tare da gyara wuyan hijabinta.
Abba ya cigaba da cewa.
“To Kuma Manager company shima ba shida lafiya toh sun nemi da Inje kuma nima bana jin daɗin jikina bazan iya zuwa ba”.
Ahankali Ummi ta ɗago kanta tare da kallon sa gani tayi baki ɗaya ya rame ya zama wani so silent dashi.
Cikin sanyin murya da tausayawa tace.
“Toh Abban Jameel Idan bamu sa haƙuri aranmu ba ya zamuyi ka kwantar da hankalin ka Ubangiji Allah yajiƙan Jameelu shine kawai fatan mu da addu'ar mu”.
Kai ya gyara tare da sauƙe numfashi yace.
“Insha Allah zan kiyaye.
Yanzu mshawan jinin ne baki ɗaya yasani agaba duk kan magungunan da nake sha sai yazama kamar basa min aiki”.
Jinjina kai tayi cikin sanyin murya tace.
“Allah ya sawwaƙa amma ka rage tunani koda kana shan magani idan baka rage tunani ba ba zaiyi aiki ba”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana yace.
“Toh Fatima ya zanyi idan banyi tunani ba!?”.
Ahankali ta sunkuyar da kanta hawaye na zuba daga idanunta.
Gyara zama Abba yayi cikin sanyin murya yace.
“Toh dama shine nake so Moddibo ya wakilceni yaje shine yake cemin bawai zuwan bane baya so amma baya so yayi nesa da Umminsa”.
Ahankali ta ɗago Idanunta dake jiƙe da ruwan hawaye ta kalli Moddibo murmushi tayi kana tace.
“Ba komai Babana kaje wannan ma ai abin farin ciki da al'fahari ne zaka cika burin da Jameeluna yake son cikawa. Ubangiji Allah yakai ka lafiya ya dawo da kai lafiya Allah ya maka albarka”.
Cikin sanyin murya da tausayawa Moddibo ya amsa da Ameen asaman laɓɓansa.
Ahankali Ummi ta cigaba da cewa.
“Insha Allah zanyi ta binka da addu'a ba komai Babana ai muna tare ina nan ina Marocco amma idan ya gama zai dawo ko?”.
Ta ƙarasa maganar ta sigar tambaya tana kallon Abba.
Kai Abba ya gyaɗa mata kana yace.
“Eh zai dawo Insha Allah bazai wuce sati biyu”.
Jinjina kai tayi tare da kallon Moddibo kana tace.
“Badamuwa Babana ai zamu nayin waya”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Shikenan Ummi ba matsala tunda kin amince.
Murmushi tayi still Idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Na amince Babana Allah Ubangiji ya kaika lafiya Allah ya dawo da kai lafiya Allah yasanya alkhairi da albarka acikin tafiyar.
Ahankali yace.
“Ameen Ummi”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauke tare da kallonta kana yace.
“Yanzu kuma sai batun kuɗin ku da aka har haɗa”.
Sunkuyar da kai Ummi tayi Atake hawaye suka cigaba da zubowa daga Idanunta cikin raunin murya tace.
“Toni me zanyi da kuɗin nan ne Abban Jameel?”.
Kai Abba ya Girgiza cikin rawan murya da rauni yace.
“Toh nima ɗin idan kun barsu awajena me zanyi dasu ga kuɗin Aliyu ga naki kowa ya karɓi kuɗin sa kowa yana da bukatarsa motar ki da Sarƙoƙinki kika siyar ki sayi wata mota amfani dashi”.
Kallonsa ya mayar kan Moddibo kana yace.
“Kaima Moddibo ka karɓi kuɗin ka ka sayi mota sannan sauran kuɗin kayi abinda ya dace dasu”.
Kai Moddibo ya girdiza ciki rauni yace.
“Abba me zanyi da kuɗin?.
Ai kuɗi na gama abinda ya dace inyi dasu Babu abinda zanyi dasu tun da har basu tseratar min da J ɗina ba wani amfani zasu yimin?”.
Cikin rauni Abba yace.
“Bakomai Moddibo ka karɓi kuɗin nan idan ka barsu awajena kun barmin tashin hankali da damuwa”.
Jinjina kai Malam Ahmad yayi tare da faɗin.
“Kuyi hakuri duk kan tsanani yana tare da sauƙi addu'a kaɗai zamuyi wa Jameelu amma kamar yanda yace ne Moddibo ka karɓi kuɗin nan sannan kema Fatima ki karɓi kuɗin na shine abu mafi a'ala”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.
“Yawwa shine dai ki bani account number inyi Miki transfer”.
Kai Ummi ta shiga Girgizawa hawaye na kwaranya daga Idanunta.
Ganin haka yasa Malam Ahmad ya karbi wayarta tare da fito da account number ya faɗawa Abba Atake Abba ya mata transfer kuɗinta Naira million goma da dubu ɗari takwas kasancewar yana da account number Moddibo Shima Atake ya Masa transfer kuɗinsa.
Anutse ya gyara zamansa tare da Kallonsu cikin sanyin murya yace.
“Nagode da halarcinku agareni musamman ma kai Moddibo Allah Ubangijin ya biya da mafificin alkhairi”.
Atake Moddibo yaji wani irin rauni ya mamaye sa kallon Abba yayi muryarsa na rawa yace.
“Abba akan J ne kake min godiya?”.
Numfashi Abba ya fesar tare da sauƙe ajiyar zuciya yace.
“Toh Aliyu ya zanyi kayi min halarci duk kan inda Aboki na gari ya cika ka cika Ubangiji Allah yasaka da alkhairi Nagode da halarcin ka”.
Cikin raunin murya Moddibo yace.
“Ameen Abba”.
Kallon Ummi Abba yayi kana yace.
“Toh insha Allah sammako zaiyi ya tafi kinsan akwai tazara tsakaninmu da Adamawa kuma can zai shiga jirgin zuwa Abuja”.
“Toh Allah ya kaimu Allah yakai ka lafiya Babana Allah ya kareka”.
Cikin sanyin murya yace.
“Ameen Ummi”.
Miƙewa Abba yayi tare da cewa.
“Toh bari mu tafi”.
Godiya suka masa har sun fita Ummi ta miƙe tare da bin bayansu abakin barandar ta tsaya tare da cewa.
“Babana amma ai zaka dawo daddare muyi sallama ko?”.
Jinjina kai yayi kana yace.
“Insha Allah Ummi zan zo”.
Bayan sun fita kai tsaye gidan Malam Arɗo Abba ya ajiye Moddibo zaiyi masa sallama kana Abba ya wuce gida.
Cikin sanyin jiki Khausar ta isa Bedroom din Mommy, a hankali ta zauna agabanta cikin Muryan kuka tace.
“Mommy kiyi haƙuri kada kiyi fushi dani”.
Tsira mata Ido Mommy tayi ba tare da tace Uffan ba.
Cikin raunin murya Khausar ta haɗa hannunta waje ɗaya kana ta fashe da matsanancin kuka da sheshsheƙan tace.
“Mommy dan girman Allah kiyi haƙuri ki daina fushi dani”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da fesar da nunfashi kana tace.
“Khausar to ni me zan ce miki?.
Bani da abinda zan ce miki tunda ai hukunci ne kin riga da kin gama yanke shi baki nemi shawarata ko izinina ba”.
Girgiza kai Khausar tayi hawaye na cigaba da kwaranya daga Idanunta.
Ita kuwa Mommy kauda kayi tayi gefe kaba ta cigaba da cewa.
“Kawai kin fadi maganarki gaba gaɗi, sannan koda akeɓance baki taɓa faɗa min tsakanina ni dake ba, sai da kika zaɓi cikin mutane sannan kika faɗa saboda ki kunya tani kin bani mamaki ban taɓa zaton haka daga gareki ba”.
Khausar kuwa kai take Girgiza cikin muryan kuka mai gunji kana Muryanta na rawa tace.
“Mommy nima ina tsoron Modibbo bafa, dan nasan baya sona”.
Kallonta Mommy tayi cikin da mmki ta tsareta da ido tare da cewa.
“Toh kina tsoron Auren Moddibo kuma, akan wani dalili zaki ce zaki Aureshi? Kuma bayan kina sane baya sonki”.
Sunkuyar da kai ƙasa tayi cikin gunjin kuka ta lumshe Idanunta tare da taune Lip ɗinta cikin raunin murya tace.
“Mommy wasiyyar Yah Jameel ne Yah Jameel ne ya roƙi al'farma awajena sannan tun lokacin daya faɗa min yace min wasiyya ya barmin yace koda ya mutu kada in manta ya nemi wannan al'farma awajena”.
Sai kuma ta kasa ci gaba da mgnar sakamakon kuka da yaci ƙarfinta hannu ta sanya ta goge hawayen fuskarta wani na sake zubowa Muryanta na rawa ta cigaba da cewa.
“Aranan da za'a ɗauke Yah Jameel bayan mun taho amota yace min yana neman alfarma awajena in na ɗauka Alfarman da yake nema awajena tamkar wasiyya ce".
Sai kuma ta kife kanta kan cinyar Mommy tana mai sakin wani irin raunataccen kuka murya na karkarwa taci gaba da cewa.
“Mommy a ranar a gabana Yah Jameel yayi ta kuka kamar yaro ƙaramin ya rinƙa haɗani da Allah da Manzonsa cikin sanyin murya da neman alfarma yace dan Allah kada ince bazan yi masa ba yana so koda bayan Ransa in Auri Moddibo”.
Kallon ta kawai Mommy keyi bako ƙyaftawa yayinda itama hawaye ke zubo mata.
Cikin sheshsheƙan Kuka Khausar ta lumshe Idanunta tana tuna lokacin da suka kasance da M Jameel amota yana faɗa mata magana da sauri ta sanya tafin hannunta ta rufe fuskarta kana muryanta na rawa tace.
“Mommy alokacin Cike da damuwa na kalli Yah Jameel nace ya Jameel Meyesa kake Fadar haka Meyesa kake magana me karyar da zuciya dan Allah kada kace wasiyya nidai ka faɗi ko wace irin alfarma kake so zanyi maka domin kafi ƙarfin alfarma awajena”.
Taja hanci tare da kallon Mommy da yanayin ta ya sauya Muryanta na rawa kana numfashinta na fusga tace.
“Sai yace min Khausar koda ace kin riski labarin mutuwa ta ki tuna da Alfarman da kuma Wasiyyar da na bar miki ki Auri Moddibo idan kuma Allah yasa ina raye zanfi kowa farin cikin ganin An ɗaura Aurenki da Moddibo”.
Ahankali Mommy ta sun kuyar da kanta ƙasa cikin wani irin yanayi na tsananin tausayawa da kuma tsoron Allah Mabuwayi gagara Misali tol-tol haka hawayenta ke zuba jin Khausar taci gaba da cewa.
“Mommy Yah Jameel ya faɗa min cewa ya fadawa. Kakar Moddibo cewa dan Allah ayi Aurena da Moddibo Mommy dan girman Allah ki tayani cikawa Yah Jameel Wasiyyar daya barmin bani da abinda zanyi masa a wannan duniyar wanda zaisa Yah Jameel farin ciki amakwancinsa sama da in cika masa burinsa naji na gani zan rayu da Moddibo duk da nasan ya tsaneni zan rayu dashi sabida darajar Yah Jameel da wasiyarsa zan juri dukkan uƙubar da Moddibo zaimin koda kuwa zai kasheni zan zan cikawa Yah Jameel burinsa”.
Cikin sheshsheƙan Kuka da fisgar numfashi tace.
“Mommy wannan buri da fatan Yah Jameel ne dan Allah da Manzonsa ku barni in cika masa burinsa, tun da muke rayuwa da Moddibo Amakaranta yace ko yaushe kallon mu yake amatsayin mata da miji yace bashi da