Author : Aisha Aliyu Garkuwa Category : Free Novels Online (Read & Download)
kukan wani mutun.
Da sauri ya juyo kan zaburarran dokin da yaji an kira da Rinƙas ɗin da yayiwa farin sani a mafarkansa.
Sai kuma ya kuma kallon dottijon da kallo ɗaya zakayi mishi kasan cikekken mahaukacine tubran.
Rinƙas kuwa wani irin gigitaccen haniniya da sukuwa mai bada sautin takunsa mai jawo hankalin mutane, yayinda daga can baya kuma mai gadin sashin dawakanne ke ihu da kururuwa tare da yin mgn cikin tashin hankali yake cewa Modibbo.
“Ka gudu! Nace ka gudu zai kasheka fa".
Sai kuma ya ƙara ɗaga murya tare da cewa.
“Sarkim Dawaki taimakon gaggawa”.
Dai-dai lokacin kuma Rinƙas yayi wani iri-iri haniniya tare da harbin iska kana ya baza gashin kan wuyanshi tare da zura ƙafafunsa na gaba suka tafi suuuwwwh kan Modibbo.
Shi kuwa Modibbo cikin tariyo yanayin da yake rayuwa da dokin a mafarkansa na tsawon rayuwarsa.
Ya ture hular kansa tare da girgiza kansa yayi yadda dokin yayi, kana ya saita ƙwayar idanunsa, cikin tsakiyar idanun dokin.
Tare da ɗaga tafin hannunsa na dama ya saita kan goshin dokin.
Wanda hakan ne kuma yasa dokin sakin wani hargitstsen haniniyar da saida ta ratsa kunnuwan tsarki da tawagarsa dake cikin fadar suna zaman yiwa Sarki Jabeer Nuruddeen Gwadabe sallama dan yau yake shirin komawa Nigeria.
Juyowa mai martaba sarki Youssef Muhammad Mouley yayi tare da kallon gefen da Sarkin Dawaki yake tare lunshe idanunsa wanda hakan kaɗai ya wadatar ya gane nufin Sarkin.
A can waje kuwa gaba ɗaya jama'ar idanu suka zubawa Modibbo da Rinƙas suna kallon sarautar Allah, shi kuwa Modibbo.
Lumshe idanunsa yayi tare da buɗasu cikin na dokin.
Wani irin ɗaga sawu sama dokin yayi alamun sarawa da kuma cikekkiyar sanayya yayi Modibbo, kana yayi ƙasa dasu a hankali ya manna goshinsa da tafin hannun Modibbo.
Shi kuwa Modibbo shafa sumar gaban goshin yayi tare da fesar da sassayyan numfashi.
Mutumin dake gefen sane yayi wani irin sake baki tare da furta Yah Salam.
Dan sai lokacin ya samu damar ƙarewa fuskantar Modibbo kallo.
Dokin kuwa cikin nuna alamun shaƙuwa da sanayya mai tarin yawa, ya rinƙa karkaɗa jelarsa tare da baza gashin wuyansa da sakin haniniya kana ya fara zaga Modibbo tamkar maiyin ɗawafi.
Shi kuwa Modibbo wani irin mataccen murmushi yake tare da jujjuyawa yana kallon duk inda dokin yayi.
Saida ya zagayashi sau uku, sai kuma ya dawo gabanshi.
A hankali ya sunkuyo haka yasa Modibbo sumbatar wuyan dokin.
Dai-dai lokacin kuma sarki Dawaki ya buɗe ƙofar fadan ya fito da sassarfa ya fara taka steps din.
Shi kuwa Modibbo ɗan buge goshin dokin yayi sai ga dokin yayi ƙasa a hankali ya kwanta tare da karkarɗa jelarsa alamun so yake Modibbo ya hau kanshi.
Ya ilahi ya mujibatda'awato. Yah Salam, shine kaɗai abinda gaba ɗaya al'ummar dake kewaye da bishiyoyin suka fara faɗa tare da sauƙowa suka nufo Modibbo.
Shi kuwa Modibbo gashin saman wuyan dokin ya kamo tare da ja,
Haka yasa dokin miƙewa tsaye cike da biyayya.
Shiko Modibbon a hankali ya lumshe idanunsa, sai kuma yayi gaba dokin na biye dashi tamkar raƙumi da akala.
Duk da babu linzami a wuyan dokin.
Shi kuwa Modibbo ido a lumshe ya juya gefen hagunsa ya fara tafiya yana mai kallon taswirar hanyar inda zaije ya ɗaure dokin na dawo masa filla-filla kamar yadda yake gani a mafarkansa.
Wannan al'amari yayi masifar sa mamaki da kaɗuwa a zuƙatan al'ummar waje.
Dr Jameel kuwa ido ya zubawa Modibbo.
Yayinda sauran Hadiman kuwa gaba ɗaya hannun suka rinƙa ɗaurawa a ƙirzansu suna ɗan ronƙofowa kaɗan sunayiwa Modibbo wani irin gaisuwar ban girma.
Sarki Dawaki kuwa cike da al'ajabi da ta'ajjudin ganin yadda wani ke sarrafa Rinƙas ban ya sani duk duniya shida Abualeey ne kaɗai ke iya sarrafa dokin wato sarki Youseef, ko Ibrahim Mouley baya matsowa kusa dashi, kana ya sani kusan mutum uku ya kashe a cikin masarautar.
Hakane yasa ya fara sassarfa, amman ina ya kasa iso Modibbo da dokin domin shima da sassarfan yake tafiya ganin dokin na sonyin sukuwa.
Kana gaba ɗaya mutanen kuma yuuuh sukayi suka bi bayan Sarki Dawaki domin al'ajabin wannan al'amarin.
Tafiya mai nisa sukayi kana Modibbo yayi kwanan gefen yamma nan ma tafiya mai tsawo sukayi kana suka ɓullo kan wani ƙaton farfajiya wanda a ƙalla dawakai sun kai ɗari uku zuwa huɗu ke wurin.
Duk inda ka wulga idonka iya ganinka dawakaine a wurin. Shi kuwa Modibbo wata yalwatacciyar hanya yabi tare da ratsa tsakiyar dawakan ya wuce.
“Iko sai Allah”. Mutumin nan dake ya shelanta tsinkewar Rinƙas da gudu ya nufosu tare da maɗaukakiyar mamaki a fuskantar.
Shiko Modibbon ratsawa ya rinƙayi har ya isa inda nanne tirken dokin. Ɗaureshi yayi kana ya juyo.
Juyowarsa kuwa itace tasa numfashin Sarkin Dawaki kusan ɗaukewa a fili yace.
“Yah salam”. Sabida ganin kamannin fuskantar Modibbo tayi masifar girzashi, kawai sai ya ɗaura hannunshi na dama kan ƙirjinsa ya ɗan rusunar da kai, yayinda gaba ɗaya sauran ma haka sukayi.
Shi kuwa Modibbo ratsasu yake a hankali tare da bin hanyar da bata nan ya zo ba, tafiya kaɗan yayi ya ɓullo kan fadar.
Wanda tuni wasu hadiman sun kuma maye gurɓin waɗancan da suka tafi wurin dokin.
Jiyo alamun takun mutanene yasa ya ɗan juyo, ainkuwa zugar tawagar da ya barine suke biye dashi cike da girmama.
Bai fahimci komaiba a cikin abinda suke mishi, kawai dai yana bin hanyoyin da ya saba gani a mafarkansa ne, hakan yasa ya fara taka steps ɗin.
Da sauri wanda yake bakin ƙofar ya tura ƙofar tare da sa hannun sa ɗaya a ƙirji ya ɗan rusunar da kai, ɗai hannun kuma yayi masa alamun bismlillah ga hanya ka shiga.
A hankali yake takun cike da kamala da haiba, ya kutsa kanshi cikin tamfatsestsen falo na al'farmar da ƙasaita. Wanda komai na cikinsa ja ne, sai ratsin baƙi, bisa alamu kalan tutar ƙasarsu ce.
Babban falone wanda a ƙalla zai iya ɗaukan mutun sama da ɗari.
Yana shiga Sarkin Dawaki na biye dashi a baya.
Da sauri ya kalli gefen damanshi jin muryar yaron nan da suka haɗu a jirgi na cewa.
“Alhamadullah Abeey kaga ga wanda nacema mun haɗu dashi a jirgi, mai kama da Ibrahim”.
Faɗin hakane yasa duk suka kalleshi sai kuma suka kalli inda yake nuna musu.
Da sauri wani Kekkyawan Mutun mai cikar haiba, kamala, haɗi da ƙasaita ya miƙe tsaye cikin shiga ta al'farmar dake nuni da shine Sarkin masarautar ƙasar Marocco.
Miƙewarsa tsayence tasa dukkan sauran mutanen kama daga Waziri, Galafima, Wambai, Ɗan Maliki, Sarkin gida, Sarkin fada, dama gyara kimtsi Sarkin zagi kab suma suka miƙe tsaye cike da zubawa Modibbo idanu tamkar zasu ɗagashi sama da idon.
Dr Jameel kuwa, muƙut ya haɗiye wani yawu mai haɗe da mmki dan jarabar neman mata shi bai barshi yayi wani tunani kan kamannin Modibbo da Ibarahim ba koma yace da kawunshi ba.
Sai kuma yace.
“Har nan”.
Moddibo kuwa Jabeer bin Jabeer daya dawo gabanshi yana miƙa mishi hannu ya zubawa ido tara da bashi hannun.
Shiko Jabeer jawoshi yayi har zuwa gaban Sarkin tare da cewa.
“Ganshifa ko makaho ne ya shafa fuskarsa ya shafa taka ko ta Ibrahim yasan wannan mallakinmu ne shi, Abeey ba dama na gaya makaba”.
Ya ƙare mgnar da kallon Sheikh Jabeer .
Shi kuwa Sheikh Jabeer wani Gwauron numfashi ya fesar tare da yiwa Ɗan aminin nashi nuni daya zauna.
Cike da kaɗuwa Sarkin Mouleey ya zauna kana yayiwa dukkan fada alamun su zauna.
Haka kuwa duk suka zauna.
Dr Jameel ne ya ɗanyi gyaran murya tare da rusunar da kai cikin ladab yace.
“Ayi min izini in tashi zan shiga wurin Didi in duba Rahman".
kai Sarkin fada ya gyaɗa masa tare da nuna masa hanya alamun yaje.
Cikin sauri Dr Jameel ɗin ya miƙe da tare da kamo hannun wani ɗan yaron da bazai gaza shekara gomaba yace “Muje”. Ya ida maganar tare da jan hannunsa suka juya zasu fita.
Da sauri Modibbo ya miƙe tare da bin bayan Dr Jameel.
Cike da mmki ya tsaya ganin fadawan da suka zagayeshi da sauri kana sunkayi mishi zobe tare da baza manyan rigunansu.
Suka tareshi baya iya ganin Dr Jameel.
Cikin sanyin murya yace.
“Yah haka Ku buɗe min hanya mana zan tafi”.
Da sauri ya juyo jin Muryar Sarkin Zagi na cewa.
“Gyara kimtsi bisa umarnin mai martaba kuyi mishi jagora sashi na musamman”.
Kafin ya fahimci mai kalaman Sarkin zagin ke nufi, sai ji yayi anja hannunsa ba tare da an cire ƙawanyar da ankayi masaba, yaji sun fara tafiya dashi.
“Ikon Allah wai na zaune ya daɗi".
Shine abinda yake faɗi a ransa yana mai ƙoƙarin ɗago kanshi sama, wai ko zai samu yaga gabanshi amman ina.
A hankali ya fesar da numfashi sabida tariyo masa da mafarkansa da kwakwalwarsa tayi masa.
Taku yaci gaba dayi da bin sawun Sarkin gida dake jansa wanda ta cikin ƙaton falon sukabi ta wata babbar ƙofa, tafiya mai tsawo sukayi kana yaji sun fara hawa steps jim kaɗan kuma yaji sun ɓulo ta wata kusurwar, ɗan gajeren tsaki yaja.
sabida jin tafiyarfa taƙi ƙarewa, kuma mutumin nan yayi mishi riƙon babban ɓarawo, ga ƙattin fadawa da suka zagayeshi.
“Toh wai me haka”.
Ya faɗa dai-dai lokacin da yaji, an ajiyeshi bisa wata ƙasaitacciyar kujera.
Sai kuma yaga duk sun janye ƙawanyar da sukayi mishi kana suka juya suka fita.
Da ido ya rakasu har suka je bakin ƙofa ga mmkinsa sai yaga mutumin nan da ya riƙo hannunsa yaja ƙofar da ƙarfi ya ruf....
Muje zuwa, wasa ya jiƙa, karatu dan aka biya kuɗin laranra Littafin yafi ɗadi ba haƙƙin kowa a kanki 1k ne fa kacal ki biya kada ki kiranta na sata 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 ki biya in tura miki littafin ki karanta abinki cikin Salam kana in saki a Group ɗin littafin kusha comments,
Tallah !! Tallah !!
Shahararriyar Marubuciyar nan Ikilima Adam (kyauta daga Allah) wacce ta nishadantar daku a littafin ta mai suna *Kanwata* , yau ta sake dawo muku Domin tallata muku Littafin mai Suna ( Rai Daya Jan Zaki) littafine mai kunshe da Butulci , cin amana ,zagon Kasa , soyayya irin ta gani kasheni , aminci da saura n su basai n'a cika Ku da surutu ba Hausawa sukace Gani yakori ji.
Farashin wannan littafin Naira Dari biyar ne 500 kacal postin biyu a arana banda ranar Juma'a .
Domin Karin bayani Ku tuntubeni a lambata kamar haka (09069080725 ko Kuma + 22953726162 ) wacce Bata shirya Siya ba kada mu batawa juna lokaci.
Domin aikawa da kudi kai tsaye . 3115484026 ikilima Adam first bank
Turo shaidar biya akan wannan 09069080725 sai najiku.
By
*GARKUWAR MARUBUTA*SAKAYAH
42
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*TSAYA! TSAYA!!! NACE ki TSAYAKO Sister's* duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing, gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai ba🤗nd wanan new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku, domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso ga number's ɗin da zakuyi mgn bani AYSHA ALIYU GARKUWA, zakuyiwa mgn ba, gaban 👇🏻👇🏻👇🏻Ga ta inda zakuyi magana Whatsapp
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare
Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai na amare special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin keda kanki zaki shaida cewa fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549
Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free
Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏
Cike da matsanancin mamaki Moddibo ya tsirawa ƙofar da suka rufe ido, toh shin me hakan yake nufi, gwauron numfashi ya fesar yayin da abubuwa da yawa suka riƙa dawowa cikin ƙwaƙwalwarsa, cikin kasala ya jingina bayansa da jikin kujeran kana ya buɗe manyan idanunsa da suka sauya launi.
Ahankali ya shiga ƙarewa tsarin falon kallo, falone mai masifar girma da kyau tun daga farkon falon yake ɗauke da wasu lumtsa-lumtsan kujeru 4couner tun daga farkon Falon har ƙarshesa kujerune zagaye dashi ya kasance kalan Golden ne da ratsin milk kana da ɗigon Coffe ga wasu trust pillow kalan Golden da suka sake ƙawata kyawun kushin ɗin yayin da ƙasan falon ke mamaye da wani lallausan Darduma kalar Golden da ratsin milk kana da ɗigon Coffe daga can saman P.o.p kuwa wasu irin Gloves ne da akayi musu dising na ƙawa da alfarma, yayin da Labulayen suma suka kasance kalan Golden ɗin, daga tsakiyar Falon kuwa wasu stool ne masu azabar kyau guda biyu ɗaya daga farkon falon ɗaya kuma daga ƙarshe kuma jikinsu duk akwai ƴan ƙananan stoll guda huɗu, wanda za'a iya jansu, iya tsaruwa falon ya tsaru kana sai can gefen daga gefe kuma dinning area ne mai ɗauke da dining table shima komai goldie ne, sai daga gefen dama can wata ƙoface dake da ƙawanyar labule, hakama gefen hagu falo ne na al'farmar kai da ka gani kasan babu ƙaranta a cikin lamarin tsarin komai a fili zai nuna maka anci uban kuɗi a Masaarautar daga can tsakiya wani shunfiɗeɗɗen steps ne mai faɗi wanda ake shimfi tattausan Carpet na al'farmar busa alamun akwai wuri na musamman a saman.
Cikin fesar da numfashi ya riƙa juya idanunsa lungu da saƙo na cikin falon, kafin ahankali idanunsa suka sauƙa akan wasu jerin hotuna masu yawa.
Ware idanunsa yayi ganin wani kyakykyawan Matashi mai masifar kama da shi tamkar an tsaga kara babu abinda ya raba sa dashi yana cikin shiga ta al'farmar dake nuni da rainon masarautar ce.
A hankali kuma ya dire idanunsa bisa hoton dake gefen.
Wannan mutumin daya gani a fada ne amatsayin Sarki sai kuma wata kyakykyawa mata mai matsakaicin shekaru.
Zazzafan Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da maida idanunsa dake lumshe kan wasu kyawawan mata su uku biyu daga ciki zasu girmeshi ɗaya daga cikin kuma da alamun itace ƴar auta sai kuma hoton wani Kekkyawan jariri da aka ɗaura saitin cinyar Sarki, sai dai bisa alamu haɗa hoton akayi.
Suna zagaye da iyayen nasu, sai kuma ya maida idanunsa kan hoton dake gaba...
Cikin sauri ya miƙe tsaye murya ɗauke da tsananin mamaki da kaɗuwa gami da al'ajabi ya motsa Pinch lips ɗinsa tare da faɗin.
“Innayi”.
Ganin hoton Innayinsa ɓaro-ɓaro tare dana wannan ahalin duk da kuwa cewa alokacin tana da ƙarancin shekaru bai hanashi ganeta ba, ko dan yasan hoton a wurinta ne, dan tabbas tana da hoton wanda kuma hannunta ke riƙe da jariri fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi wanda kuma ta sha faɗi mishi shine a hannunta a ranar da anka haifeshi akayi musu hoton.
Yatsunsa biyu na yasa ya murza idanunsa ganin ko mafarki yake.
Cikin bugawar zuciya yace.
“Wannan fa innayi ce ba gizo idanuna kemin ba”.
Cikin tsananin al'ajabi ya furta.
“Ya salam Abun Al'ajabi”.
Kafin ahankali ya ɗaga ƙafafunsa da yaji sunyi masa mugun nauyi ya nufi jikin hoton, yayin da ƙwaƙwalwarsa ke tariyo masa cewa tabbas Innayi nada wannan hoton awajenta.
Da sauri ya dafe kansa tuno kalmarta agaresa da take cewa Kaje sai nazo.
Hannunsa duka biyu ya Sanya tare da dafe kansa lokaci ɗaya abubuwa da yawa suka shiga dawo masa ƙwaƙwalwarsa kama daga abubuwan da yake yawan mafarkinsu, atsawon rayuwarsa wanda tunda ya shigo masarautar nan yake ganinsu ra'anul ayn.
da kuma irin kalaman da Innayi ke masa wasu lokuta kana da tsananin kamanninsa da yaron dake jikin hoton da kuma Sarki wanda Babu bancin dake tsakaninsu wanda zai iya nuna cewa ba mutum ba ɗaya bane, sai dai shekarun da Sarkin yake dashi wanda shi kuma nashi basu kai haka ba kana hatta ƴan matan dake zagaye da hoton suna tsakanin kama dashi.
Zazzafan Ajiyar zuciya ya sauƙe akaro na barkatai kana ya tsirawa farcen hannun mutanen dake jikin hoton idanu wanda baiyi fari tasss ba yayi kalan ruwan ƙasa-ƙasa wanda haka shima nashi yake.
Kansa ne ya shiga juyawa cikin tsananin tarin mmki a zuciya yashiga jada baya yana tafiya da baya da baya har ya isa jikin kujeran da aka ajiyesa da farko kana ya runtse idanunsa kansa ya dafe da hannunsa na dama ya fara tunani.
“Shin me yake faruwa dani? Me hakan yake nufi? Ina ne nan? Toh menene haɗina dasu? Meyesa suka kawoni nan suka rufe ni? Meye nufinsu? Shin ko dai mafarkaina gsky ne?.”
Tambayoyin da yake yiwa kansa kenan.
Cikin sauri ya janye hannunsa dake kansa ya shiga laluma aljihunsa da niyyar ciro wayarsa dan ya kira Innayi. sai yaji wayam iska ya furzar mai zafi tuno cewa ya barsu acikin amota...
Acan cikin gida kuwa wani hamshaƙin falone me masifar kyau da tsari wanda yaji komai na more rayuwa daga can tsakiyar falon kuwa wata kyakykyawar Matace wacce take cikin hoton da Moddibo ya gani Hakimce akan wata kujera ta alfarma.
Yayinda ƴaƴanta ke zagaye da ita a hoton, sunlma suna gefenta sai dai Ba Ibrahim kana babu Rahma, bisa alamu hira suke cike da shaƙuwa.
Cikin nutsuwa Dr Jameel suka kutsa kai cikin falon da sauri yaron da Dr Jameel ke riƙe da hannunsa ya janye kana ya nufi gaban matar tare da riƙo hannunta da cewa.
“Didi kin san wani abu kuwa".
Cikin kula da so irin na kakannin a kan jikokinsu ta girgiza mishi kai tare da cewa.
“Toh Sarkin fada, me ka gano kuma, dan na lura in kunzo dai kana son zaman fada”.
Da sauri ya zauna gefenta tare da cewa.
“Didi wlh yanzu na ga wani mai kama da Uncle Ibrahim sai kingani kamarsa ɗaya da Uncle Ibrahim.
Sai dai shi yafi Uncle Ibrahim tsawo da kyau amma Didi babu abinda ya raba su da ace Uncle Ibrahim zai ɓata toh wlh wannan za'a ɗauka ya maye gurbinsa”.
Cikin sauri da bugawar zuciya. Didi ta kalli Dr Jameel kana tace.
“Jameel waye shi?Akan wayake Hakim ke magana?”.
Ajiyar zuciya Dr Jameel ya sauƙe tare da zama akan Lallausan Darduman dake malale ƙasan tiles ɗin kana yace.
“Kai Didi gsky nima abin nan yaban mamaki.
Didi yau tsawon kwana huɗu kenan yake bibiyata bansan shiba amma tun ranan farko dana fara ganinsa yana