Author : Aisha Aliyu Garkuwa Category : Free Novels Online (Read & Download)
zagin Ubana ki daina saka shi acikin wannan maganar ki barshi ya kwanta akabarinsa cikin nutsuwa da salama tun da dai ba wani mugun abu na aikata ba bare kiyita ihu kina son tara mana mutane”.
Cikin fushi da takaici Mommy ta Kai hannunta na dama tare da kwaɗawa bakinta mari kana ta watsa mata Harara tare da cewa.
“Rufe min baki fitsarariya mara kunya. Wallahi Khausar kin bani mamaki sam ban taɓa zaton haka daga gareki ba agaban idanun mu Khausar yaushe kika zama haka ni zaki kunyata?”.
Da sauri Khausar taja baya tare da fashewa da matsanancin kuka me tsuma zuciya.
Cikin sanyi Lamiɗo ya kalli Khausar dake kuka tamkar ranta zai fita kana yace.
“Khausar tashi ki tafi ɗaki”.
Da gudu ta miƙe ta nufi ɗakinta, kana Dije ta mara mata baya. Khausar na shiga ɗaki ta faɗa kan gado tare da fashewa da matsanancin Kuka me tsuma zuciya da ban tausayi yayin da hawaye wani ke bin wani suna kwaranya daga Idanunta.
Acan Falon kuwa ta inda Hajja Nana ke shiga ba tanan take fita ba, baki ɗaya Idanunta sun rufe sai Masifa take zazzaga musu musamman Mommy ganin yanda take zazzaga Masifa ba Full stop bare commer yasa Lamiɗo kasa fadar abinda ke ransa cikin sanyin murya da ladabi yace.
“Dan Allah Hajja Nana kiyi haƙuri, muyi mgnar a tsanake, kinfa san shi Aure fa rabone, sannan nufi ne na Ubangiji sannan matar mutum kabarinsa, idan har Allah ya ƙadarta cewa Aliyu shine mijin Khausar to fa duk duniya idan za'a haɗu babu wanda ya isa ya raba wannan auren”.
Wani irin kallo Hajja Nana ke binsa dashi tana mai tafasa dan masifa.
Cike da ladabi da kuma sanyin murya Lamiɗo ya cigaba da cewa.
“Idan kuma har Allah bai ƙadarta cewa Aliyu shine mijinta ba, tofa babu wanda ya isa yasa hakan ya kasance, dan haka dan Allah kiyi haƙuri Insha Allah komai zai dai-dai ta”.
Girgiza kai Hajja Nana tayi tare da juyawa ta kalli Mommy da kanta ke ƙasa cikin fushi tace.
“Lallai Aysha dama irin wannan tarbiyyar kika bawa ƴarki kenan?
Yanzu mu awajen mu wace yarinya ce ta isa ta kalli tsabar idon magabatan ta tace wai ga wanda take so wannan abin kunyar har ina?”.
Cikin sanyi da alamun damuwa Mommy ke kallonta baki daya ta rasa wani kalma za tayi amfani dashi wajen bawa Hajja Nana haƙuri.
Hajja Nana kuwa ƙwaffa tayi cikin rawan murya ta cigaba da cewa.
“Tirrr da wannan rayuwa wai yarinya ƙarama kamar Khausar har tasan ta tsaya agaban manya tace ita ga wanda take so, watoma kenan itace zatayiwa kanta zaɓin mijin da zata aura.
To mu azamanin mu koda ya rinya itace Sarauniyar kyau idan magabatan ta suka zaba mata miji koda kuma shine Sarkin munin duniya haka zata zauna dashi bare me Khausar zata nunawa Aliyu?Mutumin da koda kyaune ya fita”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauke tare da gyara zaman sa kana ya tsira mata idanu yana mamakin yanda ta ɗauki al'amarin da zafi kawai dan Khausar tace Moddibo take so shine ta kafa aƙota sai kace wacce akace tayi cikin shege shi kam baiga abin tada jijiyoyin wuya akan maganar ba.
Numfashi ya fesar tare da sassauta muryarsa yace.
“Dan Allah Hajja Nana kiyi haƙuri Insha Allah komai zai dai-dai ta akwai yarinta atare da Khausar har yanzu bata mallaki hankalin kanta ba, amma bawai dan baki isa da ita bane yasa tayi magana”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da ɗago kanta kana cikin sanyin murya ta kalli Hajja Nana dake matsar kwallar da taƙi fitowa tace.
“Dan Allah Hajja kiyi haƙuri wallahi Ni kaina ban taɓa jin wannan kalmar abakin Khausar ba, sai yau da ace tun farko naji to wallahi bazan bari ya fito fili ba zan dakatar da ita”.
Wani irin kallo Hajja Nana ta watsa mata tare da ƙankance ido tace.
“Wallahi ƙarya kike Aysha Babu ta yanda za ayi ƴarki na soyayya da wani amma baki sani ba, kawai dai so kike kinuna min iyakata akan Khausar kuma kisani duk abinda zakiyi ke dai baki isa ki canza matsayina ba”.
Kai Mommy ta girgiza cikin sanyi da ladabi ta cigaba da bata haƙuri haka zalika Lamiɗo hakuri kawai suke bata.
Miƙewa Hajja Nana tayi tare da ƙankance Ido ta kalli Lamiɗo da Mommy kana ta ya mutse baki tare da cewa.
“Ni dai Wallahi Allah wannan maganar jinta nake kamar saɓon Allah”.
Cike da damuwa Mommy tace.
“Dan Allah kiyi haƙuri ki zauna. Khausar tayi kuskure amma zamuyi wa tufkar hanci”.
Cikin sauri Hajja Nana ta kalli Mommy tare da faɗin.
“In zauna fa kika ce? Inani ina zaman nan? Ina sam nikam banga wajen zama ba. Subhanallah Allah ya tsareni ai sai Girgiza ƙasa ya rufta dani aciki yarinya budurwa yarinya ƙarama har tanada tsaurin idon da zata zauna tsakanin magabatan ta masu aurar da ita, ta iya buɗe baki tace bata son zaɓin su sai zabinta”.
Ta ida maganar tare da ficewa tana mita, da korwa da kororowa haɗi da kormoto.
Cikin sauri Lamiɗo da Mommy suka bi bayanta cike da girmamawa suke bata haƙuri amma firr wannan fitinenniyar tsohuwa taƙi sauraronsu tafiya kawai take tana kumfar baki, har ta isa Farfajiyar gidan.
Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya ta fito tare da kallon Hajja Nana sai kuma ta maida kallonta kan Mommy dake aikin rarrashin Hajja Nana tana bata haƙuri tace.
“Aysha lafiya kuwa yau nakeji hayaniya naga kamar ran Hajja Nana aɓace".
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe cikin sanyin murya tace.
“Dan Allah Hajiya ki tayamu bata haƙuri fushi tayi”.
Kallon Hajja Nana. Hajiya Bunayya tayi da murmushi afuskarta tace.
“Ayyah Hajja Nana kiyi haƙuri dan Allah”.
Ko kallonta Hajja Nana ba tayi ba bare ta tanka ta ta nufi jikin mota.
Baffa Jimeta da Baffa Liman dake zaune Falon Lamiɗo kuwa jiyo hayaniyarta yasa sukayi saurin miƙewa tsaye, sai kuma suka nufi wajan jin Muryan Hajja Nana na tashi cikin sauri suka fito tsaye suka hangota jikin motar tana ta sababi kallon Baffa Liman Baffa Jimeta yayi cike da mamaki yace.
“Yau kuma waya taɓo Hajja Nana haka?".
Girgiza kai Baffa Liman yayi tare da faɗin.
“Allahu a'alam amma dai baya wuce Khausar ba”.
Suna isa jikin Motar Baffa Jimeta ya matsa kusa da ita tare da sassauta murya yace.
“Hajja lafiya kuwa me yafaru?”.
Kallonsa tayi cikin fushi tace.
“Wuce mu tafi ina Liman maza ku wuce mutafi wannan gida ba gidan zuwa bane gidan fitsararru da rashin tarbiyya”.
Dai-dai lokacin Gimbiya Dadu ta fito daga sashen ta jin hayaniyar babu walwala afuskarta ta kalli Hajja Nana tare da cewa.
“Dakata!, Mukam ba fitsararru marasa tarbiyya bane Jikar kice dai fitsararriya mara tarbiyya”.
Afusace Hajja Nana ta kalleta tare da ɗaga mata hannu cikin fushi da ɗaga murya tace.
“Keee dakata kada kice zaki faɗa min magana”.
Cikin sauri Lamiɗo ya juya ya kalli Gimbiya Dadu cikin sanyin murya yace.
“Dan Allah Mama kada kiyi magana, ki taya mu bata haƙuri baki san meye ɓata mata rai ba”.
Taɓe baki Gimbiya Dadu tayi kana tace.
“Yo aiji nayi tana haɗa mana Jami'n zuriya gaba ɗaya ne tana aibanta mu”.
Tafe hannu Hajja Nana tayi tare da ƙankance ido kana tace.
“Toh Zuri'ar taku ta arziƙi ce? Nace zuru'ar taku har wata kayan gabas ce? Kin sani dai na sani. ko kuma wata tsiyace da ita zuri'ar Mayu”.
Girgiza kai Baffa Jimeta yayi tare da cewa.
“Inalillahi Ash'sha haba Hajja Nana dan Allah kiyi haƙuri mana”.
Kusa da ita Baffa Liman ya matsa cike da rarrashi yace.
“Dan Allah Addah Hajja am kiyi haƙuri ki kwantar da hankalin ki kizo muje mu zauna”.
Girgiza kai tayi tare da faɗin.
“Inaaa zan zauna mutafi kawai nifa bazan zauna awannan gidan ba wallahi banga wajen zama ba wannan abin kunya da tashin zuciyar ba dani ba”.
Ganin yanda ta tashi hankalinta yasa Baffa Jimeta ya buɗe mata bayan mota tashiga sannan ya zagaya yashiga mazaunin Driver Baffa Liman ya zauna gefensa.
Ahankali Lamiɗo ya matsa jikin motar ta Side din da hajja Nana ke zaune cike da ladabi yace.
“Dan Allah Hajja kiyi haƙuri akan abin da ya faru”.
Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Ba komai Lamiɗo ai ba laifin ka bane, ai kai baka da laifi aciki laifin uwarta ne da ita kanta”.
Mommy Kam da kallo tabi motar har ya fice daga gidan.
Bayan sun fita Baffa Jimeta ya juya tare da kallon Hajja Nana da tayi kicin-kicin da fuska kana yace.
“Toh Hajja yanzu gida zamu tafi kenan?”.
Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Kaini gidan ƙawata Innare”.
Jinjina kai yayi kana yace.
“Toh”.
Kai tsaye gidan su Moddibo ya nufa da motar.
Acan gidansu Abba kuwa zaune yake afalonsa cikin yanayin shiru-shirun daya saba ya tallafe haɓarsa da hannunsa na dama baki ɗaya ya rame dan bai cika Lafiya ba ahankali ya kalli center table dake gabansa jin wayarsa na ruri ɗauka sunan Manager company sa dake Marocco ne ya bayyana Picking Yayi tare da kaiwa Kunnensa sannan yayi sallama.
Bayan sun gaisa Manager ya fara mishi mgn da larabci kamar yadda suka saba yace.
“Yallaɓai sabbin kaya da mukayi Order daga Chaina sun iso gaba ɗaya sannan ana bukatar kai ko ni wani ya zamana yana wajen domin aikin sabbin na'uran sarrafa Arabia Gawn da mukeson fara sabbin samfurin.
To gashi kuma ni yanzu ba na nan, kasan ina India naje aduba min lafiyar ƙafana to dole since sai an wakilta wani kafin asauke kayan aga yanayin da abubuwan suka iso lafiya”.
Jingina kai Abba yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya kana yace.
“Toh kuma gashi nima kuma ban cika lafiya ba kullum ina fama da matsanancin ciwon kai, dama can a tsarina Jameel ne zai wakilceni aiyi aikin”.
Cike da tausayawa Manager yace.
“Ayyah Allah Ubangiji ya sawwaka.
Yallaɓai sai dai a cigaba da haƙuri Jameelu kuwa Allah yajiƙan sa ya gafarta masa, amma ya kamata asamu awakilta wani tunda bana nan ga kaya sun iso gashi audugar da aka tura da Nigeria ta iso, kuma tunda tazoma bamuyi mgnar ba sabida wannan iftila'in ɓatan Jameel”.
Jinjina kai Abba yayi tare da cewa.
“Toh shikenan, amman bazan samu zuwa ba, domin nima kaina ba lafiyar bace dani amma Insha Allah zan turo Aliyu yazo zaiyi dukkan abinda ya dace”.
Kai Manager ya gyaɗa kana yace.
“Toh Allah ya bada iko dan kaya sun iso tun jiya suketa ƙoƙarin za afara aikin sauƙe kayayyakin da ayyukan su masu motocin ma sun matsa min don suna so su fita cikin Company'n dan sunce basu son su wuce kwana biyar zuwa takwas, in sun wuce haka kuma sai in za'ainta biyansu ne”.
Cikin sanyin murya Abba yace.
“Toh shikenan ba komai Insha Allah zanyi wa Moddibo magana zai zo yanzu zan kira shi in sha Allah in this week zai shigo Marocco”.
Acan gidan su Moddibo kuwa abakin ƙofa Baffa Jimeta yayi Parking din motarsa cikin sauri Hajja Nana ta buɗe Murfin motar ta fita tare da buɗe gate din gidan tashiga.
Da kallo Baffa Jimeta da Baffa Liman suka bita har ta shige cikin gidan.
Ita kuwa tana shiga tun daga ƙaramin gate da zai sadata da ɗaya sashen ta fara doka sallama tare da faɗin.
“Innare! Innare!! Innare!!!Bakya Nan ne!?”.
Cikin sauri Innayi ta fito daga ɗakinta da murmushi afuskarta tace.
“A'a wannan muryar wa nake ji kamar Hajja Nana”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh Innare nice dai”.
Murmushi Innayi tayi tare da ƙarasawa kusa da ita tace.
“A lale maraba Barka da zuwa Maraba maraba mu shiga daga ciki”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa sannan suka shiga ciki cike da kulawa Innayi ta ajiye mata ruwa da abin taɓawa Sannan ta kalli Hajja Nana dake ta cika tana batsewa tace.
“Hajjia Nana mutan maka da Madina Bismillahi”.
Girgiza kai Hajja Nana tayi kana tace.
“A'a bazan iya cin komai ba barshi kawai Nagode”.
“Meye faru kuma?”.
Girgiza kai tayi cike datakaici tace.
“Ƴaƴan zamani kai Allah ya kyauta”.
Zama Innayi ta gyara tare da cewa.
“Waya taɓoki?”.
Ƙwaffa Hajja Nana tayi kana tace.
“Hegiyar yarinyar nanne fitsararriya gantalalliyar yarinya da batasan abin da ya dace da kanta ba, ana nuna mata gabas tana ga yamma.”
Sai kuma ta fesar da numfashin kana taci gaba.
“Uyumm yarinya har an kai matakin da yarinya ƙarama ana magana tana mgna ta fetsare Idanunta ta kalli idanun Magabatan ta tace wai tayiwa kanta zaɓin mijin Aure”.
Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da kallon Hajja Nana kana tace.
“Wace yarinya ce haka”.
Cike da takaici Hajja Nana tace.
“Khausar mana”.
Cike da Mamaki Innayi tace.
“Ha'a Khausar kuma wace Khausar ɗin?".
Jinina kai Hajja Nana tayi tace.
“Eh Khausar jikata”.
Gyaɗa kai Innayi tayi tare da cewa.
“Eh na fahimta.”
Kallonta Hajja Nana tayi kana tace.
“Yanzu na fito daga gidan Lamiɗo ai”.
Cike da mamaki Innayi tace.
“Dama Khausar ɗin gidan Lamiɗo itace jikar ki?”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh itace jikata ɗin mana”.
Numfashi mai nauyi Innayi ta sauƙe tare da gyara zamanta kana tace.
“Toh ki kwantar da hankalin ki me yayi tsanani aciki?”.
Ƙwaffa Hajja Nana tayi tare da kallon Innayi tace.
“Mun zo da batun Aurenta da ɗan Uwanta, sannan dama anan cikin zuri'ar gidan Lamiɗo kin sansu Zuri'ar Mayune to wai akwai wani yaro Naseeru da yake sonta”.
Gyara zama Innayi tayi tana kallonta.
ita ko Hajja Nana ta cigaba da cewa.
“To Ni duk atunanina ma idan batason Aliyu Naseeru zata ce tana so amma wai.
Yarinya nan tace wai wani take so, saboda rainin hankali wai Uwar ma batasan da batun ba”.
Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da fuskantar Hajja Nana tace.
“Toh me abin tashin hankali kinsan zamanin da dana yanzu ba ɗaya bane, abinda aka mana muka jura na yanzu ba zasu jura ba, bama a isa ayi musu ba, bare kuma har aje matakin su ɗauka, amma yanzu kisha ruwa ranki yayi sanyi tukun”.
Numfashi Hajja Nana ta fesar kana tace.
“Wallahi baki daya a fusace nake yarinya tayi matuƙar ɓata min rai ta fusata min zuciya ni zata wa tsawa ƙasa a ido.
Baffanta yayi tattaki gari ya garara yazo amma tace bata son ɗan sa saboda bata da mutunci”.
Innayi kuwa ruwa ta miƙa mata tare da cewa.
“Ke dai kisha ruwa zuciyarki yayi sanyi”.
Karɓa tayi tare da kafawa abakinta ta fara sha
Acan Falon Moddibo kuwa zaune yake akan Sallaya bayan ya idar da sallar Walha hannunsa riƙe da Alkur'ani yana karanta suratul Tauba yana Aya ta ɗari da ashirin da bakwai yaji wayarsa na Vibrating Kallon screen ɗin wayar yayi ganin sunan Abba yasa ya cigaba da karatun kasancewar saura Ayoyin biyun ƙarshe yasa ya cigaba yana ƙarasawa ya shafa addu'ar dai-dai lokacin wani sabon kiran ya sake shigowa.
Anutse ya ɗaga wayar tare da kaiwa Kunnensa yayi Sallama.
Cikin sanyin murya Abba ya amsa tare da cewa.
“Aliyu”.
Ahankali Moddibo yace.
“Na'am Abba ina kwana ya ƙarfin jikin naka?”.
Cikin sanyin murya Abba yace.
“Lafiya lau Alhamdulillah ya gida? Aliyu ya kwana biyu duk ban jika ba”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe kana yace.
“Wlh kuwa Abba ya ƙarfin jikin naka?”.
Ahankali Abba ya sauƙe numfashi kana yace.
“Jiki da sauƙi”.
gyara zamansa yayi tare da cewa.
“Toh Abba Allah ya ƙara sauƙi amma lafiya kuwa?”.
“Eh lfy lau. Yanzuma nayi waya da.
Mgnar Company na dake Marocco, to dama akwai kayan da mukayi Order sabbbin Injuna, sabida tsoffin sun fara samun matsala kasancewar sun kwana biyu to an kawo sabbin kuma Manager baya nan yaje duba lafiyarsa, kuma yanzu dole ana buƙatar sai akwai sahalewar wani da kuma sa hannu na kafin afara sauƙe kayan dole kuma akwai buƙatar tsayeyye da zai sa ido kan aikin kafa musarrafan da za'ayi”.
Tunda Abba ya fara magana Moddibo ya lumshe idanunsa yana cigaba da sauraron sa.
Abba ya cigaba da cewa.
“To yanemi da Inje, to ni kuma bazan iya ba, kullum ina fama da ciwon kai kuma kaga ga yanayin da nake ciki har yanzu ana zuwa min gaisuwa, shiyasa nake so ka shirya ka wakilceni, kaje ka fuskanci aikin idan yaso idan komai ya dai-dai-ta aka fara aiki in anyi rukunin forko saika dawo ba zaka daɗe ba”.
Moddibo kuwa shiru yayi tare da jingina bayansa da jikin Cushing.
Daga ɗaya ɓangaren Abba yace.
“Hello! Aliyu Hello!!, Hello!!! Aliyu kana jina kuwa?”.
Shi kuwa Moddibo cije Lip ɗinsa na ƙasa yayi Aransa yace bana son garin Gembila baki ɗaya jihar Taraba ta fitar masa ji yake tamkar wuta ake watsa masa aduk lokacin daya tuna shi kaɗaine ke rayuwa babu J ɗinsa, babu wani akusa dashi idan zai tafi masallaci shi kaɗai sannan idan zai dawo shi kaɗai kana idan zaici abinci shi kaɗai baki ɗaya ilahirin garin ya masa duhu kana ya masa ƙunci sam baya son zama acikinsa Nigeria kanta ta fice masa arai.
To amma kuma idan ya tafi Ummi ya zatayi.
Cikin sauri ya buɗe Idanunsa dake lumshe jin Abba na cewa.
“Aliyu ya dai kayi shiru baka ce komai ba?”.
Numfashi mai tsayi yaja kafin ya sauƙe ahankali cikin sanyin murya yace.
“Abba Ummi idan na tafi nayi nesa da Ummi ba zata ji daɗi ba sannan Innayina, da waye zan barta?”.
Ahankali Abba ya sauƙe Ajiyar zuciya tare da sauƙe dogon numfashi kana yace.
“Ba komai Aliyu Insha Allah za ayi ƙoƙari akula da duk kan al'amurran su sannan ba daɗewa zaka yiba”.
Cikin raunin murya Moddibo yace.
“Abba Ummi tace idan banje wajenta ba hankalinta na tashi damuwarta na tsananta. Abba bana son ganin Ummi cikin wani yanayi, Innayi na kuma bata da kowa a duniya saini in nayi nesa da ita ya zataji”.
Ajiyar zuciya Abba ya kuma sauƙe kana yace.
“Bakomai Insha Allah za muyi magana da Malam Ahmad za'a kwantar mata da hankalin ta, sannan dama inaso zamuyi magana dakai Innayi kuma kada ka damu zata iya dawowa gidana kafin ka dawo ko gidan Ummin”.
Ahankali Moddibo ya gyara zaman wayar akunnensa.
Yayinda Abba kuma ya cigaba da cewa.
“Akan kuɗin da aka har haɗa aka turo wanda Fatima ta saida Sarƙoƙinta da kuma motarta kazo zamuyi maganar ka karɓi kuɗin Asiya mata wata motar sannan sauran ta ajiye idan zata sai wasu kadarorin ma ta ajiye”.
A hankali ya gyara zamansa tare da rintse idanunsa kana ya cigaba da cewa.
“Sannan kaima naga motar da kake Amfani da ita tsohuwar mota ce ya kamata ka siya wata sabuwar motar ka riƙa hawa”.
Girgiza kai Moddibo yayi cikin raunin murya yace.
“Abba me zanyi da wata sabuwar mota Abba bana son Kuɗin dan Allah kadaina maganar Abba ni dai bana son Kuɗin Abba bana son su”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da girgiza kai kana yace.
“A'a Aliyu ya za ayi kace haka?”.
Moddibo kuwa rumtse idanunsa yayi tare da taune Lip ɗinsa na ƙasa kana yace.
“Toh Abba me zanyi da kuɗin da suka kasa ceton min J me zanyi da kuɗin da suka kasa temakon ceto mun rayuwar J Abba bana son Kuɗin Abba dan