Author : Aisha Aliyu Garkuwa Category : Free Novels Online (Read & Download)
juya tare da tattara duk kan nutsuwarta zuwa gareta tace.
“Na'am”.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace.
“Khausar wai Maganar da naji gaskiya ne abu ya kankama wai har an ɗaura aurenku?”.
Numfashi Khausar ta fesar kana ta sunkuyar da kanta ƙasa cikin rauni ta riƙo hannun Asma'u ta mannasu da kumatunta ga mamakin Asma'u sai taga hawaye na zuba Shar-shar-shar akuncinta.
Cikin sanyi da rauni Asma'u tace.
“Haba Khausar daga na miki magana sai ki fara kuka ai mu abun farin cikine”.
Ƙasa cewa komai Khausar tayi sai hawaye da take ahankali ta fara sheshsheƙa dake fita daga ainihin zuciyarta.
Araunane Asma'u tace.
“Haba Khausar kina kuka Ni kuma ya kikeso inyi kawai daga nazo muyi magana ta tsakanin mu sai ki fara kuka ai wannan abin farin cikine ba abin kuka ba”.
Kai Khausar ta girgiza cikin rawan murya tare da ƙoƙarin hana kanta kuka tace.
“Asma'u na amince ne saboda wasiyyar da Yah Jameel ya barmin kenan, amma ke kinsani kinsan waye Moddibo kinsan yanda tsakanina dashi yake kuma ni wlh banyi zaton da sauri-sauri haka zasu liƙa mishi niba”.
Hawaye na bin kuncinta ta cigaba da cewa.
“Bansan wace irin rayuwa zanyi atare dashi ba bansan wani iri zama zanyi ba bansan wani irin ƙakubalen zan fuskanta ba amma ina cikin taraddadi da tashin hankali Asmau”.
Atake idanun Asma'u suka cika da hawaye cike da tausayin Khausar.
Araunane Khausar ta cigaba da cewa.
“Ranar ma abinda ya kaini gidanku kenan naje ne muyi maganar amma sai in rasa ta yanda zan fara maganar ta ina zan kama mgnar ma”.
Cikin matsanancin kuka da tashin hankali tace.
“Asma'u shin menene makomata Yah Jameel ya barni da nauyi mai tarin yawa inaso in wanzar masa da wasiyyar sa gashi ya kasantu to amman ni menene makomata”.
Cikin rauni da tarin damuwa Asmau tace.
“Khausar ki daina kuka in dai kin gamsu Saboda farin cikin Yah Jameel amakwancinsa kikayi to ki daina kuka na tabbatar da Yah Jameel yana raye ba zaiso kukan kiba”.
Kasa da kai Khausar tayi hawaye na cigaba da zuba daga idanunta cikin zubda hawaye Asma'u ta cigaba da cewa.
“In dai har kinyi haka saboda farin ciki da kuma Wasiyyar Yah Jameel ya bar miki toh kada kiyi Kuka Yah Moddibo ai Namiji, ke kuma macece, kuma zuciya tana son mai kyau tata mata ke kuma mace cefa cikekkiya mai ababen muradin dukkan namiji”.
Ta sauƙe Ajiyar zuciya still Hawaye na bin fuskarta ta cigaba da cewa.
“Ina da tabbaci Khausar ko Yah Moddibo muddin yaji wasiyya ce Yah Jameel ya bar miki sannan saboda wasiyyar sa kika ce kinji kin gani zaki auresa nasan bazai zalunceki ba muddin bai kyautata miki ba to bazai zalunceki ba”.
Kai Khausar ta girgiza ta tare da ƙara danne sheshsheƙan Kukan ta haka ma Asma'u cikin sauri Khausar ta fara share mata hawayen fuskarta murya na rawa Asma'u tace.
“Khausar ban san da wani irin baki zan miki godiya ba, Ubangiji Allah ya biya ki da mafi kyawun sakamako saboda wasiyyar ɗan uwana kika amince da mgnar duk da ba yayanki bane”.
Cikin sauri Khausar ta sa hannu ta rufe mata baki muryan ta na rawa tace.
“Asma'u meyesa zaki ce haka Yah Jameel kike cewa ba Yayana bane?”.
Kai Asma'u ta girgiza kana cikin raunin murya tace.
“Ba haka nake nufi ba Khausar”.
Araunane Khausar tace.
“Toh meyesa haka Yah Jameel Yayana ne kuma Malami nane sannan Al'farma ya nema ya haɗani da Allah da Manzon ranan rabuwa ta na ƙarshe da Yah Jameel”.
Sai kuma tayi saurin rufe fuskarta da tafin hannunta kana cikin rauni ta cigaba da cewa.
“Yah Jameel Yana Kuka fa Asma'u yake cemin Khausar nasa zaiyi wuya inyi tsawon rayuwa alokacin daya faɗa min hankalina ya tashi na gigice bansan lokacin da hawaye ya fara zubo minba”.
Asma'u kuwa lumshe idonta tayi tana mai jin ƙaunar Khausar aranta.
Cikin sheshsheƙa Khausar ta cigaba da cewa.
“Ganin ina kuka sai ya fara yimin dariya yana cewa dan yace min zai mutu shine xan fara kuka ai bawai dan ya faɗa yana nufin mutuwa zaiyi ba, sannan yace min akwai Alfarma da temakon da yake nema awajena”.
Ta lumshe Idanunta hawaye masu zafi suka zubo kana ta cigaba da cewa.
“Yasa na mishi al'ƙawari koda bayan ransa zan cika masa wasiyyar Asma'u kuma nayi nasa al'ƙawarin idan har ban auri Moddibo ba kenan ban cikawa Yah Jameel Wasiyyar sa banyi masa taimakonba shiyasa nace Moddibo zan aura amma ke kin sani tsoron Moddibo nake hasalima babu wacce Moddibo ya tsana arayuwar sa sama dani kinsan shi baya sona ni kuma ina tsoronsa”.
Cikin sanyi da son ƙarfafa mata gwiwa Asma'u tace.
“Insha Allah ba zaki taɓe ba Ummi ma tayi farin ciki da wannan auren kowa kin sashi afarin ciki Insha Allah Ubangiji zai dawwamar miki da farin ciki agidan Auren ki”.
Ajiyar zuciya mai nauyi Khausar ta sauƙe kana yace.
“Ni dai zanyi wannan al'amarin saboda Yah Jameel ne kuma na yarda zan jure duk kan ƙunci, Haranta, Cin fuska, Tozarci, Cin zali da duk wani salon wulaƙanci da Moddibo zai min saboda cika burin Yah Jameel”.
Asma'u kuwa kai ta girgiza kana tace.
“Insha Allah ma ba zai miki ba da yardan Allah ba zaki ƙuntata ba rayuwa ba zata miki ƙunciba tunda Mommy ta sanya Albarka aciki komai zai tafi dai-dai”.
Ta ida maganar tare dasa hannu tana share mata hawaye murmushi tayi ko kaɗan bata son ganin hawayen Khausar cikin son ƙawar mata da damuwarta tace.
“Keda kike amarya wayasan amarya da kuka kuma amaryar ma ango mai tsada matar Yah Moddibo?”.
Harara Khausar ta watsa mata da jiƙaƙƙun Idanunta da Eyelashes ɗinta suka sake zara-zara dasu sai kuma ta tura baki tace.
“Ba wata amarya amarya ko kuma wahalalliya dai!?”.
Dariya Asma'u tayi kana tace.
“Ba wata wahalalliya amarya dai”.
Cikin sanyi Khausar tace.
“Hmmm Asma'u Ni dai hankalina atashe yake ina tsoron Moddibo bansan wani irin zama zamuyi ba”.
A dai-dai lokacin kuwa Samira Sani ce, da Amina ke waya tana gaya mata batun auren MODIBBO DA Khausar, Ya Salam wannan labarin ya girgiza Samira, haka yasa bta cilla wayar bisa gado ma tare da ta katse kiranba.
Da gudu ta nufi ɗakin Hajia Lami, tana shiga ta ganta zaune bakin gado da waya a kunne tane cewa.
“Haba dai Hajia Bunayyah wanne irin aure kuma, innalillahi ya za'a mana haka muna nan muna shiri mun rasa nitsuwa dan jawo hankalin wannan yaro kuma azo ace wannan shegiyar yarinyar ya aura, ya zasu fito mana a bazata”.
Sai kuma ta katse wayar tare da ruggume Samira da ta faɗa jikinta tana kuka wui-wui tare da cewa.
“Mommy shike nan ni kam nayi batam ɓaka tamtam, ni ba budurcinaba, ni ba Modibbo ba, ni ba lafiyata ba ni da zunubin zina da boka, ga ruwa mai wari da ke bibiyata”.
Ta ƙare mgnar da fashewa da matsanancin kukan da yasa Hajia Lami ruggume mata cike da takaici ta fara lallashinta.
Acan Falon Lamiɗo kuwa kallon Mommy dake zaune gefensa yayi ahankali ya sauke ajiyar zuciya kana yace.
“Ɗazun Alh Bukar suka zo maganar Amina da Naseeru to kuma har angama magana anbawa Naseer Amina since Ashirye suke nan da kwana goma suke so dan Ashirye suke”.
Murmushi Mommy tayi kana tace.
“A'a Masha Allah Abu yayi kyau Allah yasanya al'khairi”.
Anutse Lamiɗo ya gyara zamansa kana yace.
“Toh kuma tunda sakaranar yazo abakin gaba kawai za ahaɗa da ɗaurin bikin Khausar”.
Saurin Kallonsa Mommy tayi Asanyaye tace.
“Mai martaba da sauri haka?”.
Kallon yanda tayi da fuska yayi kana yace.
“Toh ke Meye damuwarki aciki?”.
Cike da damuwa tace.
“Toh Babu abinda muka shirya wa bikin nan fa”.
Numfashi ya fesar kana yace.
“Toh na saki ne ko kuma nace kishirya ne?,Ko cokali bansa ki siyawa Khausar ba kibar min ƴata Ni zan mata komai”.
Ya ƙarasa maganar cike da kara, mutuntaka, da kuma dattako.
Cike da kunya da jin daɗin karansa Mommy tayi murmushi kana tace.
“Nagode Allah yasanya musu al'khairi duk abinda kace haka za ayi”.
Murmushi yayi kana yace.
“Haka nake son ji ke dai ki sanya Albarka acikin wannan al'amarin”.
Jinjina kai tayi cikin sanyin murya tace.
“Allah yasanya alkhairi”.
*Morocco*
Cikin fushi Dr Jameel ya watsa wa Moddibo Harara kana yace.
“Haka kawai zaka zo kana takura min rayuwa dan bansa ankore kaba?”.
Cikin wani irin yanayi Moddibo yace.
“Korana?,Kasa akoreni J ni kake cewa zaka kora?J Bismillah in baka koreni ba baka amsa sunan ka Jameel ba”.
Afusace Dr Jameel yaja hannun farkarsa yace.
“Mu tafi Baby”.
Cikin sauri Moddibo yabi bayansa kafin ya fita tuni Dr Jameel yashiga mota, Cikin sauri yashiga motarsa zaiyi reverse yaga wasu motoci biyu sun taresa dole sai anja daya daga ciki kafin ya samu ya fita Dr Jameel kuwa tuni yaja motarsa ya tafi.
Da sauri Moddibo ya fito daga motarsa yace.
“Waye wannan yazo ya tare min mota ta ina zan fita”.
Dai-dai lokacin mamallakin Motar yazo cikin sanyin murya yace.
“Ayyah Bawan Allah kayi haƙuri na ajiye mota abayan naka banyi tsammanin zan daɗe ba abu kawai zan karba”.
Uffan dai Moddibo bai ce da mutumin ba yashiga motarsa yaja ya tafi sannan Moddibo ya shiga nasa yaja ya fita sai dai ba motar Dr Jameel ba labarinsa gefe da gefen Asibitin ya zagaya amma koda wasa baiga alamunsa ba.
Komawa yayi da niyyar shiga asibitin security suka hanasa duk yanda yaso shiga sunƙi barinsa cikin takaici ya juya akalar motarsa kai tsaye Mouley Youssef Hotel Rabat ya nufa cike da tunani iri-iri, yana isa yayi Parking kana ya fito yashiga cikin harabar Hotel ɗin ya shiga reception kai tsaye ya wuce masauƙinsa yana ya sa key ya buɗe ya shiga bakinsa ɗauke da sallama
Zama yayi akan 1sitter ya dafe kansa da hannu bibbiyu cikin sauri ya janye hannu ya ɗauki wayarsa ya kira Number Abba amma har ya katse ba adauƙa ba.
Lokacin da kiran yashiga wayar Abba tuni yayi bacci miss call uku Moddibo yayi ganin bai ɗauka ba yasa ya haƙura ya jinginar da kansa da jikin kushin yasani koda ace J zaiyi ko wani irin basaja ne aduniya ba zaiyu ace anyi masa Aure Iyayensa basu sani ba kuma ga duk kan alamu ma wancan karuwa ce domin tafi kama da karuwai wannan ne ya fara ɗarsa mishi shakku anya wannan J ɗin shi ne kuwa a fili yace.
“Ina inada tabbacin J na ba mazinaci bane, kuma bazai aikata zinaba, shin toh in ba J na bane waye wannan”.
Kanshi ya daddafe da duka hannunsa yana mai rumtse idanunsa da ƙarfi da kuma ƙarfin yace.
“No J bazai kasance haka, ina ba J ɗina bane kuma J na ko allura bai iya yiba ba abinda ma ya haɗashi da likitanci”.
Yayi mgnar da cikekkiyar yaƙini da yarda da hakan sabida yanzu ya fara samun nitsuwa, ya gamsu kawai tsananin kamannine mutumin yake dashi da Jameel ɗinsa wanda hatta sautin muryarsu iri ɗaya ne da J dinsa.
“Yah Salam. Allah mai iko to waye wannan ɗin".
Yayiwa kansa tambayar da yake masifar son sanin amsarta”.
*Gembila*
Ɓangaren Asma'u da Khausar ma haka suka raba dare wajen hira har misalin ƙarfe uku suna zaune suna hiransu ta Aminai daga baya suka koma hiran makaranta wani abin idan sun tuna suyi dariya wani suyi murmushi musamman rigimar kwausar da Modibbo, rayuwa kenan shikenan rayuwar makaranta ta wuce kamar ba ayiba cikin murmushi Khausar ta gyara zamanta tare da kallon Asma'u kana ta ɗan tsuke fuska sai kuma tayi kasa da kai cikin juya murya zuwa irin ta Modibbo tace.
“Ke uwar rawar kai”. Sai kuma taja tsaki tare da cewa.
“Ko sunanafa baya kira wai ke”
Dariya sosai Asma'u keyi tare da riƙe ciki, ita kuma Khausar baki ta ɗan taɓa kana a hankali tace.
“Da jajayen lips inshi a wurin kamar balarabe da dunduniyarsa laushi kamar ta jariyai, gashin ƙeya kamar jikin Mage.”
Cikin nunata da yatsa Asma'u tace.
“Yah Salam ashe har haka akeson Ƴaƴana ban saniba”.
Harara ta watsawa Asma'u tare da cewa.
“Kamar yaya so”.
Tafa hannu Asma'u tayi tana faɗin.
“Toh fisabilillahi in ba soba mai ya kai hankalin da idanunki kan lips inshi harda ƙeyarshi duk yawan sa hulanshi, shin tukun nama ya akayi kika san dunduniyarsa da taushi, na shiga uku ashe Allah ya tsare bawan Allah da kin fyaɗeshi”.
Cikin kauda kai dan sai yanzuma taji kunyar kalamaanta a hankali tace.
“Ba wani nan kin dai san kawai ni ina son mai kyau, haka Allah yayini”.
Ta ƙare mgnar tana lumshe idanunta, a hankali ta buɗesu ganin yadda lips enshi ke motsawa in yana mata masifa.
Haka dai sukayi ta hira mafi akasari kan Modibbo ne yanayi tana kusheshi kushen da yake naɗe da cikekken yabon halittarsa da ɗabi'unsa.
Washegari da safe Misalin shaɗaya bayan sun gama yiwa Mommy Komai suka shirya suka tafi gidan Ummi suna isa suka samu komai fes-fes ta gyara har ta gama girki.
Ummi kuwa murmushi tayi ganin su yasa tace.
“Yawwa ƴan al'barka tun ɗazu nake son zamu tafi gidan Abban Jameel nida Innayi, kuma gidan shiru Bashir ya tafi sabgogin gabansa”.
Khausar na zama tace.
“Ai haka suke Ummi haka ma Haiydar shegen yawo ne da yaran nan”.
Kai Asma'u ta jinjina tace.
“Haka suke kuma idan mutum ya fita na minti biyar su riƙa cewa shine yake yawo.
Murmushi Ummi tayi kana tace.
“Yau ɗauki wannan Asma'u ki ƙaiwa Innayi yanzu na leƙa na samu tana walaha”.
Zare ido Khausar za tayi cikin sauri tace.
“Innayin tana nanne?”.
Da sauri Asma'u tace.
“Ai tunda Yah Modibbo ya tafi Marocco ta dawo nan”.
Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe ta koma ta zauna tare da faɗin.
“Au”.
Ahankali Asma'u ta jawo kular dake gaban Ummi tana buɗewa tace.
“Yau kuma mai akayiwa Innayi?”.
Kallon kulan Ummi tayi kana tace.
“Tuwo nayi mata nasan tanason tuwo”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana tace.
“Ayyah aikam dai”.
Ta ƙare mgnar tare da nufar ɗakinta da kular don nan innayi take.
Anutse Ummi ta maida kallonta kan Khausar cike da kulawa tace.
“Khausar”.
Cikin sanyi ta ɗago kanta tace.
“Na'am Ummi”.
Ido Ummi ta tsira mata kana tace.
“Ahaka za ayi zaman auren?”.
Khausar kuwa da sauri tayi ƙasa da kanta batare da tace Uffan ba yayin da hawaye ke cika mata kwarmin ido.
Ahankali Ummi ta sake kiran sunan da faɗin.
“Khausar”.
Shiru Khausar tayi sake kiran sunanta ta kuma yi.
Still Bata dagoba numfashin Ummi ta fesar tare da cewa.
“Khausar ɗago mana ki kalleni”.
Ahankali ta ɗago Idanunta dake cike da ruwan hawaye cikin sauri Ummi ta girgiza mata kai kana tace.
“Kar kiyi kuka Khausar insha Allah inaji Ajikina akwai al'khairi a alaƙarki da Moddibo Ubangiji Allah ya miki albarka”.
Cikin rauni da zubda hawaye ta amsa da Ameen asaman laɓɓanta.
Cikin rarrashi da son kwantar mata da hankali Ummi ta cigaba da cewa.
“Sai kuma batun tsoro ki daina mutumin da kike ƙoƙarin kasancewa ƙarƙashin inuwar Aurensa ai bai canci irin wannan tsoronba, shi ba Dodo bane Aliyu da kike ganifa yana da mutunci, Kara, tausayawa, da kuma karamci tsoron da kike nunawa akansa ya tsananta”.
Cikin sanyi ta girgiza kanta muryan ta na rawa tace.
“Ummi baki sanshi bane ba fa”.
Itama Ummi cikin sanyi tace.
“Nasan shi mana Khausar”.
Araunane Khausar ta girgiza kai cikin son Hana kanta kuka tace.
“Ummi baki san saba yana da mugunta fa”.
Kai Ummi ta girgiza kana tace.
“Ba zai miki mugunta ba Khausar in Allah yaso ya yarda Babana bazai miki mugunta ba saboda kin masa duk kan halarcin duniya”.
Lumshe Idanunta tayi cikin raunin murya tace.
“Ummi baya sona ya tsaneni koda kallon fuskatane baya so tunda muke tare Amakaranta da zaran mun haɗu zai nemi laifin da zai lika min kawai dan ya dake ni”.
Ta share hawayen da suka zubo mata cikin sanyi ta cigaba da cewa.
“Ummi ina tsoron rayuwa dashi sannan kuma Ummi ina so in cikawa Yah Jameel burinsa Ina so ciki wannan al'ƙawarin dana ɗauka”.
Ahankali Ummi ta matsa kusa da ita ta janyota jikinta ta Rungume cikin ƙarfafa mata gwiwa tace.
“Kar kiyi kuka Khausar! Kada jiki tsoro! Kada ki damu ki daina tsoron Babana babu abinda zai Miki”.
Ta ƙare mgnar dasa hannunta, amshi wayar Khausar tare da cewa.
“Yanzu bani wayarki in sa miki number's, ko kinada ita?”.
Cikin sauri ta jujjuya kanta.
Ita kuwa Ummi cikin kulawa yace.
“Toh bani wayar, in sa miki, yanzu dai kin san ke matar aurece, igiyoyin aurensa na kanki, banda yawan yawo, dukda dama nasan baku da yawan yawo".
Ta ƙare mgnar da fara sa mata number Modibbo dan wayarta ba pin, tana gama sa number's ɗin ta miƙa mata waya.
Amsa tayi tare da kife wayar bisa cinyarta. Ita kuwa Ummi da sauri ta kalleta jin tana cewa...
Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276. Kana in tura miki shi kisha karatunki cikin aminci.
By
*GARKUWAR MARUBUTA*SAKAYYA
41
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*
_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_
_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman