Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Sakayya Complete Hausa Novel by Aisha Aliyu Garkuwa

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Free Novels Online (Read & Download)

Chapter   90 / 140

267K to 270K   out of 417.8K words

Moddibo ya ratsa kunnensu.
Kai Sheikh Jabeer ya jinjina kana yace.
“Toh menene cikekken sunanka ai Moddibo ba sunan yanka bane?”.
Lumshe idanu Moddibo yayi tare da buɗe su kana ya shafa sajensa a hankali yace.
“Sunana Aliyu Youseep Muhammad Mouleey”.
Cikin matsanancin mamaki daya sake mamaye zuciyoyinsu da tabbatar musu lallai babu haufi jininsu ne, akaro na barkatai suka juya suka shiga kallon junansu da ƙyar Sheikh Jabeer ya furta.
“Kace me sunan ka?”.
Ahankali Moddibo ya kuma motsa laɓɓansa tare da faɗin.
“Sunana Aliyu Youseep Muhammad Mouleey”.
Cike da matsanancin mamaki daya daki zuciyoyinsu suka haɗa baki wajen faɗin.
“Ikon Allah sunan ka kenan?”.
Kai ya gyaɗa yana ɗan ciza lips ɗin sa na ƙasa ya furta.
“Eh sunana kenan?”.
Ahankali Sheikh Jabeer ya furta.
“Ikon Allah toh waye mahaifinka”.
Araunane ya jingina bayansa da jikin Kujeran kana ya girgiza kai tare da lumshe idanunsa yace.
“Babana ya rasu!”.
Da sauri Lalla Khadijah tace.
“Wlh mahaifinka na raye gashi nan a gabansa kusa da kai”.

Cikin Sauri Didi ta katse Khadijah ta hanyar daga mata hannun, kana ta juyo ta kalli Modibbo zuciyarta na cigaba da bugawa da karfi tamkar zai fasa ƙirjinta ya fito ta tace.
“Toh wacece Mahaifiyarka!?”.
Idanunsa cike da rauni ya buɗe ya kalleta kana yace.
“Mahaifiyata ma ta rasu”.
Cikin sauri Rahama tace.
“Ga Didi nan a gabanka a raye waya ce maka baka da mama”.
haka nan yakejin baya son kukan Rahma har ransa, ya kuma lura ta ƙoshi da sakalci cikin sanyi yake jujjuya mata kai alamun kada tayi kuka.
Sarki Youseep Mouleey kuwa cikin sauri yayi gyaran murya tare da faɗin.
“Toh waya faɗa maka Iyayen ka sun rasu?”.
Moddibo kuwa cikin sanyi da fesar da numfashi ya kallesa kana ya gyara zamansa tare da faɗin.
“Kakata ce ta faɗa min”.
Aƙage Sarki Youseep Mouleey ya kuma cewa.
“Shin wacece kakar ta ka?”.
Ahankali ya ɗaga yatsarsa tare da nuna musu hoton dake manne jikin bango kana yace.
“Gata can Kakata na rasa ya akayi nazo na samu hotonta acikin wannan Fadar taku”.
Cikin jin dadi Jabeer bin Jabeer yace.
“Aha bana faɗa mukuba, ai wlh dama na sani wannan daga gani babu tambaya Aliyu ne”.

Da sauri Didi dake kuka ta matso kusa dashi tare rungumesa.
Shi kuwa Moddibo shiru yayi, sai idanunsa daya lumshe yayin da lokaci ɗaya wani irin yalwataccen farin ciki ya lulluɓesa alokacin data rungumesa tsintar kansa yayi da ɗaura tafukansa abayanta ya rungumeta lokaci ɗaya kuwa yaji ruwan hawaye na cika masa idanunsa wanda bai san dalilin zuwan suba kawai dai yasan yanajin wannan matar da yaranta har cikin ƙahon zuciyarsa hakanan yakeji ya aminta da ita fiye da aminci da yayiwa ko wacce uwa a duniya.
Haka zalika rungumar da tayi masa ji yayi kamar Innayi ce ta ruggumeshi amman sai yakejin aminci da son fiye yadda yake ji tare da innayi wannan ruggumar jinsa yayi ruggumace ta mahaifiyar data ɗauki cikinsa tsawon wata tara da kwana tara ce ta kuma yi naƙudarsa so a matsayin uwa zuciyarsa da jininsa suka amshi rungumesa da tayi kamar yadda jikinsa zuciyarsa suka amshi Khadijah da Hafsat da Rahman a matsayin tsotsonshi muharamansa, sabida jini baya ɓuya.
Ji yake tamkar rungumar da yake nemane tsawon shekara da shekaru ne wanda bai samu ba.

Didi kuwa kuka ta saki hadda shesh-sheƙa batare data raba jikinsu ba tace.
“Abeey wallahi wannan ɗana ne. Abba wallahi ɗana ne ku gani taya za'a yi kuce sai kunyi wani bincike? ɗana ne Aliyuna ne fa Abba ɗana ne fa”.
Kalmar da take maimaitawa kenan tana cigaba da kuka.

Da sauri Sheikh Jabeer ya riƙo hannunta kana yace.
“Fatima kada kiyi kuka na gamsu na kuma yadda ɗan kine kuma tsatsonki ne nima ina ji ajikina tabbas tsatsonki ne kuma jikana”.
Ya ida maganar yana share mata hawayen daya ƙi tsayawa a idanunta.

Sarki Youseef Mouleey kuwa cikin sauri ya buɗe wa Moddibo hannunsa kana cikin raunin murya da tsantsar bege yake faɗin.
“Zo ɗana”.
Moddibo kuwa tsintar kansa yayi da gaza yi musu gardama, kana zuciyarsa ta gamsu da kalaman da suke faɗa.
Yayin da yake jin su ɗin wani sashe ne na jikinsa.
Da wani irin bege da shauƙi ya faɗa jikin Sarki Youseep Mouleey ya rungumesa yayin da shima sarki Youseep Mouleey ya ƙanƙamesa ji yake kamar idan ya sake sa tamkar zai sake nesa dashi ne ciki rauni yake faɗin.
“Shakka babu wannan Aliyu nane”.
Kallonsa ya mayar kan Sheikh Jabeer kana yace.
“Abeey wallahi wannan ɗana ne.
Allah sarki rayuwa. Allah ya ɗauki ran Mahaifina yau da yaga jikinsa da zarrar da bai taɓa tunani da zato ba”.
Baki ɗaya kallonsu mutanen falon keyi cike da tarin tausayinsu.
Sarki Youseep Mouleey kuwa cikin rauni da farin ciki ya sake rungume Moddibo tare da kallon mahaifiyarsa Niyna yana faɗin.
“Niyna yau da Abbana na raye da yaga Jikinsa da Zarrar da zata girgiza Maƙiya, Da yaga jikinsa da zarrar da zata sa zuciyoyin maƙiya cikin tashin hankali da firgita tabbas Aliyu ɗana ne Niyna kalleshi fa”.
Kai Niyna take jinjinawa cike da gamsuwa tana mai shafa kan Modibbo.

Moddibo kuwa mamaki da al'ajabi ne ya cika masa zuciya ahankali ya janye jikinsa daga na Mahaifin nasa kana ya koma ya zauna yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya.

Ahankali ya maida idanunsa kan hoton Innayi kana ya dawo da kallonsa garesu cikin nutsuwa ya furta.
“Wacece wannan awajen ku? Kakata ce wacce da ita nake rayuwa, Kuma ita kaɗai nake da ita a duniyata”.
Cikin sauri Didi ta girgiza masa kai tare da faɗin.
“Kana da kowa aduniya. Kana da ƙanne, kana da Yayu, Kana da Mahaifi, Kana da Kakanni kakan ka ɗaya ne ya rasu Mahaifin Babanka, Kana da zuri'a zuri'arka mai tarin yawa gaba ɗaya wannan masarautar family'nka ne.
Aleey a ina kuke rayuwa?”.
Tun da ta fara magana ya tsira mata idanu yana sauraren ta har sai da tadasa aya kafin yace.
“A Nigeria muke rayuwa acikin Jahar Taraba Gembila” .
Da mamaki ta kallesa tare da faɗin.
“Allah sarki Innayi tana raye?”.
Da sauri ya kalleta jin Sunan Innayin sa abakinta sai kuma ya jinjina kai kana yace.
“Eh Innayi tana raye”.
Still idanunta na zubda hawaye ta furta.
“Allah sarki Innayi tayi min halarci mai yawa ashe wasiƙar data ajiye min da gaske ne ta kular min da ɗana kula mafi kyawu da inganci”.
Zazzafan Ajiyar zuciya ya sauke kana yace.
“Kin santa ne?”.
Kai ta jinjina masa tare da cewa.
“Na santa Hadima tace da aka haɗani da ita.
Jakadiyata da aka haɗani da ita tun daga lokacin da aka kawo ni ƙasar Marocco, ashe data tashi ƙasata ta koma da ɗana kusa da Jahata dan ta kular min da ɗana”.
Sai kuma ta lumshe idanunta akan Moddibo kana ta cigaba da faɗin.
“Sannan sai da tayi sanadin yanda ɗana zai kasance mutumi na gari har Alkur'ani mai girma ka rubuta ka kaiwa Mahaifina ya duba maka”.
Sai kuma ta mai da kallonta kan Sheikh Jabeer kana tace.
“Abeey Ya akayi baka taɓa kallonsa ba?”.
Sanyayyar numfashi Sheik Jabeer ya fesar cike da kamala yace.
“Fatima wannan abubuwane da tattaunawarsu sai ahankali kiyi haƙuri yanzu dai mu fara godewa Allah”.
Kai ta jinjina tana mai yin tasbihi azuciyarta...

Jakadiya kuwa cike da tsantsar farin ciki tace.
“Ai wannan ma babu bukatar wani bin cike ko wani abu tsatso ne na gidan nan, jinine na gidan nan, haihuwa ne na gidan nan,Tarbiyya ce ta gidan nan,Masha Allah”.
Ta sauƙe Ajiyar zuciya tare da cigaba da cewa. _“Fatabarakallahu Akhsanul Khaliƙin_, Halittace ta gidan nan daga gani ma babu tambaya tsatsone namu, ina Ibraahim yazo yaga ɗan uwansa da yake cewa yana haɗuwa dashi acikin mafarkai”.
Haka nan suka ci-gaba da tattaunawa cike da al'ajabi da mamaki wanda mgna ce ta gsky da gsky wacce gskyarce tayi aikin da dole Modibbo yaji zuciyarsa ta gamsu da kalamansu koda suka fara yi mishi tambaya kan yadda ya sarrafa Rinƙas ya shaida musu yasan Rinƙas a mafarkine ga mamkinsu dukkan wasu al'adu ko wani abu na sittin masarautar duk ya sani.

Cike da kulawa Sheikh Jabeer ya kalli Moddibo kana yace.
“Moddibo ka shiga ka kwanta in Allah ya kaimu da safe zamu ƙarasa magana”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Wayoyina suna cikin mota ina so akawo min su ina buƙatar mgn da innayi inada tarin tambayoyin da nakeso inyi mata”.
Kallonsa Sarki Youseep Mouleey kana ya girgiza masa kai tare da faɗin.
“Kada ka damu duk abinda kake buƙata ga hadimanka za'a yi maka sannan duk tambayoyinka ka tarasu lokacin amsasu nan tafe”.
Kai ya gyaɗa yana mai cigaba da jin nutsuwa su kuwa sallama suka masa kana suka fice.

Nigeria Gembulan
Dai-dai lokacin kuma Naseer ne, zaune tsakiya falonshi wasu hawaye masu zafin gaskene wani ke korar wani, tunda yaje gidan Lamiɗo, hira wurin Amina da Lamiɗo da kanshi ya sanar masa an daura auren Khausar da Modibbo ya kasa ƙara sawa cikin gidanma ya juyo ya dawo, kuka yayi tayi tamkar mace har yanzu ɗaya gaza bari kife kansa yayi bisa guiwowinsa a fili yake faɗin.
“Khausar ya za'ayi jinin haka, duk wani burina da sha'awata a kanki ne, na soki tun baki san kanki ba, rana tsaka ba zato ba tsammani inji wai an aura miki Modibbo, shike nan na rasaki kenan, domin na sani yafi ƙarfin iyawata, bani da abinda zan iyayi a kanshi, yayi min zarrar rayuwa ya kwace min ke”.
Sai kuma ya ɗan tsagaita kukan tare da kallon wayarsa da kiran Amina ya shigo, cikin tarin takaici ya kashe wayar a fili yace.
“Khausar ne kaɗai a raina Amina zan dai aureki ne dan biyan buƙatar rayuwata, da kuma rage jarabar rashin malakar Khausar ne”.
Haka yaci gaba da surutai kamar zautacce, Allah ya sani baiyi zaton hakaba.

Rabat Marocco
Washe gari tun shida da rabi na safe ƴan uwanshi mata suka shigo a jere, Lalla Hafsat ce riƙe da wani tray mai ɗauke da wasu ƴan ƙaran kwanuka masu kayan gani, Ragama kuwa wayace makale a kafaɗarta. inda yake suka nufa, jawo stoll Hafsat tayi tare da ajiye trayn kana ta fara haɗa mishi tea.
Lalla Khadijah kuwa hannun ta miƙe mishintare da yimishi sallama alamun musabaha takeso suyi.
a hankali ya ɗago hannunsa na dama ya miƙa ta, dai-dai lokacin kuma Rahama ta manna mishi wayar dake hannunta a kunne, tare da cewa.
“Yah Aleey ga Yah Ibraahim daga jiya zuwa yau ya kirani yafi sau goma, wai in ban haɗuka ba yaji muryarka in ya dawo bazai min mgn ba”.
Ɗan murmushin gefen baki yayi tare da sa hannushi na hagu ya amshi wayar.
It kuwa Rahama cikin jin dadi ta kalli askin kan Modibbo tare da cewa.
“Lah Yah Aleey ko askinkafa irin na ahlin masarautar Mouley ne”. sai kuma ta ƙara sunkuyowa kanshi tare da cewa.
“Lah Adda Khadi zoki gani, wlh shima yanada naɗeɗɗen gashin irin na Abualeey”.
Numfashi me ɗan tsawo ya fesar ganin Hafsat na miƙa mishi cup ɗin tea da kuma turo masa stoll din gabanshi tare da cewa.
“Bisimillah Didi tace ka ɗan taɓa wannan kafin ta ƙarasamaka breakfast inka”.
Longwaɓar da kai yayi tare da ɗan yamutsa fuska kana a hankali yace.
“Toh me ɗaya zanyi mgn a waya ko cin abinci ko gaisuwar ku, ko kuma kallon kaina zan bari Rahama tayi tayi”.
Ya ƙare mgnar da amsa sallamar da yaji anyi mishi da muryar da ta kasance irin tasa sak.
Sai kuma ya ɗanyi murmushi jin Ibraahim na cewa.
“Yah Aleey ka koresu in ba hakaba bazasu Barka ka huta ba fa more especially Rahama Bata da aiki sai suru”.
Cikin sanyi yace.
“Kana ina yanzu Ibraahim kai ban gankaba”.
Cikin jin daɗi Ibraahim yace.
“Ina Istanbul, nima jiya na tafi da safe kai kuma ka isa da yamma”.
Kai ya gyaɗa tare da kallon Hafsat dake miƙa mishi tea ɗin amsa yayi da hannunsa na dama. Ya lura kusan halinta iri ɗaya ne da nashi bata da yawan surutu da fara'a sosai sai dai kuma tana da kula.
Lalla Khadijah kuwa miƙewa tayi tare da cewa.
“Bari inje in taya Didi aiki”.
Kai ya gyaɗa mata kana ta fita.
Daga nan yaci gaba da mgn da Ibraahim, tare da kallon Hafsat dake ƙara mishi siymil wani abinci su ne na larabawan can da fulawa akeyishin sai dai ya wadatu da nama.

Cup din ya miƙawa Rahama tare da kallon Hafsat kana yace.
“Alhamdullah na ƙoshi, kai ta jinjina kana ta tattara wurin tare da cewa.
“Toh kaje ka ɗan kwanta ka huta, ke kuma Rahana zomi tafi".
Kai jinjina mata, daga nan suka fita suka tafi.

Sai misalin ƙarfe 9:30 Didi ce da Sarki Youseep Mouleey suka shiga falon suna shiga suka ji falon shiru alamar baya nan yayin da suka fara jiyo wani sautin murya mai daɗi da sanya nutsuwa na karatun Alkur'ani na ratsa kunnensu.
Cikin nutsuwa Sarki Youseep Mouleey ya fara bin direction ɗin da yake jiyo sautin karatun Yayin da Didi ke biye dashi.
Akan darduma suka hango sa da alama Salatul duha ya idar kana idanunsa na lumshe yana karatun akansa.
Daga gefensa suka zauna lokaci ɗaya hawaye ya shiga bin kuncinta cike da farin ciki ta ɗaga hannunta sama kana tace.
“Alhamdulillah Innayi kinyi min duk kan gatan duniya kin bawa ɗana Ilimi mafi girman ilimi mafi tsada da daraja wanda zai amfanesa duniya da lahira sannan zai amfanemu”.
Sai ta kuma kalli Moddibo still hawaye na kwaranya daga idanunta ta cigaba da faɗin.
“Wannan ɗana ne yake karatun Alkur'ani tamkar acikin harami wanda koda acikin harami sai an jinjina masa”.
Moddibo kuwa jin sautin Muryanta da kuma motsin Mahaifinsa yasa ya buɗe Idanunsa jin tana cigaba da cewa.
“Innayi Allah ya biya ki da mafificin Al'khairi Ubangiji Allah ya sadamu inyi miki *SAKAYYAH* da mafi kyawun abinda ki kayi min sannan inyi miki godiyar da ban san da wani irin baki zan miki ba”.
Ahankali Moddibo ya shafa addu'a kasancewar yazo ƙarshen surar da yake karantawa.
Anutse ya juya ya kallesu haka nan zuciyarsa ta aminta da cewa Tabbas suɗin wasu ababene na jikinsa da Zaran ya kalli Mahaifinsa zai ga tsananin kamanninsa dashi babu abinda ya raba su shi kansa kamanninsa da mutumin yana bashi mamaki babu abinda ya rabasu sai dai shi Modibbo yawan shekarun sa bai kai nasa ba zuwa yanzu ya gama gamsuwa iyayensa ne su.
Cike da ladabi ya gaishe su kana suka amsa cikin sakin fuska da tarin ƙaunarsa.

Didi kuwa ahankali ta janyo basket data shigo dashi ta ajiye agabansa, tare da fitar da kulolin, kana ta ɗauki plate ta zuba masa abincin da ta dafa mishi da kanta, kana ta kalleshi cike da so da ƙauna tace.
“Wannan abinci da kaina na shiga kitchen na dafa maka dan kaci da kyau”.
Cikin gamsuwa da kalamanta ya jinjina kai ya tabbatar nutsuwa da kamalarta da kuma kimarta tafi ƙarfin tayi masa ƙarya maganganun da take faɗa daga zuciyarta ne kuma gaskiya ne babu shakka ko haufi aciki shi kanshi ya gamsu mahaifiyarsa ce ita Abualeey kuwa mahaifinsa ne masarautar Mouley kuwa tabbas mahaifarsace...
Fuska ɗauke da yalwataccen murmushi Sarki Youseep Mouleey ya janyo Cup tare da faɗin.
“Ni kuma da kaina zan haɗa maka tea in baka duk kan kulawar daka rasa atare damu na tsawon shekaru, in Sha Allah sai mun haɗa ta mun baka a iya tsawon sauran Rayuwar da Allah ya ƙadddara mana anan gaba”.
Cikin wani irin tattali da kulawa suka ci-gaba da faɗa masa maganganu masu sanyi da ratsa ƙwaƙwalwa wanda ko wani ɗa yake fatan saurara daga iyayensa.
Moddibo kuwa tamkar amafarki haka yake jin abubuwan sai dai wani lokaci wani abu ya taɓa ganinsa amafarki sa.
Haka suka cigaba da kulawa dashi suna hira da kara fahimtar yasan komai ma masarautarsu, yinin wannan rana suna tare dashi koda motsi yayi zasu tambayesa me yake so ko kuma me yake buƙata sai gab Azahar suka yi masa sallama suka fita suna tafiya aka kira sallar Azahar...
Anan yayi Sallar Azahar ɗin sa yinin wannan ranan ma ba'a buɗe sa.
Haka yayi kwanaki biyu anan batare daya fita koda ƙofan falon ba sai dai akawo masa abinci sai dai kuma su shigo suyi hira dashi...
Yau ta kasance Asabar inda ya zama kwanakinsa uku kenan a Masarautar Mouleey bayan fitar Mahaifiyarsa, Mahaifinsa da kuma Sheikh Jabeer yana zaune a falon kamar daga sama ya fara jiyo shesh-sheƙan kuka.
Cikin sauri ya juya ya kalli Hadiman dake tare dashi sai kuma ya kauda kansa ganin basu bane cikin yanayin mamaki da al'ajabi ya juya gabas da yamma kudu da Arewa yaga dai duk basu bane keyi kukan. Bisa alamu kuma kamar su basujiba, ahankali ya miƙe ya nufi Corridor har ya isa falon nan ma ba kowa sai dai yana jin shesh-sheƙan kukan daga cikin bedroom cikin sassarfa ya nufi bedroom ɗin yana shiga ya hangi Jalaluddeen ne zaune agefen gadon yana kuka tamkar ransa zai fita.
Cike da matsanancin mamaki gami da al'ajabi yace.
“Jalaluddeen k...”.....



LITTAFIN SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 in tura miki kisha karatunki.

GAREKU masu son Maganin infection duk maiso ta biya yau in Sha Allah jibi saƙonku zai taho.


By
*GARKUWAR MARUBUTA*SAKAYAH

43

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Tallah !! Tallah !!

Shahararriyar Marubuciyar nan Ikilima Adam (kyauta daga Allah) wacce ta nishadantar daku a littafin ta mai suna *Kanwata* , yau ta sake dawo muku Domin tallata muku Littafin mai Suna ( Rai Daya Jan Zaki) littafine mai kunshe da Butulci , cin amana ,zagon Kasa , soyayya irin ta gani kasheni , aminci da saura n su basai n'a cika Ku da surutu ba Hausawa sukace Gani yakori ji.

Farashin wannan littafin Naira Dari biyar ne 500 kacal postin biyu a arana banda ranar Juma'a .
Domin Karin bayani Ku tuntubeni a lambata kamar haka (09069080725 ko Kuma + 22953726162 ) wacce Bata shirya Siya ba kada mu batawa juna lokaci.
Domin aikawa da kudi kai tsaye . 3115484026 ikilima Adam first bank
Turo shaidar biya akan wannan 09069080725 sai najiku.

Jalaludeen kuwa cikin rauni ya ɗago idanunsa wanda suka zama tamkar garwashin wuta, saboda yanda sukayi ja-jawur yayin da baki ɗaya ilahirin jikinsa ke rawa kar-kar tamkar wanda aka jona masa Shorking kuka yake mai shiga jiki tare da ratsa zuciyar duk wani mai imani daya saurara.
Da sauri Moddibo ya ƙara sa kusa dashi gefenshi ya zauna cike da matsanancin rauni da kuma famewar mikin dake zuciyarsa na rashin J ɗinsa ya shiga rera wani irin raunataccen kuka tamkar ransa zai fita, kukan wanda

90 / 140

Chapters