Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Sakayya Complete Hausa Novel by Aisha Aliyu Garkuwa

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Free Novels Online (Read & Download)

Chapter   70 / 140

207K to 210K   out of 417.8K words

Jameel da kuma yanda aka samu gawarsa saiya zubda hawaye tare da la'antar wa anda suka aikata masa haka.

Asma'u dake gefen Ummi zaune Idanunta cike da hawaye tana ganin Khausar ta fashe da sabon kuka kana ta miƙa mata hannu cikin sauri Khausar ta kamo hannunta tare da zama gefenta ta.
Rungume juna sukay tare da fashewa da wani irin kuka mai tsuma zuciya.
Mommy da Hajiya Bunayya kuwa kusa da Ummi suka zauna.
Mommy na Kallon Ummi taji wasu sabbin hawaye sun zubo mata cike da tausayawa Mommy tace.
“Ummi Sannu”.
Sunkuyar da kai Ummi tayi cike da dauriya tace.
“Toh ya zamuyi Aysha ya zamuyi da hukuncin Ubangiji.
Jameelu ya riga mu gidan gaskiya ya tafi ya barni da gurbin da bansan ya zai cikeminba”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.
“Kiyi haƙuri Ummi”.
Kasa ƙara sawa tayi sabida kuka yaci ƙarfin ta kawai saita kife kanta gefen Ummi ta shiga rera kuka.
Ajiyar zuciyar Ummi ta sauƙe cikin sanyin murya me ɗauke da ƙuna tace.
“Kiyi haƙuri Aysha haka Ubangiji ya tsara bamu isa muja da lamarinsa ba addu'ar mu suke buƙata muyi musu addu'a Allah ya gafarta musu”.
Cikin sheshsheƙa Mommy tace.
“Ameen”.
Ahankali Mommy ta juya suka gaisa da Hajiya Turai da Hajiya Karima sannan da ƙannen Abban Jameel Hajiya Maryam da Hajiya Fa'iza suka yi musu ta'aziyya.

Khausar dake Rungume da Asma'u cikin Muryan kuka tace.
“Asma'u yanzu da gaske Yah Jameel ya rasu shikenan ya tafi ya barmu!”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa.
“Da gaske Khausar Yah Jameel ya rasu shikenan gatanmu ya rasu rufin asirin mu ya tafi garkuwan mu ya barmu Inuwarmu wajen fakewar mu ya gushe, bangon da muke jingina muji daɗi ya fadi ƙasa”.
Kasa ƙara sawa tayi kawai ta fashe da kuka me tsuma zuciya.
Cikin sauri Ummi ta girgiza mata kai Araunane tace.
“Kul Asma'u!,Kada ki faɗi haka kada kiyi butulci ga Ubangiji domin shi ya bamu Jameelu kuma shi ya ɗauke mana shi kuma zai jibanci laluranmu muddin mukayi tawakkali”.
Innayi dake gefe ta matso kusa da Asma'u da Khausar ta janyosu jikinta tare da ɗaura kansu akan cinyarta cikin Muryan rarrashi tace.
“Kuyi haƙuri kuyi masa addu'a”.
Ahankali Khausar ta ɗago tare da kallon Innayi kana tace.
“Innayi yanzu shikenan Yah Jameel ya tafi ya barmu har abada baza ku sake ganinsa ba!? Bazai sakeyi mana nasihaba, bazai sake neman al'farma a wajenaba ashe Yah Jameel Wasiyya yayi ta barmin a wancar ranar”.
Shafa kanta Innayi tayi kana tace.
“Khausar kada kiyi kuka muyi masa addu'a shine abinda yake buƙata awajenmu kana mu cika masa dukkan wasiyar daya bar mana”.
Kai Khausar ta gyaɗa kana ta cigaba da kuka mai ciwo har Idanunta suka kumbura.
Sai Bayan sun idar da Sallar Maghariba kafin Lamiɗo ya ɗebe su suka tafi
A wannan daren ranar baki ɗaya haka suka kwana cikin ƙunci zuciya da alhini Moddibo kuwa baya um bare Um-um ko awajen zaman makoki idan akace masa sannu baya magana saidai kallo sai ance Allah ya jikansa kafin yace.
“Ameen ya Allah Nagode”. Iya abinda yake iya faɗi kenan.

Haka rayuwa tayi musu ƙunci da ɗaci haka aka ɗauki tsawon kwanaki bakwai ana zaman makoki har awannan kwanaki kullum cikin gida da waje a cike yake da masu zuwa ta'aziyya.
Washe garin rana ta takwas da safe Moddibo na fita bai nufi ko ina ba sai gidan Ummi bakinsa ɗauke da Sallama yashiga falon zaune ya sameta hannunta riƙe da carbi ta zubawa waje ɗaya ido.
Jin Sallamar sane yasa ta ɗago kanta tare da tsira masa Ido agefenta ya zauna.
Cikin sanyi tace.
“Babana”.
Ahankali yace.
“Na'am Ummi”.
Cike da tausayawa Ummi tace.
“Babana kalli yanda ka sake dawowa fa yaushe zaka sawa ranka dangana ne? Kadafa muyi abinda Allah bayaso”.
Batare da yace Uffan ba yayi ƙasa da kansa yana jin wani irin zafi azuciyarsa.
Jin muryarsa yasa Asma'u dake Bedroom ta fito tare da zama agefensa kana ta gaishesa.

Ahankali Moddibo ya juya ya kalli Ummi kana yace.
“Ummi yanzu a Duniya babu abinda nake buri daya wuce ingano su waye suka sace J sannan suka yi masa kisan gillah ina so insani. Ummi inaso inyi bincike akai ina so inga lallai a hukunta su kwatankwacin zalinci da suka mana”.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe tare da cewa.
“Aikuwa Yah Moddibo Khausar tana da dan abinda ta sani.
Domin ranan da muka rabu da Yah Jameel na karshe aranan ne ya maida Khausar gida kuma tace mana.
Taga wata mota na binsu.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tace.
“Amma Babana Meye amfanin bincike bayan sun kashesa!?”.
Cikin sauri yace.
“To ai Ummi nan nema yake da amfani tunda suka kashesa dama mun biye musu ne saboda munji tsoron kada su kashesa shiyasa mukabi tsarinsu!”.
Girgiza kai Ummi tayi kana tace.
“Toh amma dai ni inaganin barin shi yafi A'ala kada kai ɗinma da ka rage mana su cutar mana da kai”.
Sam Ummi ta rigada ta saki komai na duniya shiyasa duk yadda yaso ayi mgnar a sake buɗe file din binciken taki.
Fahimtarsa bazata yardabane yasa ya nuna mata ya hakura.
Kallon Asma'u yayi tare da miƙewa kana yace.
“Asma'u zamuyi magana”.
Kai ta gyaɗa sannan ya fice.

Yau ya kama sati biyu da rasuwar Ramadan wanda yayi daidai da kwanaki sha biyu da jana'izar M Jameel.
Acan gidan Lamiɗo kuwa da misalin karfe sha biyu na rana Hajiya Ruƙayya da Mommy da kuma Khausar na zaune afalo suna hira kamar daga sama suka jiyo Sallamar Hajja Nana da faɗin.
“Assalamu Alaikum”...!

*Kada kyiwa labarin bahagon fahimta. Wasu abubuwa na cikin Labarin gaba ɗaya gaskiyane ya faru da gaske. Ina mai roƙonku da Allah kuyiwa Jameel Addu'o'i Allah ya jiƙamsa da rahama ya kuma toni asirin waɗanda sunka saceshi suka kasheshi kisa mai muni. Ku sashi a addu'o'i ku, domin Wallahi tallahi rasuwar Jameel gsky ne kuma ya faru, da gaske wanda nasan mafi akasarin mazauna Adamawa zasu san labarin rasuwar Jamilu matashi mai Kekkyawan ɗabi'un sun kashewa sun bar mahaifiyarsa da ƙunshin a zuciya, sun sa mahaifinshi a rauni mai ciwo. Yah Allah ka jiƙan Jamilu kayi masa rahama da gafara, ka tausashi zuciyar iyayensa ka ƙara zamewa mahaifiyarsa Gatan*


🤝🏻KADA KUMA KU DAMU ZAKUSHA MAMAKIN YADDA LABARIN ZAI SAKU FARINCI DA SHAUƘI ZAKUSHA MMKIN YADDA LAMARIN ZAI BADA CITTA, KU DAI KU BIYONI KUSHA LABARI, WACCE BATA BIYA TA BIYA.


By
*GARKUWAR MARUBUTA*SAKAYAH

33

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇



Spbnɗettett. Cikin ɗan sakin fuska Mommy ta miƙe tare da cewa.
“Wa'alaikum Salam Hajja Nana sannunku da zuwa”.
Hajja Nana na zama aɗaya daga cikin kujerun falon tace.
“Yawwa Aysha sannunki”.
Cike da farin ciki Khausar ta miƙe tare da riƙe hannun Dije kana ta jata suka zauna akan 2sitter.
Murmushi Mommy tayi tare da juyawa ta shiga kichen.
Ta kawo mu abin taɓa,
Fuska ɗauke da murmushi Khausar dake riƙe da hannun Dije ta juya tare da kallon Hajja data zuba mata Ido, cikin sanyi tace.
“Maraba Hajja Nana ya gida ya Baffa Liman, Baffa Jauro,Baffa Sadu, Baffa, Garga Yaya Sadik? Duk kowa da kowa dai”.
Harara Hajja Nana ta watsa mata kana tace.
“Sai yanzu kika ganni wacce ta dameki ai gashi tun shigowarta kika jata jiki, kuke gaisawa idan kin matsu da sanin yanda suke sai kije ki duba su da kanki”.
Uhum kawai Khausar ce tare da loggobar da kai dan har yau bata dawo dai-dai ba cikin sanyi tace.
“Kai wannan tsohuwa ke dai akwai ki da kishi, da mita ina ce dai yanzu gashi na gaishe ki amaimakon ki amsa shine sai kin cakaleni”.
Riƙe haɓa Hajja Nana tayi tare da maka mata Harara kana tace.
“Yo ki riƙe abinki mana ko wata tsiyar gaisuwar ki zai min?”.
Ta ida maganar tare da sauƙa ta ɗauki Cup ɗin tea da Mommy ta zuba mata kana ta kurɓa”.
Taɓe baki Khausar tayi tare da cewa.
“Oho dai ai ko bazai miki amfani ba kin nema bare ma amfanin zai miki”.

Mommy da fitowarta daga kichen kenan tayiwa Khausar alamar tayi shiru kana ta zauna gefen Hajja Nana cike da girmamawa ta gaisheta tare da tambayar mutane gida.

Miƙewa Khausar tayi tare da riƙe hannun Dije tace.
“Zo mushiga ciki”.
Saurin Kallonta Hajja Nana tayi tare da faɗin.
“Dawo ki zauna”.
Tsayawa tayi tare da kallon Hajja Nana still hannunta na riƙe da Dije tace.
“Toh me kuma zan miki?”.
Sassauta murya Hajja Nana tayi tare da faɗin.
“Ke kam ki dawo ki zauna mana”.

Sake hannun Dije tayi tare da tsare Hajja Nana da ido kana tace.
“To wai mai zan miki zamuje muyi hiranmu irin na ƴan Uwanta kema kuyi hiranku mana ko sai dole na zauna ne?”.
Harara Hajja Nana ta maka mata tare da cewa.
“Wato ke dai daga zuwana sai kinsa mun raba hali, ko ba a isa ace yi kiyiba sai kinyi musu?”.

Kallon Khausar Mommy tayi tare da cewa.
“Ke dai ki dawo ki zauna mana koma menene ai zaki ji”.
Kai ta gyaɗa tare da janyo hannu Dije suka zauna gefen Mommy ya zamana Khausar na fuskantar Hajja Nana.
Hajja Nana kuwa zamanta ta gyara tare da fuskantar Mommy Cike da isa, gadara, taƙama, Iko, kana da Power da take jin tana dashi akan Khausar da kuma rigima irin ta tsofaffi tace.
“Alhamdilillah mun godewa Allah daya nuna mana lokacin da Khausar ta gama karatu lafiya”.
Cikin sauri Khausar ta kalleta tare da cewa.
“An gama karatu lafiya ko kuma anfara taka matsayin karatu? Ko tsakiyar karatu ma naje ne bare akai ga maganar gamawa?”.
Wani kallo Hajja Nana ta watsa mata tare da cewa.
“Karatun ƙa'ida kam nasan angama shi tunda kinyi haddar Alkur'ani kin sauƙe sannan kinsan, Ahallari, Kinsan ishmawi, Kinsan Fiqhu, Kinsan Arbauna, Kinsan Sira da sauransu yanzu wani karatu ya rage miki”.

kallonta kawai take sai data gama jerawa kafin tace.
“Karatu kam wanda ya ragene yafi yawa aisharan fage kawai nayi acikin karatu”.
Harara Hajja Nana ta watsa mata cikin yanayin zafinta tace.
“A'a sannu Al-huda-huda sarkin karatu dole kika ce sharen fagi kikayi mana, tunda kin samu anbarki kinyi wannan ɗin”.
Sake baki Khausar tayi tare tura baki kana tace.
“Ikon Allah dana samu anbarni nayi da mekike nufi kenan, ko kuma dama kece zaki tsara min abinda zanyi?”.

Gyara zama Hajja Nana tayi cikin ƙanƙance Ido tace.
“Ke ko kunya bakya ji dube ki fa duk kin gama girma agida shekarunki kusan Ashirin ai wannan ma taumaka miki za'ayi dan kin gama tsufa”.

Buɗe baki Khausar tayi tare da kallon kanta kana ta kalli Hajja Nana cike da Isa Hajja Nana tace.
“Kalleni da kyau yo ƙarya na miki, ƙannen bayanki nawa aka Aurar wasu da yara bibbiyu wasu kuma ɗaddaya ke kam wannan wani sai dai yace bazawara ce ke dan kin gama girma”.
Wani kallo Khausar ta mata tare da cewa.
“A'a Hajja Nana ya isa haka cin fuska dan wlh bazan juraba.Wanda suka fini dubu nawa ne basuyi Aure ba, sai dai idan A Rugar kune ake irin wannan Auren, amma nikam yanzu ma nayi ƙarama da Aure.
Mommy kuwa kallon Khausar tayi tare da ɗaga mata hannu kana tace.
“Haka naki Khausar kiyi mana shiru”.
Sunkuyar da kanta ƙasa tayi batare da ta sake cewa Uffan ba kawai dai tasan in ba ita ke tare Hajja Nana ba Mommy kam ba abinda zatace tanaji tana gani za'a tauyeta.

Hajja Nana Khausar ta nunata da ɗan yatsa tace.
“Ki kiyayeni bada ke nake magana ba fitsararriya mara kunya!”.
Gyara zama Khausar tayi tare da juya mata manyan Idanunta da kawar da kai gefe.
Murmushi Dije dake gefen Khausar tayi tare da riƙe hannun ta da ido tayi mata alamar ta daina.
Gyaran murya Hajja Nana tayi tare da cewa.
“Aysha Ni dake nake magana bada Khausar ba, ya batun maganar da mukayi tunda Allah yasa tagama yanzu, sannan makon daya gabata Baffanta yazo daga Adamawa aranan daya zo aranan ya koma”.
Sai kuma ta kalli Khausar tare da watsa mata Harara kana ta maida kallonta kan Mommy dake sauraronta tace.
“Toh dama ace yazo da niyyar kwana zamu ƙara so nan, ayi magana to amma ke me kikace tsakaninta da Aliyu ɗan Uwanta!?”.
Ahankali Mommy ta sunkuyar da kanta ƙasa kana tayi shiru cikin yanayin sanyinta da Kawaici, da mutumtaka da kuma kamala tace.
“Toh Hajja Nana wannan magana duk yanda kuka zantar ai hakane Baffanta shine me Aurar da ita, dan haka duk abinda ya yanke akanta shine dai-dai”.

Jinjina kai Hajja Nana tayi tare da tura kallabin kanta kana ta gyara zamanta cikin jin daɗi tace.
“Shima yace min Insha Allah nan da wata ɗaya ko sati uku zai zo idan ya samu sarari zaizo su zanta da Uban goyon yarinyar, shima abashi mutuncinsa tunda shi ya raineta tun tana da wata wata uku shi yamata komai”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da faɗin.
“Bakomai duk abinda kuka tsara yayi Idan har Auren Khausar da ɗan Uwanta Al'khairi ne Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa”.

Cikin sauri Khausar ta tura bakinta tare da cewa.
“Ni dai bana sonshi kuma ke dai Mommy ayita Addu'ar alkhairi”.
Wani kallo Mommy ta watsa mata alamar rufe min baki, shiru Khausar tayi tare da sunkuyar da kanta ƙasa Mommy kuwa kallon Hajja Nana tayi cikin sanyin murya tace.
“Ni dai Allah ya tabbatar da al'khairi idan al'khairi ne Allah ya tabbatar ya kuma zaɓa musu abinda yafi zama al'khairi atsakanin su.
Gyara zama Hajja Nana tayi kana tace.
“Ammen,Kuma Insha Allahu ma alkhairi ne”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.
“Adduar da mukeyi kenan”.
Miƙewa Khausar tayi tare da riƙe hannun Dije da alamun ɓacin rai tace.
“Dije mu tafi”.

Harara Hajja Nana ta watsa mata tare da sake tura daurin Kallabinta gaba kana tace.
“Aikuwa wannan magana ya zama dole ki saurareta tunda batu ne na Aurenki akeyi”.
Cikin ƙankance Ido Khausar tace.
“Nifa bazanyi Aureba ehe ke baki da aiki sai ƙaƙale ƙaƙalen magana ina ruwanki da batun Aurena!?”.
Afusace ta kalleta kana tayi Ƙwaffa tare da cewa.
“Aikuwa dan Ubanki nike da ruwa dake kuma dole kiyu Aure”.
cikin tsirawa Hajja Nana ido tace.
“Amma dai na faɗa miki ki daina zagin mahaifina Aure kuwa idan Allah ya nufa zanyi amma ba wanda kike cewa ba kam!?”.
Ajiyar zuciya Hajja Nana ta sauke kana tana kallonta bako ƙyaftawa sai kuma ta sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.
“To wa kike so ki Aura?”.
Juya ido Khausar tayi tare da cewa.
“Aini nasan wanda zan Aura, kuma dan haka babu ruwanki dani sai kace ke lokacin da zaki yi Aure zaɓa miki wanda zaki Aura akayi ba ke kika zaɓa da kanki ba!”.

Girgiza kai Mommy tayi tare da nunawa Khausar hanya da hannu alamar tabar wajen ita har ga Allah bata so ma Hajja Nana ta tsaida Khausar a cikin mgnar ba in bana tsohuwaba taya zata tsaida Khausar bayan tasan yadda suke da juna.
Tura baki Khausar tayi tare da jan hannun Dije dake murmushi sam bata gajiya da kallon Dramer Khausar da Hajja Nana.
Khausar da Dije na isa ƙofar Bedroom ɗin zasu shiga Akuma dai-dai lokacin Asma'u tayi sallama cike da ladabi tsugunna agaban Mommy ta gaisheta Cike da kulawa Mommy ta amsa tare da tambayarta ya Umminta ta amsa da tana lafiya.
Kana ahankali ta maida kallonta kan Hajja Nana dake cin Inabi tace.
“Hajja Nana inayini fatan kunzo lafiya?”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa.
“Lafiya lau Alhamdulillah Allah ya miki albarka kar dai ki riƙa ɗaukar hallayar wasu ƙawaye na tsiwa”.
Ɗan murmushi Asma'u tayi kana cikin sanyi ta gyaɗa kanta Khausar dake tsaye bakin ƙofa ta wani ɓata fuska tare da kawar da kai gefe.

Miƙewa Asma'u tayi ta nufi wajensu Khausar suka shiga Bedroom cikin ɗan sakin fuska da sanyi Asma'u tace.
“A Dije sannu da zuwa ya gida ya mutanen Jauro yaya!?”.
Murmushi Dije tayi cikin yanayin sanyin ta tace.
“Duk lafiya lau?”.
Kallon Dije Khausar tayi kana cikin sanyin tace.
“Ayyah Dije yayan Asma'u Malam Jameel Allah ya masa rasuwa kwanan nan ƴan Kidnapping suka kashesa!”.
Cike da tausayawa Dije tace.
“Ayyah Ubangiji Allah yajiƙan sa da rahma sukuma Allah ya tona musu asiri”.
Atare Asma'u da Khausar suka amsa da.
“Ameen”.
Asma'u kuwa Idanunta ne suka ciko da ruwan hawaye.
Cikin sanyi Khausar ta dafa kafaɗar ta kana tace.
“Dan Allah Asma'u kiyi haƙuri kin sani babu abinda Yah Jameel ke buƙata awajenmu face addu'a Insha Allah Yah Jameel na cikin rahamar Allah”.
Jinjina kai Asma'u tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Insha Allah muna yi kuma zamu cigaba dayi”.
Miƙewa Asma'u tayi tare da kallon khausar cikin sanyin murya tace.
“Toni zan tafi”.
Da sauri Khausar ta ɗago kanta cike da kulawa tace.
“Sauri-sauri haka”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tare da lumshe Idanunta cikin sanyin murya daya zame mata jiki tace.
“Wallahi gidan Innayi nake son zuwa dama na biyo ne akan ince muje ki rakani kuma sai na ganki da baƙuwa, shiyasa nayi shiru bance komai ba”.
Ajiyar zuciya Khausar ta sauke tare da tsira mata ido cikin fesar da numfashi tace.
“Ayyah wallahi kuwa badan baƙuwar ba ai da naje na rakaki amma lafiya kuwa?”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tana gyaran zaman hijabinta tace.
“Eh Ummi ce ta aikeni wajen Innayi akan Inje wajen.
Yaya Moddibo yau kusan sati kenan bai sake zuwa gidanmu ba sannan kuma Innayi ma ta kirata tana faɗa mata ko cikin gida baya fita”.
Jinjina kai Khausar tayi cike da tausayinsu tace.
“Allah sarki Malam Moddibo dole ya shiga cikin tashin hankali da alhinin rashin.
Yah Jameel insha Allahu jinin Yah Jameel da hakkinmu ba zai taɓa bari wannan mutanen su samu salama acikin rayuwarsu ba!”.
Kai Asma'u ta gyaɗa cikin sheshsheƙan Kuka tace.
“Tabbas sun cutar da rayuwar mu, cuta mafi muni sun zalunce mu kana sun ɗauke mana duk wani farin ciki da walwalarmu. Yah Jameel shine Komai namu Yah Jameel shine fitilar dake haska zukatanmu amma dare ɗaya suka rabamu da wannan hasken kuma jigonmu”.
Cikin sanyi da tausayawa Dije tace.
“Asmau'u kiyi haƙuri Allah baya zalunci sannan baya bari ayi zalunci da sannu Ubangiji zai fallasa asirin wanda suka aikata wannan ta'asar sannan sai sun wulaƙanta wulaƙanci mai muni insha Allah”.
Cikin sanyi da Khausar da su kaji mutuwar ya dawo musu sabo suka hada baki wajen cewa.
“Ameen”.
Miƙewa Asma'u tayi tare da faɗi.
“Bari na tafi dan Ummi tayi ta kiran wayarsa baya ɗauka sannan itama Ummi baki daya bata jin daɗin jikinta sosai ta dawo tamkar majinyaciya.
Khausar sai kinga gidanmu baki ɗaya duniyar bata mana daɗi”.
Cikin sanyin da rarrashi Khausar tace.
“Ayyah Asma'u am haka rayuwa ta gada Ubangiji Allah ya jikan Yah Jameel da rahma mu kuma Ubangiji yasa mana dangana azuciyarmu sannan mu cigaba dayi masa addu'a gatan da zamu nuna masa kenan”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana tace.
“in sha Allah, na tafi”.
Kai Khausar ta gyaɗa sannan ta kalli Dije tace.
“Muje mu

70 / 140

Chapters