Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Sakayya Complete Hausa Novel by Aisha Aliyu Garkuwa

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Free Novels Online (Read & Download)

Chapter   79 / 140

234K to 237K   out of 417.8K words

samu dama kizo zamuyita, yanzun sauri nake”.
Ta ida maganar tare ɗago kanta.
Idanunta ne suka sauƙa cikin idanun Moddibo.
Atsorace ta zira Idonta cikin nasa tare da juya su acikin nasa wanda hakan ya zama kamar hararansa tayi ita kuma cikin mamakin yadda ya rame ya wani zama shiru, ne yayi matuƙar bata mamaki da tausayi domin da dane da tuni ya danna mata harara.
Cike da tsoro ta janye kwayar idanunta daga garesa, tana mai mamakin sauyinsa rayuwa, cikin wani irin sauri ta nufi ƙofar falon yayin da jikinta ke tsuma Muryanta na rawa tace.
“Ummi ni na tafi”.
Kallon yanda ta nufi ƙofar Ummi tayi kana ta kallo Moddibo da har zuwa lokacin idanunsa ke ƙasa da mamaki tace.
“Ya da sauri kamar kinga Dodo?”.
Kai ta girgiza batare data juya ba tace.
“A'a Ummi nikam na tafi”.
Cike da kulawa Ummi tace.
“Toh ki tsaya Kiyi breakfast mana”.

Kai ta girgiza still jikinta na tsuma tace.
“A'a Ummi Allah Mommy na za tayi faɗa idan na daɗe”.
Jinjina kai Ummi tayi kana tace.
“Toh shikenan nagode ki gaida Mommy ki gashi kin ki kitsaya kiyi breakfast”.
Da sauri tace.
“Allah Ummi sai da nayi breakfast agida kafin na fito”.
Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.
“Ki gaida Mommy naki da Raudat dasu Haiydar”.
Cikin sauri ta fice daga falon bayan tace zasuji.

Moddibo kuwa ahankali ya jinginar da kansa da jikin kujeran tare da lumshe Idanunsa kana ya cije Lip ɗinsa na ƙasa, sai kuma yayi saurin buɗesu sabida ganin surar jikinta da yayi ziraran miraran.
Gashi da zaran yaji muryan yarinyar zai riƙa jin wani irin abu mai wuyar fassarawa kana lokacin da ƙwayar idanunsu suka haɗu babu abinda suka hango masa face.
Ƙirjinta tamkar zasu tsole mishi idanu.
Asma'u Mommy tasa ta kawo masa ɗan waken da sukayi sai ruwan Tea ba laifi yaci danwaken da ɗan dama kana yasha ruwan Tea.
Malam Ahmad ne yashigo tare da yi masa addu'ar Allah ya tsare miƙewa yayi ya fita kana yaja tsohuwar motarsa zuwan gidan Abba yana isa yayi Hong mai gadi ya buɗe masa Parking Yayi aharabar gidan kana yashiga sashen Abba bakinsa ɗauke da sallama ya shiga falon Cike da kulawa Abba da Hajiya Turai dake zaune gefensa suka amsa masa.

Anutse ya ƙarasa tare da zama gefen Abba cike da kulawa Abba yace.
“Aliyu ka ƙara so?”.
Jinjina kai Moddibo yayi cikin sanyin murya yace.
“Eh Abba ina kwana ya ƙarfin jikin”.

“Jiki da sauƙi Aliyu”.

Bayan sun gama gaisawa Abba yayiwa Moddibo duk kan wasu bayanai kana ya bashi wasu takardu da duk wani abu daya kamata sai da Abba ya masa bayani.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.
“Toh Abba ni zan tafi”.
Ahankali Abba ya sanya hannu a aljihu tare da ciro key mota sabo dal ƙiran PRADO ya miƙa Masa tare da cewa.
“Ga wannan Aliyu za'a kaika Airport dashi, in Manu driver ya dawo kuma gidan ku zaije ya ajiye maka ita”.
Cikin sauri Moddibo ya ɗago kansa tare da Kallonsa.
“Abba mota kuma?”.
Kai Abba ya gyaɗa masa alamar eh.
Cikin sanyi Moddibo ya sake kallon key motar kana yace.
“Abba to ai ina da mota”.

Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.
“Uhm-Uhm Aliyu kenan. Ɗan Allah kada kayi min gardama ka karɓa kawai ka sanya albarka aciki”.
Sunkuyar da kai Moddibo yayi batare da da yace Uffan ba.
Kallonsa Hajiya Turai tayi kana tace.
“Ka karɓa mana Aliyu ai yanzu kam an zama ɗaya”.
Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.
“Toh shikenan Abba Nagode Allah yasaka da Akhairi Ubangiji Allah ya mayar maka da dubunsa”.
Murmushi Abba yayi kana yace.
“Ameen”.
Nan take ya ɗauko takardun motar ya miƙa masa tare da cewa.
“Jiya mukayi magana da Alhj Abubakar nasa ya kawo min da yamma gatanan lafiyarta ƙalau anyi mata dukkan abinda ya dace”.
Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.
“Nagode Abba Allah yasaka da alkhairi ni zan tafi”.
Ahankali Abba yace.
“Allah ya tsare Aliyu Allah ya bada abinda akaje nema”.
Ameen ya amsa kana ya miƙe Abba ya rakasa da kansa ya buɗe masa bayan motar ya shiga, sabuwar motarsa sosai motar ta burgesa duda bai wani damu da bakin abuba, amman collor bakin yayi masifar kyau dan sai sheƙin sabunta takeyi,
Manu ne ya shiga yaja motar suka fita.
Kai tsaye gidan Malam Arɗo ya wuce dashi bisa umarninsa.
Sallama yayi masa kana daga nan suka ɗauki hanyar da zata sadasu da cikin Taraba Jaligo ja gari na Baba Abasu babban birnin Gembila kenan wanda kuma tsakanin local government ɗin nasu zuwa cikin ƙwaryar birnin Taraban tafiyace ta musamman.
Koda suka isa cikin Taraba, basu tsayaba suka nausa hanyar Adamawa Yola.

Jauro yaya
Baffan Liman ne zaune agaban Hajja Nana cikin sanyi murya da ladabi yayi ƙasa da kansa tare da cewa.
“Hajja kiyi haƙuri bai kamata ace kina fushi akan abinda bai kai ya kawoba, wannan al'amari ba wani al'amari mai girma bane bai kamata ace ki ɗauki zafi akansa har haka ba”.
Kallonsa kawai Hajja Nana keyi tana girgiza ƙafa tare da girgiza kai.
Ajiyar zuciya Baffa Liman ya sauke kana ya cigaba da cewa.
“Idan kin lura Khausar fa jika ce agareki ba ƴa bace, kinga kuwa duk ikon ka akan jika yana zama mai rauni, bare wannan zamanin da muke ya bambanta dana baya dan Allah Addah Hajja kiyi wa wannan al'amarin Kyakkyawan fahimta”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana tace.
“Na lura sannan na fahimci Liman da kai dasu Garga, Sadu, Jauro baki ɗaya bakin ku ɗaya akan al'amarin Khausar tun da haka kuka ce ni bani da abinda zance kuje kuyi duk yanda kuka ga dama”.
Ahankali Baffa Liman ya ɗago ya kalleta kana ya sake sunkuyar da kansa.
Cikin alamun ɓacin rai ta cigaba da cewa.
“Amma fa kusa ni ba zata Auri wannan yaron ba, tunda har ta iya buɗe baki ta kalli tsabar idona tace bata son. Aliyu jikina kuma ɗan Uwanta toni babu hannu na akanta kuyi mata yanda take so amma banda Auren mara tushe da asali”.

Gyaran murya Baffa Garga yayi kana yace.
“Dan Allah Addah Hajja kiyi haƙuri shikansa. Muhammadu Jimeta yace zai zo amma yafi so yazo ya sameki cikin farin ciki kada akan batun Khausar ranki ya dinga ɓaci abanza a wofi”.

Fuska ta ɓata tare da Kallonsu ɗaya bayan ɗaya kana tace.
“Idan yayi niyyar zuwa yazo idan kuma baiyi niyyar zuwa ba yayi ta zama tunda shi kansa bayanta yake bi, tun da wai har cewa yake bazai yi mata dole ba”.

Baffa Liman ya sake sassauta muryarsa yace.
“Dan Allah Addah Hajja kiyi haƙuri ki bi lamarin asannu da izinin Ubangiji komai zai dai-dai-ta amma bama son ganinki cikin damuwa”.
Haka suka riƙa Rarrashinta tare da kalamai masu kwantar da zuciya.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa tafiya tsakanin Taraba da Yola tafiya ce mai zaman kanta sai dai bata wuce awa biyu zuwa uku, tuƙi Manu keyi cike da ƙwarewa ga samun sabuwar mota.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya fesar da sassayan numfashi.
Sabida ji yake wani irin yanayi yana lullubeshi gaba ɗaya tunanin J ɗin sa ya dawo masa ji yake tamkar idan ya juya gefen damansa zai ga J ɗin sa, ahankali ya zira hannunsa ya kara volume din ƙira'ar da yake ji acikin Suratul Nisa'i, sai kuma ya koma baya ya jingina bayanshi da jikin Seat ɗin.
Domin idan har ba karatu yake jiba ko kuma yake yi sam baya taɓa samun nutsuwa, saidai kuma ta wani ɓangaren haka nan yake jin wani irin farin ciki da yabar garin Gembila, ji yake tamkar yabar wani yanki da yake da tarin ƙunci, ji yake tamkar yabar wani waje mai duhu da zafi ji yake tamkar ana zare ransa da ruhinsa daga waje mai ƙunci da azaba, kana kamar ana nufar dashi awaje mai tarin nutsuwa da salama yakeji.
Domin tun bayan rasuwar Amininsa garin Gembila tayi masa zafi da ƙunci kana tayi masa duhu baya kallon haskenta gaba ɗaya ya tsani garin, to dama Meya rage masa da garin Innayinsa ce kaɗai sai kuma Ummi dasu Asma'u.

Sai Misalin ƙarfe biyu da rabi ya shiga cikin Adamawa suna isa cikin Adamawa.
Manu yayi Parking A dai-dai Masallacin jum'ae dake cikin Atiku Abubakar shopping mall ɗinsu nan sukayi Al'wala sukayi sallar Azahar Kasancewar hanya zai kama, ɗan tafiya yasa a gaba shiyasa yayi niyar ƙasaru ya haɗa da sallar La'asar domin karfe uku dai-dai jirginsu zai tashi.
Baya jin zai iya cin wani abu haka yasa ya kalli Manu cikin mutuntaka yace.
“Manu sannu da yunwa”.
Cikin girmamawa Manu yace.
“Laa ba komai ai kafin mu fito ma naci abinci”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Muje ka kaini cikin Airport ɗin, sai kayi sauri ka juya, kada kayi dare a komawa”.
Cike da gamsuwa Manu yace.
“Toh”.
Daga nan ya kaishi Airport sannan shi kuma ya fito, ya ɗan samu abin da ya taɓa kana ya kama hanyar komawa Taraba, Gembila.


Ƙarfe uku Dai-dai jirginsu Modibbo ya tashi daga Adamawa zuwa birnin tarayyar Nigeria Abuja.


Alhamdulillah cikin kwanaki huɗu bizi'nsa ya fito da yake business bisa ne ba wuya.
Alhamdulillah ranar Al'hamis da misalin ƙarfe biyu dai-dai jirginsu ya ɗaga daga Abujam Nigeria.
Zuwa Rabat babban birnin ƙasar Marocco kenan

A hankali ya fesar da wani irin zazzafan numfashi dai-dai lokacin da tayun jirginsu ke raɓuwa da ƙasar Nigeria, rumtse idanunsa yayi da karfi sabida wasu irin zafafan hawaye da yaji suna tsastsafo mishi ta cikin dukkan jijiyoyin idanunsa.
Wani irin yanayin da bai taɓajiba duk tafiye-tafiyen da yakeyi yaji yana dabaibaye rayuwarsa haka kawai yakeji kamar ya bar kasar kenan bari na har abada.
Lokaci ɗaya tunanin Jameel ya dawo masa, wanda hakan yasa yayi saurin jingina bayansa da kujerar jirgin.
Yana mai jin wani irin sassayan kuka na taso mishi daga can cikin ƙahon zuciyarsa, hakanne yasa ya fara karatun Alqur'ani mai girma a hankali.

Yayinda mutanen cikin jirgin kuwa kowa keta hidimar gabansa.

Shi kuwa Modibbo tunda ya zauna bai ɗago kansa ya kalli kowaba.
Sabida yanayin da yakeji.

A hankali dai tafiya ta fara nisa, tuni sun kutsa cikin sararin samaniya jirgi ya kama hanyarsa.

Koda akazo tambayarsu me yake buƙata.
Cewa yayi baya buƙatar komai.

A ƙalla sunyi tafiyar awa uku a sararin samaniya.
Zuwa yanzu kam mafi akasarin matafiyan kowa ya nitsu hada-hadar ta ragu matuƙa, wanda zuwa lokacin kuma sauran musu 57 minutes su dira cikin birnin Rabat sabida daga Abuja zuwa can tafiyar awa uku da minti hamsin da bakwai ne cib-cib.

A hankali ya gyara zamansa tare da kallon farin matashi da ya zo ya zauna gefensa wanda bazai wuce sa'anan ba.
Murmushi matashin yayi tare da miƙa masa hannun yana mai mishi wani irin kallo mai cike da tambayo al'ajabi da kaɗuwa.
Shima ɗan murmushin yayi tare da bashi hannu sukayi musabaha.
“Jabeer bin Jabeer Joɗa. Wanda ya kira kansa da Jabeer ɗan Jabeer Joɗa ɗin ya kare mgnar cike da masifar mamaki da zurawa fuskar Modibbo idanu yana matuƙar mamakin kamanninsa.
Shi kuwa Modibbo cikin yanayin sanyi yace.
“Aliyu Youssef Muhammad Mouley”.
Cikin tsananin bayyanar mamaki ya zazzaro idanu waje tare da juyowa garesa da kyau cikin alamu rawan jiki ya juya harshe zuwa larabci yace.
“Yah Salam toh kuma yaushe kazo”.
Cikin ɗan sanyi Modibbo shima juya harshe ih zuwa asalin amintaccen larabci yace.
“Nazo kuma? Nida ƙasata, me zanje yi a Marocco dai zaka ce”.
Kai Jabeer bin Jabeer Joɗa ya jujjuya tare da juyawa yayi mishi mgn da hausa yace.
“Kamar yaya ƙasar kuma?”.
Ga mamakin Jabeer sai yaji Moddibon na bashi amsa da harshen hausa.
“Sabida ni ɗan Nigeria ne girman Nigeria”.
Da sauri Jabeer yace.
“A'a wannan ai ko makaho ya shafa yasan kai ba ɗan Nigeria bane kuma ma sunan da ka fadi ai ya isa shaidar inda ka nufa komawa zaka yi ba zuwaba”. Ya ƙare mgnar da iya haƙiƙanin gskyrsa da rawan jiki.
Cikin ɗan ƙosawa da surutun sa Modibbo yace.
“To sabida me?”.
Da sauri Jabeer yace.
“Sabida kafi kama da Larabawa”.

“Toh gashi kuma kaima da larabawan kake kama”.

Gyara zama Jabeer yayi tare da cewa.
“Kuma ni dai ba fullatanine”.
A hankali shima Middibo yace.
“Minfu mi pullo”.
To zuwa yanzu kam mamakin Jabeer ya tsananta.
Ya buɗi baki da niyar zaiyi wata mgnar kenan aka kirashi a baya bisa dukkan alamu Kakanshi ne da sauri ya tashi ya nufi can bayan.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya fesar da numfashin gajiya da surutun da Jabeer ya sashin.
Tare da fara karatun Alqur'ani mai girma.

Jim kaɗan da tafiya Jabeer sai gashi ya dawo zama yayi bakinsa cike da tarin mgn to amman samun yana karatun Alqur'ani mai girma yasa dole ya haɗiye dukkan rogowar mgnarsa da tarin tambayoyinsa.

A hankali Moddibon ya ɗago manyan idanunsa tare da kallon taswirar kasar Rarat da suka iso tsakiyarta.
Wanda tuni an sanar musu.
Haka nan yake jin wani irin salama da kwanciyar hankali kana da nutsuwa tunda suka shiga yankin ƙasar Marocco yake jin wani irin sanyi da more happy Wanda har ya iya jure surutun Jabeer.
Numfashin mai sanyi ya fesar tare da ƙara ware manyan idanunsa yana kallon garin ta window'n jirgin.
Haka nan yakeji tamkar yabar damuwarsa baki ɗaya acikin Nigeria ya kuma saki dukkan ƙuncinsa a cikin Taraba.
Cikin nutsuwa da kwanciyar hankali yake bin tsarin dogayen benayen gidajen garin da kallo kana sassayan muryarsa na ratsa kunnuwansa yana jin sautin karatunsa da yakeyi jikin suratul Kahf.

Misalin ƙarfe shida saura minti uku rak.
Jirginsu yayi sauƙar angulu a cikin babban Airport dinsu.
Rabat Sale international airport.
Wanda dai-dai lokacin kuma ya dire ayar ƙarshe ta Suratul Kahf ɗin tuni kuma jirginsu ya dai-dai-ta da'irar tsayuwarsa.
Da sauri Jabeer ya kalleshi sai kuma yayi sauri ya mayar kallonshi gefen damanshi ganin har an buɗe ƙofar jirgin.
Juyowar da zaiyi kuwa sai ganin Middibo yayi a tsaye yana jawo jakarsa daga drower dake samansu.
Da sauri ya miƙe shima, sai kuma yaji ana kiransa a baya, da sauri ya nufi bayan.
Shi kuwa Modibbo agogon dake hannunsa ya kalla, da ɗan hanzarin sa ya nufi wajen sabida ƙaratowar lokacin sallan magrib.

A hankali ya fesar da sassayan numfashi, dai-dai lokacin da ya taka step na forko wanda ya fito da kanshi sararin garin Rarat, duk da dai duk Arfica ne amman ƙasar Marocco sunyi mana rata zarrama mai girma, sunada ci gaba na musamman.
A hankali ya furta.
“Yah Salam”.
Sabida wani irin ni'imtaccen iskane mai cike da salama ke ratsashi yana shiga duk ta inda hudar gashin jikinsa yake.
Wani rin amintaccen numfashin mai cike da yanayin sauƙe ajiyar zuciya ya shaka, like ɗan da ya daɗe baiga mahaifiyarsa ba, kuma yayi kuka.
A hankali yaci gaba da taka steps din yana sauƙo ƙasa.

Wani saurin runtse idanunsa yayi lokacin da ya dire tafin ƙafarsa kan ƙasar Marocco cikin yankin Rarat.
Wani irin tsuma yaji naman jikinsa nayi tun daga can cikin jikinsa da zuciyarsa yakejiyo wani irin tsuma.
Wanda ya ta'allaƙa hakan da tsananin yanayin sanyin garin ne.
“Alhamdulillah!!!”.
Ya furta a saman lips inshi sabida, tunda Allah ya halicce shi bai taɓajiba irin yanayin da yakeji a yanzu, ko Saudia yaje bayajin yanayin nan.

Yana mai shaƙar sassayan iskan garin ya fara bin ayarin sauran matafiya.
Yayinda can gefen kuma manyan motocine na al'farma wanda bisa dukkan alamun wani babba akazo ɗauka.

Su kuwa a cikin yanayin gajiya suka ƙaraso inda masu tarɓarsu suke.

Ɗan dube-dube ya yayi.
Da sauri ya nufi wani Balarabe dake jingina da Taxi yana riƙe da ɗan allon tarba wanda aka rubuta Aliyu Youssef Muhammad Mouley.
Yana isa yayi masa sallama.
Cike da tsananin girmamawa Balaraben yayi saurin buɗe masa marfin motar tare da cewa.
“Marhababuka”.
Kai ya jinjina masa cike da gajiya da ƙosawa.
Yasan Taxi Abba ne ya turosa.

Da sauri shima ya shiga Taxi ɗin kana yaja suka fita daga cikin Airport ɗin.
A hankali yayi miƙa tare da jingina bayansa da seat ɗin dai-dai lokacin da suka ratso ta cikin unguwar Ben slimane.
Anƙuwace ta masu alfarma, haka yasa tsarinta na musamman ne.
haka nan yaji yanayin Weather yayi masa masifar daɗi da kyau.

Gashi yanayin damuna ne Iska mai sanyi da ratsa jiki na kaɗawa gashi duk ta inda ka wulga ido bishi yoyin dabinone masu kyan tsari ke rausayawa sunyi kore shar dasu iska na kaɗawa suna rangaji ga kasar garin ajiƙe yake alamun anyi ruwa.

Ƙarfe shida da minti sha biyar dai-dai mai Taxi ɗin ya juya hancin motarsa kan wani gini mai kyau da ɗaukan indo wanda a samansa aka rubuta.
Belere Hotel Rabat.
Kai da ganin masifar kyau da tsaruwan hotel ɗin kasan zaiyi masifar tsada.
Cikin taushin murya ya kalli Balaraben dake riƙon.
Tare dayin mgn da larabcin.
“Muje wani wanda bai kaishi ba”.
Cikin sanin darajar aiki mai Taxi ɗin ya ɗan kalleshi ta madubi tare da cewa.
“Toh".
Daga nan ya juya akalar motar ya ɗauki hanyar da zata sadashi da unguwar Sidi bettache.
Tafiya kaɗan sukayi suka fito kan babban titinsu.
Da sauri Modibbo yace.
“Masha Allah”.
Dai-dai lokacin da
Idanunsa suka sauƙa akan tamfatsetsen masha'hurin hotel mai masifar kyau da tsari daga can sama tsololuwan ginin an rubuta.
Welcome to Sofitel Youssef Mouley hotel.
Da sauri yace.
“Tsaya mu shiga nan”.
Yayi mgnar still idanunsa na kan sunan hotel ɗin da yayi kama da sunanshi hakan don sunan hotel ɗin yaji yana son sauƙa a nan.
Murmushin mai Taxi ɗin yayi tare da cewa.
“Toh ai wannan yafi wancan tsadama”.
Da sauri ya gyaɗa mishi kai tare da cewa.
“Eh shi yayi”.
Ya ƙare mgnar da lumshe idanunsa jin sautin kiransan salla a masallacin dake cikin hotel ɗin.
Haka yasa shima mai Taxi ɗin saurin shiga.

Numfashi mai sanyi ya fesar tare da buɗe Idanunsa daya lumshe kana ahankali.

Wani irin hotel ne mai masifar kyau da tsari da girma duk da cewa a farfajiyar akwai masallaci sai dai ba wani Babba bane, amma farfajiyar babbe ne me kyau da tsari daga gefen dama wajen Parking din Motoci ne wanda aƙalla zai ɗauki motoci settu zuwa saba'in da biyar kana daga jikin doguwar kantamgar kuwa bishiyoyin kwakwane zagaye da ginin daga can gefe kuma wasu irin flowers ne dake wadace da damshin ruwa haka yasa jikinsu sai sheƙi kayi, tafiya kaɗan zaka samu side ɗin shiga Reception ɗin.
Atsakiya daga gefe da gefe kuma hanya ce kana daga baya wani ƙaton gardin ne wanda yana iya hango bishiyoyin dake ciki kana yana jiyo sautin kukan tsuntsaye kala da ban daban.
Ahankali ɗago daga jingina da seat din da yayi.
Yana Jin zuciyarsa na harbawa kaɗan kaɗan cikin sauri mai taxi ɗin ya rufe marfin gefensa cikin sassarfa ya zagoyo gefen da Modibbo yake tare da buɗe masa murfin motar kana fuskarsa ɗauke da murmushi yace.
“Lalle marhaba fatan an ka isa Marocco lfy”.
Cikin sanyin murya da tarin gajiya yace.
“Yawwa”.
Kana ahankali ya ziro ƙafafunsa waje ya sauke aƙasa.
Da sauri ya rumtse idanunsa tare da kuma buɗesu a lokaci ɗaya yaji wani irin abu mai masifar sanyi ya zira

79 / 140

Chapters