Author : Aisha Aliyu Garkuwa Category : Free Novels Online (Read & Download)
mishi ba wai yau Khausar ce matar Sarkin Morocco kuma Malam Moddibo?”.
Hoton dariya Asma'u ta sake tura musu tare da faɗin.
“Aikam ikon Ubangiji yafi gaban haka?”.
Wata mai suna Jidda ce tace.
“Aikuwa dai muma Allah yasamu Adamshin ku Asma'u ku kam kunji daɗin rayuwarku”.
Murmushin Samira Sani ta turo tare da cewa.
“Uhmmm kuma ku godewa Allah a yadda kuke ɗin”.
Da sauri Khadijah Sule tace.
“Sosai ma kam Samira am”.
Amin kuwa cikin sanyi da nadama tace.
“Alhamdulillah ai in Allah ya baka lfy ka gode masa”.
Haka dai suka cigaba da hira acikin group ɗin kowa na faɗin albarkacin bakinsa.
_Daga can gefe kuwa su ne Rafi'a,Tutus kitchen, Mom sayyeed&Noor Tatti Dija chiroma, ne da suka halarci wajen sunan ne suke ta Video da hotuna suna turawa cikin Group ɗin SAKAYYA Team Moddibo da Khausar kam baki yaƙi ruhuwa duk farin ciki ya cika su ganin irin gift da Khausar ta bayar akawo musu._
_Daga can gefe kuma ƴan karatun bati siddan na Allah ya isa kenan da basu biya kuɗi ba suke wiƙi-wiƙi da ido duk hakki ya hanasu sakewa da samun nitsuwa..._
Asma'u dake cigaba da hotuna da wayar Khausar wayar ya ɗauki suwwa ganin sunan Yah Mu'allim na yawo yasa da sauri ta nufi Khausar dake tsakiyar Didi da Momy suna hoto tayi saurin isa gareta kana ta tsugunna zata miƙa mata wayar kasancewar azaune suke haka yasa ta fito a hoton da yayi masifar kyau.
Asma'u kuwa cikin raɗa takai bakinta kunnenta tace.
“Gashi fa Yah Moddibo yana kiran ki”.
“Mu gani”.
Cewar Khausar tana karɓan wayar tare da kaiwa kunnenta tace.
“Assalamu Alaikum Yah Mu'allim”.
Cikin wani irin yanayin na musamman yace.
“Minha kizo ki sameni aɗakina”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh”.
Sai kuma ta miƙe tare da rungume jaririn kai tsaye ta nufi sashen bakinta ɗauke da sallama ta shiga falon nan ta samu Dr Jameel, Dr Zakariyya, Ibraahim,Yah Ali, da Yah Abba da sauran yan uwansa.
Yah Abba na ganinta yayi Murmushi tare da cewa.
“Mai jego kin sha ƙamashi”.
Murmushi tayi kana tace.
“Ai dai kam”.
Kallonta ta mayar kan Ibraahim tare da cewa.
“Ibraahim Yah Mu'allim fa?”.
Da hannu ya nuna mata bedroom ɗin kana yace.
“Yana ciki”.
Ahankali ta nufi bedroom ɗin kwance ta gansa akan gadon yana ganinta ya saki sanyayyar ajiyar zuciya tare da buɗe mata hannunsa.
Cike da begensa ta zauna kusa dashi miƙewa yayi ya haɗa ta da jaririn ya rungumesu ahankali ya riƙa kissing ɗin goshinta zuwa wuyanta da kuma sassan jikinta baki ta ɗan tura tare da cewa.
“Yah Mu'allim ka matsaneni kuma ɗanka ya matse min wajen Theater na”.
Cikin sauri ya saketa kana ya karɓesa ya kwantar dashi tare da jawota jikinsa ya rungumeta sai kuma ya saki sanyayyar numfashi kana ya ruggumeta tsam cike da kulawa da kuma ganin yanayinsa ta shafo sajensa tare da cewa.
“Yah Mu'allim lafiya meke faruwa?”.
Kanta ya tallofo kana ya kalleta ido cikin ido da mamaki take kallonsa ganin yanda idanunsa suka kaɗa sukayi jawur dasu cike da kulawa tace.
“Yah Mu'allim lafiya?”.
Sunkuyar da kansa ƙasa yayi kana ya ɗago ya kalleta tare da cewa.
“Minha na yiwa Abualeey laifi kuma har yayi fushi dani”.
Cikin sauri ta zare idanunta tare da faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Yah Mu'allim laifin me kayiwa Abualeey?”.
Araunane yace.
“Minha nayi mishi babban laifi naƙin bin Umarninsa”.
Cikin tsoro da kaɗuwa tace.
“Ya Ilahi Yah Mu'allim akan me baza kabi umarnin Abualeey ba?”.
Langwaɓar da kansa yayi kan wuyansa yace.
“Saboda kece ban bi Umarnin Abualeey ba!”.
Cikin sanyi da rauni tace.
“Ya Ilahi bana son jin wannan maganar sam maganar babu daɗin ji Yah Mu'allim Kabi Umarnin mahaifinka shine abinda ya dace kuma shine *SAKAYYAR* da zamuyi masa”.
Cikin rauni da karyewar zuciya yace.
“Bazan iya ba”.
Cike da mamakin shin wani irin abu ne me nauyi da girma agaresa da yasa har ya yiwa mahaifinsa gardama tace.
“Haba Yah Mu'allim ya za'a yi kace baza kayi abinda mahaifinka keso ba shin wani irin abu ne?”.
Cikin sanyi ya kalleta kana ya lumshe Idanunsa tare da cewa.
“Saboda yau yake so a bani mulkin Masarautar Mouley ahannuna”.
Cikin sauri da jin daɗi kana da Jimamin yanayin da yake ciki tace.
“Toh mene Yah Mu'allim mulkin ne baka son rikewa ko me meyesa zaka yi mishi gardama?Kuma ai nikam ma ina son mulkin nan meyesa baza ka karɓi Sarautar ba? Kawai ka karɓi mulkin shine abinda ya dace”.
Kai ya jujjuya tare da juya ƙwayar idanunsa acikin nata kana ya riƙo hannunta acikin nasa tare da cewa.
“Ba karɓan mulkin bane matsala Minha”.
Cikin rashin fahimtar abinda ke damunsa tace.
“Toh ka karɓi mulkin mana kayi mishi biyayya akai”.
Hannunta ya damƙe kana yace.
“Ki bari kiji ko menene”.
Fuska ta tsuke tare da cewa.
“Nikam babu abinda zanji Yah Mu'allim kawai kayi mishi biyayya akan abinda yake so ka karɓi mulki Allah ya tayaka riƙo ya baka ikon Adalci kai masa biyayya ka samu lada”.
Cikin sanyi da rauni yace.
“Cewa yayi an bani mulki bisa sharaɗin za'a bani Auren wata mata ya zama ina da mata biyu!”.
Da wani irin sauri ta dafe ƙahon zuciyarta da yayi wani irin harbawa cikin rauni da fusgar magana tace.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”.
Atake jikinta ya fara rawa kar-kar-kar tamkar wacce aka watsawa ruwa ƙanƙara atsakiyar hunturun sanyi kana idanunta suka kaɗa sukayi jawur tamkar garwashin wuta lokaci ɗaya taji numfashinta na Up and down alamar yana shirin barin gangar jikinta jawota yayi ya riƙe ta da damuwa atare dashi yace.
“Kee ki tsaya mana ki nutsu me haka!?”.
Gaba ɗaya ta rikice numfashinta sai fusga yake alamun tana gab da suma saboda tsabar masifar kishi, cikin fusgar numfashi da ficewar hayyaci ta dafe ƙahon zuciyarta tare da cewa.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Yah Mu'allim Aure kuma?,Wata matar za'a Aura maka?,ita?”.
Sai kuma ta tsaya da Maganar jin numfashinta na shirin barin gangar jikinta alamar zata iya rasa numfashinta.
Moddibo kuwa cikin matsanancin mamaki tsoro gami da ruɗu yake kallonta tabbas yasan tana da kishi amma bai taɓa tunanin kishinta yakai wannan matsayin ba.
Cikin sauri ya rungumeta tare da riƙo hannayenta kana yana jijjiga fuskarta yace.
“Khausar Khausar ki nutsu mana ki buɗe idanun ki dan Allah ki tsaya ki fahimci abinda zan faɗa miki”.
Da ƙyar ta iya buɗe idanunta.
Cikin sauri da tsoro ya sake tallafe Fuskarta ganin yanda ta zazzaro idanunta sukayi wani irin ja.
Ahankali ya fara bubbuga kumatunta tare da cewa.
“Dan Allah Minha ki nutsu kiji abinda zan faɗa Miki”.
Cikin rauni murya da bugawar zuciya tace.
“Yah Mu'allim yanzu mata zasu ƙara maka innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”.
Sai kuma ta kife kanta akirjinsa ta saki marayan kuka mai masifan cin rai da zafi kukan data sakene ya temaka wajen daidaiton numfashinta ya tsaya.
Ahankali ya tallafota jikinsa yace.
“Minha shine laifin da nace Miki na yiwa Abualeey saboda nace masa, in dai har sai an ƙara min mata za'a bani mulkin, ni na yafe bana buƙatar mulki abawa Ibraahim nayi alƙwari zan rayu daga Ni sai ke sai kuma ɗan mu da kuma wa'anda zamu haifa nan gaba”.
Khausar kam wani irin kuka mai tsuma zuciya da tsananin kishi take yi.
Moddibo kuwa cikin gaskiya da gaskiya ya cigaba da cewa.
“in dai akan mulkine zan yi Miki kishiya abawa Ibraahim in yaso a Aura mishi Mata huɗu a rana ɗaya, nayi alkawarin bazan yimiki kishiya a kan mulkiba Amman ban miki alkawarin cewa wai bazan Miki kishiyaba dan bansan ne Allah zai tsara a kanmuba a gaba”.
Da sauri ta tashi kana ta buɗe Idanunta cikin rauni da shesh-sheƙa tace.
“Mata fa kace zasu Aura maka”.
Cikin kwantar mata da hankali yace.
“Ba kiji mai nace Miki bane indai mulki ne na haƙura dashi a bawa Ibrahim abarni Ni in rayu dake da ɗana da abinda zaki haifa agaba”.
Ahankali ta shiga sakin ajiyar zuciya Moddibo kuwa cike da tarin ƙaunarta ya cigaba da faɗin.
“Na tabbar kun isheni farin ciki kun isheni jin daɗin rayuwa kun isheni komai batare da mulkin nan ba Ni na yarda zan kasancewa Ibraahim mai bada shawara abawa Ibraahim mulki shine abinda yafi min kwanciyar hankali hakan ya miki kinji daɗi akan haka”.
Cikin matsanancin jin daɗi da farin ciki tace.
“Na yarda in dai har Abualeey ya yarda Bama son mulkin mun bar musu mun yafe musu mulkinsu Mukam Bama so”.
Akuma dai-dai lokacin Jaririn yasa kuka cikin sauri ta kallesa cikin shesh-sheƙan kuka tace.
“Abu J ba ka jiba yana kuka shima baya so a yiwa Mimeeinsa kishiya”.
Cikin sauri ya rungumota jikinsa kana ya haɗa da jaririn ya rungumesu tare da cewa.
“Mu bar musu mulkinsu Minha ba ruwanmu suje can su ƙarata da mulkinsu, su riƙe abinsu abarmu haka mu cigaba da jin daɗi da kwanciyar hankali yafi mana”.
Dai-dai lokacin Ibraahim yayi knowking kana ya sanar masa zuwan Momy da Didi.
Suna shiga Didi ta kallesa Babu walwala atare da ita tace.
“Yanzu Aleeyu ka kyauta kenan ɓacin ran da kasa Mahaifinka”.
Cikin sauri ya mike kana ya tsugunna gaban Didi tare da cewa.
“Didi dan Allah kuyi haƙuri”.
Cikin sauri da rashin walwala Didi tace.
“Shi ya gama yanke hukunci amatsayin sa na Mahaifin ka Sarautace an riga da an baka ita sai kayi abinda kaga zaka iya akai”.
Da sauri cikin shesh-sheƙa Khausar tace.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Didi yanzu kuma harda Mata za'a ƙara mishi?,”.
Cikin tsuke fuska momy ta harareta tare da cewa.
“Dan Allah rufe mana baki, sokuwar banza sokuwar wofi, in ba'a Aure ke aka Auro ki baza ki taya mijinki yanda zai yiwa iyayensa biyayya ba, sai ki tsaya sokonci kina kuka kina cewa an ƙara masa mata matar kashe ki zata yi, ko kuma akan ki zata zauna?”.
Cikin rauni ta fashe da kuka kana ta jingina kanta da bakin gado cikin shesh-sheƙan tace.
“Momy ba zaki gane bane bazan iya rayuwa da wata mace tare da Yah Mu'allim ba”.
Ahankali Didi ta ɗagota kana ta dafa kafaɗarta tare da cewa.
“Kiyi haƙuri Sarauta ce an bashi Mata kuma tunda yace baiso da ɗaya zai zauna shikenan tun da dama bawai shariya ɓace ta tsara haka, al'adace”.
Ajiyar zuciya mai sanyi ta shiga saki tana jin nutsuwa na diran mata shi dai Moddibo kan sa na ƙasa Didi kuwa cikin kwantar mata da hankali ta cigaba da faɗin.
“Allah da kansa ya basu Umarni suyi Huɗu, Uku, Biyu idan kuma ba zasuyi adalci ba suyi ɗaya tunda yace ba zai yi adalci ba laifi.
Mahaifinsa ya yarda an bashi Sarauta batare da anƙara mashi mata ba”.
Cike da matsanancin farin ciki ta mike ta rungume Didi kana tace.
“Nagode Didi Ubangiji Allah ya miki Albarka”.
Cikin sauri ta saki Didi kana ta tsugunna ta fuski Alƙibla tare da yin Sujudur Shukur ta godewa Allah kallonta ta mayar kan Moddibo dake Murmushi ta miƙa masa hannu tare da cewa.
“Yah Mu'allim Alhamdulillah ”.
Martanin Murmushi ya mayar mata yana mai jin wani irin nutsuwa na ratsa sassan jikinsa ganinta cikin farin ciki ahankali yace
“Alhamdulillah”
Murmushi Didi tayi tare da riƙe hannun momy kana ta kalli Moddibo tace.
“Idan ka gama murnan ka tashi ka tafi Fada ana damƙa maka sarauta”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Toh”.
Momy kuwa kallon Khausar tayi kana tace.
“Wuce mu tafi ”
Ta ƙare maganar suna fita.
Cikin sauri Khausar ta miƙe tare da faɗawa jikin Moddibo tayi masa wani Amintaccen runguma sai kuma ta tallafo kansa ta haɗe bakinsu ta shiga kissing ɗin sa ahankali ta zare harshenta cikin nasa tare da riƙe hannunsa Fuskarta ɗauke da maɗaukakin farin ciki tace.
“Ina ƙaunarka Abu J My life is nothing without you”.
Murmushi yayi kana ya lakace mata hanci tare da cewa.
“Shikenan kuka ya ƙare ko?”.
Dariya ta sanya tare da ɗaukan Jaririn tabi bayansu Momy da tuni suka fice kana shi kuma ya fita ya samu su Ibraahim suka wuce Fada.
Aranan aka naɗa masa Sarautar Mouley kana aka ɗaura auren Rahama da saurayinta kana matar da za'a Aura masa aranan aka Aura wa Ibraahim ita Ibraahim kam. baki har kunne cikin jin daɗi da farin ciki aka gama Shagali da daddare aka kaiwa Ibraahim matarsa.
Tun aranan Lalla Hafsat da wasu daga cikin baƙi suka tafi da Rahama kasan cewar ƙanin mijin Lallai Hafsat ne mijinta yasa aka wuce Mexico da ita baƙin suna kuma duk an watse lfy...
Haka rayuwa ta cigaba da tafiya Khausar na samun kulawa mai kyau.
ranan da ta cika sati Uku Alhamdulillah Thearter yayi gwaɓi sosai suka je asibiti aka sake dubawa a ranan sukaje asibiti Alhamdulillah aka duba akace babu matsala yayi kyau saboda jikinta yana da kyau yaro yayi kuɓul-kuɓul gwanin sha'awa Masha Allah.
A ranan da suka cika wata ɗaya da yammaci Khausar bayan ta fito daga wanka ta shirya cikin wani riga da skirt na less me kyau jikinta sai ƙamshi yake ɗan ta yayi kuɓul-kuɓul Masha Allah yayi ƙato gwanin ban sha'awa.
Zaune suke Khausar Innayi da Hajja Nana suke a bedroom.
Yayin da Momy da Raudat ke zaune Side ɗin Didi tana ta shirye-shiryen tafiya nan da kwana biyar masu zuwa.
Ahankali Moddibo ya shigo bedroom ɗin hannunsa riƙe da Jaririn dake tsala kuka kusa da Khausar ya zauna kana ya ɗaura mata yaron akan cinyarta kai ya langwaɓar cikin wata amintacciyar murya me cike da kulawa tare da tsantsar soyayya yace..
“Minha yunwa fa yake ji”.
Ashagwaɓe ta tura baki kana ta langwaɓar da kai tare da cewa.
“Yah Mu'allim ɗazu fa yasha kuma sai yaita tsotseni”.
Akasalance yace.
“Ki ƙara mishi”.
Fuska ta narkar tare da faɗin.
“Toh tunda ya daina kuka a bari sai anjima”.
Ahankali ya girgiza kai kana yace.
“A'a ki bashi yanzu”.
Miƙewa Innayi tayi tare da cewa.
“Khausar bari inje inyi Miki ɗan wake naji kina cewa kina son ɗan wanke tunda kika haihu baki ciba”.
Murmushi tayi kana tace.
“Yawwa Innayi na ayi min shi yaji yaji yayi daɗi sosai sannan asa min da ƙwai da lemun tsami akai”.
“Toh".
Innayi ta amsa tare da ficewa.
Hajja Nana kuwa ido ta zubawa Moddibo lokacin daya zuge zip ɗin rigar Khausar ta baya.
Cikin Mamaki tace.
“Ohhhh ikon Allah”. Ta faɗa asanda taga yayi ƙasa da wuyan rigar Nonon fito, kan yaron ya tallabe ya sawa yaron abakinsa.
Ta cigaba da cewa.
“Gwara ma ni in tattara mu koma in bar muku gidanku. hankalin mu ya kwanta wai nan kai Sarki ne guda".
Juyawa yayi ya kalleta kana yace.
“Toh ce Miki akayi Sarauta anayinsa atsakanin Iyalai ne?
Ai sarauta iya kacinta Fada”.
Cikin taɓe baki Hajja Nana tace.
“Ohhh Allah ya kawo mu zamani ai kai ko A Fada idan zaka samu za kayi musu taɓara”
Murmushi yayi yana shafa sajensa yace.
“Toh Matatace fa,Ko ba matata bace?
Sadaki fa na biya”.
Hararansa tayi tare da cewa.
“Ka biya ko aka biya maka?”.
Dariya maganar nata ya bashi amma sai ya murmusa yace.
“Eh koma dai menene Matatace ni wlh kin isheni da gorin biya min sadaki akayi dan haka ni yau zan biya nawa sadakin”.
Ya ƙare maganar yana jan wayarshi tare da ƴan danne-danne.
Dariya ta sanya tare da cewa.
“Ohhh baki baya mutuwa ai da kai da ita duk bakin ku ɗaya ne”.
Khausar Murmushi take musu tana cigaba da bawa yaron Nono.
Sai kuma ta kalli wayarta jin sautin shigowar saƙo.
Hannunta na hagu tasa ta ɗauki wayar tare da buɗe saƙon.
Cikin tsananin mamaki ta zaro ido ganin alert ɗin 10 million da Modibbo ya tura nata da rubu a jiki.
*Minha ga sadaki na*.
Cikin kaɗuwa tace.
“Yah Mu'allim 10 million fa ka turo min me sanyi dasu, million goma”.
Sai kuma ta ƙare maganar da kallon Hajja Nana dake cewa.
“Da gaske”. Cikin tsananin jin daɗi Khausar tace.
“Wallahi kuwa gasu kin gani”.
Ta ƙare maganar tana miƙa mata wayar da kuma yaron sai kuma ta ruggumeshi tana saki kishi sassayan kiss tako ina a jikinsa.
Ganin yadda ta ruɗene yasa Hajja Nana yarda bawai dan ta fahimci rubutun alert ɗin ba.
Haka tai ta murna tare da godiya, kukan da Keyan ya sakan ne yasa ta saki uban ta karɓi ɗan kana taci gaba da bashi Nono.
Cikin dariya Hajja Nana tace.
“Daga yau ka huta da gori, kuma dole a bani million ɗaya a ciki”.
Murmushin yayi tare da cewa.
“Kawo account inki in baki naki sadakin tunda jikarki na gudun kishi sai in haɗata dake”.
Cikin dariya tace.
“Yoh ina ni ina aure ai na gama aure kam”.
Dariya sukayi baki ɗaya.
Bayan ta gama bashi da kansa ya mayar da Nonon kana ta mike tare da faɗin.
“Kizo muje ki gyara min Siff ɗina ya hargitse”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Toh”.
Tare da miƙewa tabi bayansa da kallo Hajja Nana ta bisu sai kuma ta saki Murmushi tare da ɗaukan Jaririn tana mishi wasa.
Suna shiga tsakiyar bedroom ya jawota jikinsa ya rungumeta yana shaƙan ƙamshin Kwalaccan Sirri da Humran _Aunty Aysha Aliyu Garkuwa_ da tayi amfani dashi sosai ƙamshinta ke zautar dashi yana masifar son ya riƙa shaƙar ƙamshin jinta yana masifar gigita masa tunani cikin wata kasalalliyar murya me cike da shauƙi da fitina yace.
“Minha yanzu dan Allah tsawon kwana nawa kika fara Sallah?”.
Cikin lumshe idanu da yanda lallausan tafin hannunsa ke yawo asassan jikinta ta fesar da sanyayyan numfashi tare da cewa.
“Yah Mu'allim nafi sati biyu da fara Sallah ”.
Ɗan ware idanunsa yayi kana muryansa can ƙasan maƙoshi yace.
“Kina tsoron kishiya kuma kina tsoron kyautatawa mijinki da ɗauke bukatarsa”.
Ashagwaɓe ta ƙyafta ƙwayar Idanunta cikin nasa tace.
“Yah Mu'allim nifaaaa”
Da sauri ya sake ƙanƙameta yana sakin ajiyar zuciya yace.
“Minha kin san dai ina da buƙata bazan iya jiran abinda Likitocin nan suka faɗa ba”.
Cikin sanyi da ɗan tsoro tace.
“Thearter na fa kada ya ɓalle”.
Yana yawo da hannunsa aƙugunta yace.
“Bazai ɓalle ba”.
Ya ida maganar yana zama bakin gado kana ya zaunar da ita kan cinyarsa tare da zuge zip ɗin rigar ta yayi ƙasa dashi kana shima ya cire nashi blanket ya jawo ya rufe su tare da ɗaura bakinsa akan dogon hancinta yana tsotsa kana ya mayar kunnenta yana hura mata sanyayyar iskan bakinsa.
Sai kuma ya tsaya jin tana cewa.
“Yah Mu'allim ina tsoron Theater nafa”.
Muryansa can ƙasan maƙoshi irin na wanda ke cikin tsananin buƙatuwa yace.
“Na sani zan biki ahankali”.
Bai jira jin Abinda zata ceba ya shiga sarrafa ta cike da bege da kuma shauƙi yayin da ya shiga Binta hankali cikin shagwaɓa da tsoro tace.
“Wayyo Yah Mu'allim wajen Theater na zafi fa ina tsoro kar ka ɓalle min ɗinki?”.
Cikin ficewar hayyaci yace.
“Minhaaaaa bazan ɓalle Miki ba ki nutsu dan Allah”.
Ita kam cigaba da zuba masa shagwaɓa da raki tayi tana cigaba dace masa wajen Theater ta sai da ya ɗauki kusan awa ɗaya akanta kafin ya janye jikinsa daga nata ya janyota jikinsa ya rungumeta yana sa mata albarka sai kuma yayi Murmushi yace.
“Matsoraciya sai raki ɗinki ɗinki ɗinki sai raki da tsoro".
Cikin sauƙe ajiyar zuciya tace.
“Yah Mu'allim Allah tsoro nake ji kar ya ɓalle”.
Yana shafa shafeffen cikinta yace.
“Ba abinda zai ɓalla shi Minha”.
Miƙewa sukayi suka shiga toilet sukayi wanka atare bayan