Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Sakayya Complete Hausa Novel by Aisha Aliyu Garkuwa

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Free Novels Online (Read & Download)

Chapter   80 / 140

237K to 240K   out of 417.8K words

masa tun daga tafin ƙafansa har zuwa ƙwaƙwalwar kansa irin dai abinda yaji daya taka ƙafarsa a Airport. cikin sauri ya kuma lumshe idanunsa tare da furta.
“Yah Salam”.
Kana ya fito dai-dai lokacin da mai kira sallah a masallacin hutel ɗin yazo dai-dai wurin kalmar shahada.

Cikin sanyi ya fara bin kalmar shahadar, wanda hakan ya ankarar da mai taxi dinma ya amsa, tare da bin addu'a'o'in da yaji Moddibon yanayi.

Cikin sanyin murya Mutumin yace.
“Sannu da zuwa”. Lokacin da yaga ya ɗan juyo ya kallesa.
Kai Modibbo ya gyaɗa masa tare da buɗe bayan motar ya ɗauki Breafcase ɗinsa tare da jakarsa, da sauri mai taxi ɗin yasa hannunsa ya amshi jakar kan nasa tare da kuma miƙa masa hannun zai amshi Breafcace ɗinma.
Kai Modibbo ya girgiza tare da faɗin.
“Barshi, zasu yi maka yawa ai”.
Cikin jin daɗi yayi gaba tare da
cewa.
“Bismillah kashiga ciki gashi ma Maghariba ta tayi”.
Cike da salama Moddibo yace.
“Bismillah”.
Yayi mgnar tare da nuna masa gabanshi alamun yayi gaba.
Cikin sauri yashiga gaba kana Moddibo yabi bayansa.
Cikin hanyar da flowers ke ajere gefe da gefe sai ɗan mawadacin hanya dake tsakani sukabi.
Ahankali Moddibo ya taka step ɗaya biyu ana ukun ya hau kan barandar Kofar falon.
Ya sanya ƙafarsa na dama aciki tare da furta.
“Masha Allahu laƙuwwata Illah billahi”.
Sosai komai na hotel ɗin keda tsari na Muslunci da burgewa.

Cikin yanayin gajiya ya ƙarasa gaban ma'aikatan dake binsa da kallon ƙurilla.
Bayan sun gaisane ya kama ɗaki, cike da mutuntaka da martabawa suka gama komai, ɗaya daga cikinsu, ya amshi jakarsa dake hannun mai taxi ɗin.
Kana yayi gaba tare dace masu bismillahi.
Cike da gajiya yabi bayanshi.

Lifter suka shiga cikin minti biyu suka isa hawa na biyu inda na ɗakin daya kaman yake.
Ma'aikacin hotel ɗin ne da kansa ya buɗe ɗakin ya shiga kana ya shimfiɗa beshit tare blanket, kana ya wuce da sauran kayan kamarsu Towel da Bathrobe da makilin da Brush sabulu ya ajiyesu bathroom tare da feffesasa Air freshner kana ya fito tare da cewa mishi.
“Sir akwai abinda kake buƙatane?”.
Kai ya jujjuya mishi alamun a'a.
Ganin haka yasa ya fice.

Shi kuwa Modibbo cike da gajiya ya ajiye woyoyinsa yana mai shaƙar ƙamshin Roomfreshner tare da kallon tsarin komai na ɗakin, komai na cikin falon Ash & maroon colour ne mai masifar kyau kama daga Cottins carpet dama kujerun.

Cike da gajiya a shiga bathroom al'wala yayi tare da fitowa da sassarfa.
Lifter ya shiga ya sauƙa kana kai tsaye masallacin dake cikin hotel ɗin ya shiga da sassarfa jin an tada iƙama.
Ya samu tuni sahu forko da na biyu duk sun cika sai ana uku suka tsaya
Suna shiga suka tada kabbara dai-dai lokacin kuma aka tafi ruku'un Farko.
Bayan anyi Sallah an idar Moddibo.
Yayi Adduo'insa na yau da kullum, ya kara da na neman aminci cikin wakilcin da zaiyiwa Abba tare da samun nasara da roƙon Allah yayi riƙo da hannayensa ya bashi ikon riƙe amana.
Yana so ya jira Isha'i amma saboda yanayin gajiya da yake ji bazai iya jira ba yana so yayi wanka duk da cewa garin akwai sanyi,
Amma yana son yayi wanka dan yaji daɗin jin kinsa da sauƙin gajiyar hanya.
A hankali ya yunƙura da niyyan tashi, cikin sauri ya juya bayansa tare da fito da Idanunsa cike da tsananin son tabbatar da ganinsa ya miƙa da sauri saboda gani fuskar da bashi da hauki ko kokonta a kai cewa fuskar J...!


*Littafin dai na kuɗi 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*





By
*GARKUWAR MARUBUTA*SAKAYAH

38

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa.* Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.
Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.
Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya Zaki kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.
KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.
INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin kala biyarne nasha kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA'AURATA.


Da sauri ya juya baki ɗayansa kana ya nufi hanyar ƙofar masallacin ta waje yana ida fita yaga anja motar dake gefe ta wajen masallacin antafi dashi cikin sauri ya sanya hannunsa duka biyu ya dafe kansa yana maimaita duk wata addu'a da tazo bakinsa.

Batare da yace Uffan ba ya juya kansa ya nufi cikin hotel cikin raunin murya yace.
“Meyesa idanuna ke yimin gizo yau kuma J ɗina nake gani”.
Haka yaci gaba da mgnar zuci har ya shiga ɗakinsa.
Baki ɗaya abin ya fara bashi tsoro anya kuwa bai far zaucewa ba. Ya ƙare mgnar zuci tare zamewa ya zauna bakin gadon.
Wayoyinshi guda biyu dake gefen jakarshi ya ɗan juya ya kalla sabida jin ƙaramar tana ruri.
Hannunsa yasa ya zarosu, duk da kiran ya katse. Numfashi mai sanyi ya fesar ganin tarin miss call ɗin Abba, Innayi, Ummi da Malam Arɗo ahankali ya fesar da numfashi tun da yabar masauƙinsa na Abuja gaba ɗaya mancewa yayi da wayoyin suna cikin jaka bai buɗe ba sai yanzu da yaji kiran. Da sauri yayi picking call ɗin Abba da ya sake shigowa.
Cikin sanyin yayi sallama tare da cewa.
“Barka da dare Abba”.

“Barka dai Aliyu ya gajiyar hanya tun ɗazu nake ta kiranka, shiru”.
Cikin lumshe ido yace.
“Alhamdullah Abba phones ɗin ne suna cikin jaka”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauke cike da kulawa yace.
“Amma to ya hanya”.
Murmushi Moddibo yayi kana yace.
“Lafiya lau hanya Alhamdulillah Abba gashi har na isa nayi sallar maghariba, yanzu wanka zanyi kafin sallar Isha'i ta gabato”.
Jinjina kai Abba yayi kana yace.
“Alhamdulillah ahuta gajiya amma kafin nan ka kira Innayi da Malam Arɗo da kuma Ummin ka dan hankalinsu ya kwanta”.
Kai ya gyaɗa cikin alamun gajiya yace.
“Toh Abba Insha Allah zan kira”.

“Wanne hotel ka sauƙa”.
Abba ya tambaya.

Ɗan guntun numfashi ya fesar tare da cewa.
Sofitel Mouley Youssef na sauƙa Abba dan naga Hotel yanada Kekkyawan tsari kuma a binciken da nayi naga yafi kusa da Companyn' namu”.
Cikin gamsuwa Abba ce.
“Sosai ma kuwa, anan kusa da shine ma gidana yake inda nake sauƙa in nazo. Kaima dan ba'a gyarashi bane shiyasa”.
Miƙe tsaye yayi da wayar saƙale a kafaɗarsa yace.
“Amman yanada tsada kam”.
Shi kuwa Abba gyara zama yayi tare da cewa.
“Ka zauna anan zuwa lokacin da za'a gyara gidana dake nan bayan hotel ɗin ƙadan, sai ka koma can, zan turo maka mai gadin gidan zai zo ya kawo maka key ɗin motar da zaka rinƙa zirya dashi, zai kuma nunnuma maka duk abubuwan da suka dace”.
cikin gamsuwa yace.
“Toh Abba sai yazo”.
Daga nan sukayi sallama.
Yana katse kiran yayi dearling number Innayi lokacin da kiran ya shiga Innayi na kan Sallaya bayan ta idar da sallan maghariba tana ganin kiran tace Alhamdulillah kana ta ɗaga tare da kaiwa kunnenta tace.
“Moddibo”.
Lumshe Idanunsa yayi tare da komawa yayi bakin gadon ya kishingiɗa kana yace.
“Na'am Innayi”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe cikin sanyin murya tace.
“Fatan ka isa lafiya?".
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Lafiya lau Alhamdulillah”.
Numfashi ta fesar kana tace.
“Masha Allah cikin Rabat kake ko kuma cikin gefenta kake?”.
Cikin alamun gajiya yace.
“A'a cikin Rabat nake a tsakiyar garinma kuwa”.
Kai ta gyaɗa cikin sauke numfashi tace.
“Wace Unguwar?”.
Hannu yasa tare da shafa sumar kansa kana yace.
“Tsetse amman a hotel ne”.
Kai ta jinjina tare da sauke numfashi tace.
“Ayyah Tsetse kuma kai bansan Unguwar ba”.
Ware ido yayi tare da miƙewa daga kishingiɗar da yayi da mamaki yace.
“Dama to kinsan Rabat ne bare kisan Unguwannin su?”.
Cikin sauri ta girgiza kai kana tace.
“Um-um bansani ba amma ban taɓa jin sunan bane”.
Ahankali yace.
“Ayyah yanzu ina so inyi wanka ne”.
Kai ta gyaɗa cike da kulawa tace.
“Toh shikenan ahuta gajiya”.
Daga nan ya kira Ummi da Malam Arɗo bayan sun gama gaisawa ya shiga toilet, da ido yabi turaren wanka Maclean brush towel pich colour yana kallo komai na ciki sabone Anutse ya fara wankan lokaci ɗaya yaji tsikar jikinsa na miƙewa sabida wanirin sanyin na ratsa baki ɗaya ilahirin jikinsa, cikin sauri yaja dogon tsaki Aransa kana yace.
Anya wannan aljanar yarinyar zata bar rayuwata ta nitsu kuwa, yarinya sai mata da nacin tsiya.
Towel ya janyo ya ɗaura kana ya ɗaura alwala ya fito dai-dai lokacin aka kira sallar Isha'i jikin Dressing mirrow ya nufa ya shafe jikinsa da mai kana ya fesa turare sa masu daɗin ƙamshi kana ya buɗe jakarsa ya ciro Jallabiya Sky blue me taushi kana ya ɗaura hirami kamar ɗankwali ya riƙe farin carbin sa sosai yayi kyau tun da aka sace M Jameel aka kashe sa bai sake yin wankan daya nutsu irin na yau ba yana fita ya nufi Masallaci akayi sallar Isha'i ana idarwa yayi adduo'i kana sai da aka wawwatse kafin ya fito ya nufi cikin ƙoƙarin shiga ya haɗu da mai gadin na fitowa.

Kallonsa mai gadin yayi cike da girmamawa yace.
“Aliyu Youssef Mouley?”.
Ya faɗin sunan da sigar tambaya tare da duba hoton Modibbo da Abba ya tura mishi ta whatsapp.
Kai Modibbo ya haɗa mishi tare da bashi hannu.
Cikin fara'a mutum miƙo hannunsa tare da cewa.
“Assalamu alaikum Yah Mouley”.
Rumtse ido Modibbo yaui domin tunowa da Jalaladdeen ne kaɗai ke kiransa da wannan suna. Sai kuma ya ƙara rumtse idanun da ƙarfi, sabida tunowa da tsawon lokacin da baiji motsin Jalaladdeen ba, tun kafin a sace. Jameel, ya tabbatar babban abune kaɗai zai iya ritsa Jalaladdeen da har zai iya hanashi nemansu na tsawon wannan lokacin.
Cikin sauri ya buɗe idanunsa tare da gyaɗa tsayuwarsa yana jan Carbin hannunsa jin Mutumin na cewa.
“Sunana Habibullah nine mai gadin gidan Alh Bashir kuma nike kanshi in yazo duk inda zaije nike kaishi kuma nida matata ke zaune a BQ ɗin gidan”.
Kai Modibbo ya gyaɗa masa tare da cewa.
“Eh Abba ya gaya min”.
Jinjina kai mai gadin yayi tare da cewa.
“Ganan abinci na kawo maka”.
Kallonsa Moddibo yayi da mamaki yace.
“Abinci kuma?”.
Kai mai ya gyaɗa alamar Eh.
Jinjina kai Moddibo yayi tare da kallon womers ɗin hannunsa yace.
“Toh daga ina aka samu abincin?”.
Murmushi mai gadin yayi kana yace.
“Ai akwai abokin Alh anan lokacin da Marigayi Jameel yazo har ya koma daga can ake kawo masa abinci”.
Lumshe idanu Moddibo yayi cikin sanyi yace.
“Ayyah yayi kyau angode”.
Sannan yayi gaba, mai gadin kuma na biye dashi.

Bisa kujerar ya zauna shi kuwa Habib kai tsaye dining area ya nufa kana ya ajiye mishi ɗan kondon da kulolin ke ciki, kana ya dawo gabanshi tare da miƙa mishi key ɗin mota tare da cewa.
“Ga wannan da ita zamana fita, in kuma baka son draving ga number'n ta sai ka Kur'ani, zanzo in kaika duk inda kakeso”.
Ya ƙare mgnar tare da miƙa masa hannunsa alamun ya bashi wayarsa ya saka mishi number's.
Wayar ya miƙa mishi ba tare da yace komai ba.
Shi kuwa Habib number's sa ya sawa wayar Modibbo kana ya miƙa mishi.
Amsa yayi tare da ajiye wayar.
Shi kuwa Habib sallama yasa kana ya miƙe ya ficee.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya miƙe jin yadda cikinsa ke ƙugi alamun yunwa.
Dinning table ya nufa, kujerar yaja ya zauna tare da zuba abinci kana ya fara ci bayan ya gama ne ya dawo falon.

Lumshe yayi dearling number Abba.
Bayan Abba ya ɗaga sun sake gaisawa ya sauƙe Ajiyar zuciya tare da cewa.
“Toh Abba yanzu me ake ciki idan Allah yakai mu gobe dame dame za'a fara?”.
Kai Abba ya Girgiza cikin yanayin sanyin muryarsa yace.
“A'a Moddibo gobe kam ka huta tun da kaga yau Alhamis gobe kuma jumma'a ne ba aiki a ƙasar tasu dan jumma'a da asabar ne ranakun hutun ƙarshen makonsu, shiyasa dama naso yau ka tafi ka kwana ka huta gobe ma huta sai jibi lahadi in Allah ya yarda zaka fara zuwa Company”.
Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.
“Toh shikenan Abba Allah ya kaimu”.
Ameen Abba ya amsa kana sukayi sallama.

Miƙewa yayi akan kushin ɗin ya lumshe Idanunsa a hankali yayi miƙa da alamun gajiya kasancewar yayi doguwar tafiya sannan dan kusan wuni yayi a zaune, da fari akan ƙarfe tare jirginsu zai tashi. Ashe tun dare sun mishi text sun caza lokacin tashin sun meda sai biyu zasu tashi bai ganiba, saida yazo Airport ɗin, shiko yanaga komawa ciki wani jidaline shiyasa ya zauna anan kawai.
To hakan ne yasa ya wuni a zaune, shiyasa gaba ɗaya gaɓoɓinsa ciwo suke masa ahankali ya gyara kwanciyar sa still Idanunsa na lumshe cikin sauri ya miƙe kana ya tashi ya zauna numfashi mai zafi ya fesar, tsaki yaja kana ya miƙe tare da nufar ƙofan Falon ya fita yana mgnar zuci Mayya jarabebbiya nan ɗinma sai kin adaddabeni.

Ahankali ya tsirawa coumpund ɗin ido zuwa wajen ganin yanda fitilu suka haska wajen kamar rana komai na hotel ɗin abin burgewane da ban sha'awa ne ahankali ya fara taka step ɗin farandar yana sauƙa kallon dattijon mai gadin dake zaune daga can wurinsa ya nufa,
Duk da tarin motocin dake wurin Hausa wurin ya cunkushe ba, yayinda kuma kowa harkar gabansa yake.
Hannu ya mikawa tsohon tare da yi mishi sallama.
Cikin tsananin girmamawa tsohon ma ya bashi hannu tare da zuba mishi ido cikin ƙare masa kallo.
Shi kuwa Modibbo a ya buɗe bakinsa tare da ɗan ɗaga sautin muryansa yanda zaiji yace.
“Baba”.
Miƙewa Dattijon yayi tare da da ɗan rusunawa kana ya ɗan ɗaura hannunsa na dama kan kirjinsa tare da ɗan sunkuyawa cike da tsananin girmamawar da ta fara bawa Modibbo haushi ya za'ayi dottijo kamar wannan yake kishi haka, in Habib ya mishi haka zai iya amsa sabida ya girmeshi.
Numfashi ya fesar tare da ɗan sakin fuska jin dottijon na cewa.
“Na'am Alh ya aka yi?”.
Gyara tsayuwar sa yayi kana yace.
“Baba kana zaune kai kaɗai ne?”.
Kai Dattijon mai gadin ya gyaɗa kana yace.
“Eh Alh gacan abokan aikina yanzu sune a bakin gate, ni sai da safe zan koma can kuma, yanzu anan nake”.
Ya ƙare mgnar yana buɗe wani mutun da yazo shiga, saida mutumin ya shiga kana ya kuma rufewa.
Girgiza kai Moddibo yayi yana kallon kalimin Dattijon numfashin ya fesar tare da cewa.
“Sunana Aliyu Youssef Muhammad Mouley, daga Nigeria amma kakata tana kirana da Moddibo zaka iya kirana Modibbo”.
Jinjina kai Dattijon mai gadin yayi yace.
“Ayyah Alh yayi kyau”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe cikin sanyin murya yace.
“A'a ba sai kace min Alh nan ba ka kirani da sunana kawai”.
Kai ya gyaɗa yana jinjina karamcinsa Aransa yace yana nan kamar ƙaninsa Ibrahim Youssef Muhammad Mouley. Ibrahim bashi da girman kai sai dai shi Ibrahim yafi wannan dariya afili kuma sai yace.
“Toh Moddibo”.
Murmushi Moddibo yayi kana yace.
“Yawwa ai yafi sannan kuma akwai abinci da aka kawo min so naci yamin yawa, kaje ka ɗauka mana sai kaci sabida kada ya lalace!”.
Cikin tsananin mamaki da ganin tsananin karancin Dottijon ya haɗa kai, tare da amsar key ɗin ɗakin da Moddibo ke miƙa masa, cike da yarda aminci yace.
“Ngd Ngd matuƙa Modibbo, Allah ya kara girma ya kare zuriyar Mouley baki ɗaya”.
Gyara tsayuwa yayi tare da girgiza kai yace.
“Amin Ya Allah”.
Gefensa mai gadin yabi kana yace.
“Bari na ɗauka to”.
Ya faɗi tare da nufar cikin, cikin nitsuwa

80 / 140

Chapters