Author : Aisha Aliyu Garkuwa Category : Free Novels Online (Read & Download)
kana ya fuskanceta da kyau yace.
“Kina da iko da ita mana muma kam mu aike kike da iko damu amma ana neman alfarma awajenki gacan Baban yaron ma awaje sai hawaye yake zubarwa yana neman alfarma acikawa dansa wasiyyar sa”.
Daga waje ta jiyo sheshsheƙan Kukan Abba cikin sauri ta miƙe ta nufi ƙofa ta fita kusa dashi ta zauna cike da tausayawa tace.
“Kuka kuma kake Alh Bashir?”.
Cikin sheshsheƙa Abba yace.
“Ya za ayi ba zanyi kuka ba burin da Jameeluna da kuma fatan da yake so yana tangarɗa koda aranan da muka rabu na ƙarshe yace min shine babban burinsa daya rage aduniya”.
Cikin zubda hawaye ya cigaba da cewa.
“Yace babban burinsa yaga Moddibo yayi Aure kafin nasa Saboda Aliyu yana buƙatar mace yana buƙatar ayi masa Aure sai dai Allah bai nufa Jameelu na zai gani ba ina tsoro saboda bani da damar da zan cika masa wasiyarsa”.
Gyara zama Hajja Nana tayi kana ta gyara ɗaurin dankwalinta ta sunkuyar da kanta ƙasa kana ahankali ta ɗago Muryanta na rawa tace.
“Na amince ina dai dan nice. To acikawa yaron nan burinsa Allah yajiƙan sa da rahama na amince Ayi aure...
Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N 09097853276.
By
*GARKUWAR FULANI*SAKAYAH
39
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.
Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.
Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwatanta Zaki kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.
KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.
INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA'AURATA.
*Book 2*
*6*
Shiru Hajja Nana tayi kafin ahankali ta ɗago ta kallesu ɗaya bayan ɗaya tace.
“Shikenan ni babu abinda zance acikin wannan al'amari zira ido da kunne nawa duk abinda yaje ya dawo Khausar ita tajawa kanta”.
Ƙwaffa tayi kana ta cigaba da cewa.
“Tunda kuma iyayenta kuce kun amince, to ni dai babu abinda zance bare inyi baƙin jini”.
Kallon Baffa Jimeta daya sunkuyar da kai ƙasa tayi taɓe baki tayi kana tace.
“Yo ni me zai da meni tunda uban daya haifi Aliyu bai damuba yanuna ayi mata yanda take so ai shikenan, tunda bata illar tsintacciyar mage bata mage ba, ɗan da ba'asan Asalinsa ba ba'a san tushensa ba duk abinda ya faru ita tajawa kanta”.
Anutse Lamiɗo ya ɗago kansa ya kalli Hajja Nana cikin sauri yace.
“Insha Allahu ma babu abinda zai faru sai Al'khairi”.
Abba kuwa karɓan maganar yayi ta hanyar cewa.
“Insha Allah Moddibo zai riƙe ta da amana da gaskiya da Izinin Ubangiji Khausar ba zata tozarta ba yanda Khausar ta amince tayi niyyar cikawa Jameelu na wasiyyar sa”.
Ahankali Khausar dake can cikin ɗaki ta lumshe Idanunta zuciyarta na bugawa da Masifaffen ƙarfi.
Cikin sanyin murya Abba ya cigaba da cewa.
“Insha Allahu Ubangiji bazai tozarta taba Allah zai cika mata burikanta na rayuwa insha Allah zata kasance cikin kwanciyar hankali da nutsuwa”.
Kallonsa Hajja Nana tayi kana ta jinjina kai tace.
“Haka kake gani kk? Hmm ta yaro kyau take bata ƙarko, kai yanzu Alh Bashir tunda kuke kasan asalin yaron ne?”.
Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa ƙasa batare da yace Uffan ba.
Ƙwaffa tayi kana tace.
“Hmm ka buɗe baki kai tsaye kace baka sani ba shine magana”.
Kallonta ta mayar kan Malam Arɗo tace.
“Malam kai da suke aiki a ƙarƙashin ka kasan Asalinsa?, kasan waye Ubansa? Kasan inane Ƙasar da suka fito kasan inane Jaharsu? kasan menene tushensa? Waye ubansa waye Uwarsa?”.
Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe kana ya kalleta Anutse yace.
“Ai a al'amarin Aure wannan duka ba magana bane”.
Kai ta girgiza cikin tsira masa ido tace.
“Yanzu ina magana da Malam Liman zai miƙe yace min Allah yace Annabi yace amma ai Aure abin bincike ne ko”.
Cikin sanyin murya Lamiɗo yace.
“Dan Allah Addah Nana kiyi haƙuri wannan tone-tonen basu da Amfani”.
Baki ta taɓe tare da Kallonsa kana tace.
“Eh basu da amfani Ni tunda dai aka samu antsira ba ɗan Mayun bane zata aura, aishikenan sai inzira mata ido ni naɗan ji sauƙi ma akan abin”.
Kallon ƙannenta tayi kana tace.
“Yo ai gaskiya ne na fada da kuka wani tsareni da ido, kuma dole idan gaskiya ta taso a faɗeta da ace ta auri ɗan mayu jikan Mayu ai gwara ɗan shegen tunda taji ta gani tana so ta bone dai tayiwa ƴaƴanta da ahalinta”.
Kai Baffa Liman ya girgiza tare da sunkuyar da kansa ƙasa cike da takaici Hajja Nana ta cigaba da cewa.
“Tunda ta yiwa kanta tabo ita tasani amma Ni dai babu ba kina babu hannu na babu ƙafana na suje can su ƙarata sanda ƴaƴanta zasu ce ina dangin Ubansu ta nemi abin faɗa musu”.
Ahankali Mommy da Lamiɗo suka sunkuyar da kansu ƙasa Khausar kuwa hannunta riƙe da kofin madaran da bata shaba bata ajiye ba ɗumin na ratsa tafin hannunta ta tsirawa waje ɗaya ido ba ƙeftawa.
Ajiyar zuciya Malam Liman ya sauƙe tare da girgiza kai kana cike da ladabi da nutsuwa yace.
“Dan Allah Addah Nana ya za'ayi ana kitse gaba kina warware baya dan Allah wasu furucin ki riƙa sanin abinda zaki riƙa faɗa saboda Manzon Allah (SAW)
_Falyaƙun Khairan Auliyastumu”_.
Baki ta taɓe kana tace.
“Naji naji Liman aini zuwa yanzu ko ƙwaƙwalwar kifi ne dani yaci ace in haddace Hadisai sama da dubu tunda duk motsin da nayi sai kace min ga abinda Allah da Manzonsa suka faɗa”.
Sunkuyar da kai Malam Liman yayi cikin taɓe baki ta cigaba da cewa.
“Ni dai na faɗa ba bakina ba hannu na babu ƙafana kuje duk abinda kuka ga ya dace kuyi. Kai kuma”.
Ta nuna Baffa Jimeta da kansa ke ƙasa kana tace.
“Tunda kaine madadin Uba agareta kace kaji ka gani ko? Sannan kaima”. Ta nuna Lamiɗo daya ɗago kansa cikin haɗe girar sama da na kasa tace.
“Kai kuma kaine wakili kuma Uba data tashi agabansa kai kace kaji ka gani ai shikenan na cire bakina aciki amma dan Usmanu na baya raye bazan bari jinjinsa ya cuta ba”.
Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauke kana yace.
“Insha Allahu ma ba zata cutuba da izinin Ubangiji zai riƙe ta da Amana”.
Baki ta taɓe cike da takaici ta juya cikin ɗaki.
Takalli Khausar da har zuwa lokacin hannunta ke riƙe da kofin madaran Harara ta watsa mata kana tace.
“Ke kam kinyi asara gaki mace har Mace Bafulatana tsayayyar mace Kyakkyawa zubin zamani ƙirar masu tsada amma ace wai ke zaki buɗe baki kice kina son Namiji”.
Cikin sauri Khausar ta ɗago kai ta kalleta.
Harara Hajja Nana ta watsa mata kana tace.
“Ki ɗauke wannan tsayayyun idanun naki akaina Ke zakice kina sonsa wanda baisan dake bama sannan baice yana sonki ba bai damu dake ba wai kice kina sonsa shi zaki Aura”.
Fuska Khausar ta ɓata kana ta kawar da kanta gefe tare da murguɗa mata baki da Ido Mommy tayi mata alamar kar tayi magana.
Tsuke bakinta tayi tare da kawar da kanta gefe, jin lokacin sallar La'asar yayi yasa duk mazan suka miƙe suka tafi masallaci.
Bayan sun daeone suna isa afarfajiyar gida suka zauna Anutse Abba ya gyara zamansa tare da fuskantar su da kyau kana yace.
“Toh Alhamdulillah yanzu dai Kamar mun samawa tufkar hanci amma kuma dai Babban abu da yake tafe damu acikin al'amarin”.
Ya sauke ajiyar zuciya kana ya cigaba da cewa.
“Ayi ƙoƙari ayi abin cikin ƙanƙanin lokaci in Allah ya yarda ya lamunce mana komai abune mai sauƙi agaremu inhar kuma kun shirya”.
Jinjina kai Baffa Jimeta yayi kana yace.
“Bakomai in dai wannan ne mu ba matsala awajenmu tunda abin yazo na wasiyya kuma dama a wasiyyar sa ya roƙa ayi cikin gaggawa sannan ya faɗa ya kara cewa yaron nan yana ɓuƙatar aure”.
Jinjina kai Abba da Malam Arɗo sukayi alokaci ɗaya.
Cike da kamala Baffa Jimeta ya cigaba da cewa.
“Tunda har ya fadi haka to yakamata ayi ƙoƙari ayi abinda ya kamata ni awajena Insha Allah ba matsala tunda dama zan kwana biyu saboda zan samu inji da tsohuwar kasan fatanmu da Adduarmu Allah yasa mu rabu dasu lafiya”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.
“Hakane ƙwarai fatanmu da addu'ar mu rabasu da lafiya domin shi yafi al'khairi”.
Murmushi Baffa Jimeta yayi kana yace.
“Toh shine nake so in Zauna da ita Ni nan awajena duk abinda ake buƙata wanda uba zaiyiwa ɗiyarsa Insha Allah bazai gagara ba komai Ashirye muke Insha Allah”.
Cikin sauri Lamiɗo ya Girgiza kai kana yace.
“A'a Alh Muhammadu ai wannan hurumi nane don Allah dan Annabi kada kuyi min haka Khausar ɗiyace awajena tun tana wata uku nake tare da ita bata da bambanci da ɗiyan cikina inaji tamkar Ni na haifeta”.
Kallonsa Baffa Jimeta yayi cike da kamala yace.
“Anya Lamiɗo za ayi haka kuwa abar maka ɗawainiya?”.
Kai Lamiɗo ya Girgiza cike da dattako yace.
“Haba dai wace irin ɗawainiya kuma?,Meye aciki ai babu wani ɗawainiya acikin al'amarin nan”.
Numfashi Abba ya fesar kana ya fuskance su da kyau yace.
“Ni duka wannan aikin ma na ɓangaren Khausar da Moddibo zanso abarmin domin burin Jameeluna ne ni kungama yimin komai da kuka lamince zaku wanzar da wasiyyar sa bayan rayuwarsa”.
Jinjina kai sukayi kana ya cigaba da cewa.
“kungama yimin komai babu abinda zan iya yi muku tukuici dashi sai dai kubarni inyi dukkan abinda ya dace na fannin Auren nan”.
Murmushi Malam Arɗo yayi kana yace.
“Masha Allah wannan Auren yazo da al'barka Ubangiji Allah yasanya al'khairi”.
Zama Malam Liman ya gyara tare da faɗin.
“Muma kanmu duk al'amarin Khausar hakkinmu ne mu sauƙe”.
Cikin sanyin murya Abba ya kallesu kana yace.
“Ni dai dan Allah na nemi alfarma abarmin wannan aikin nayi”.
Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauƙe kana yace.
“To ai ba laifi duk zamuyi buƙatun ƴa mace suna da yawa”.
Jinjina kai Lamiɗo yayi kana yace.
“Ni dai nafi so abarmin komai na fannin Khausar”.
Dariya Malam Arɗo yayi idanunsa akan su yace.
“Lallai dai kam wannan ai sai dai ɗakuna uku za aware mata irin wannan lissafin.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Insha Allah wannan duk bazai gagara ba da ɗakuna da kuma duk abinda za'a buƙata zanyi”.
Numfashi Baffa Jimeta ya fesar kana yace.
“Allah ya temaka nima insha Allah nan da mako ɗaya zan koma”.
Jinjina kai Abba yayi kana ya gyara zamansa cike da farin ciki yace.
“Ai shi kansa Aliyu ma yanzu haka yana can ƙasar Marocco yana kulamin da ayyukan Company na to Auren ma bazata muke son yi masa”.
Murmushi sukayi jin sigar da Abba yayi magana Cike da farin ciki Abba ya cigaba da cewa.
“Idan yaso bayan an ɗaura auren da kaina zan Kai masa matarsa da izinin Ubangiji sai dai yaga mata dan yanzu ya tafi yana rayuwa shi kaɗai wasu sabbin damuwa zai sake sawa ranshi”.
Cikin sauƙe numfashi Malam Arɗo yace.
“Toh Alhamdulillah gamu da gishiri da goro na tambayar mu na forko muka zo,".
Sai kuma duk suka juyo suka kalli Malam Liman sayi gyaran murya tare fuskantarsu da kyau cikin kamala da dottaku yace.
“Tunda ga yanayin yadda abin ya kasance, mu shammaci Adda Nana, domin bata da alƙibila yanzu tace ta yarda zuwa anjima zata iya cewa ta fasa, don haka mu ɗaura auren nan yanzu-yanzu ana da goron da kuka kawo in dai akwai sadaki a hannunsu tunda ga waliyan yaro ga kuma nata waliyan”.
Ya ƙare mgnar tare da yin ƙasa da murya gudun kada Hajja Nana taji mgnar.
Cikin tsanananin mamaki da farin ciki mara misaltawa Abba Jameel yasa hannunshi cikin aljihunsa jiki na rawa ya zaro sabbin kuɗin yar dubu dubu wanda ya dauko dan yin hisani. Bandir ɗaya ya ajiye a tsakiyarsu wanda har jikinsa na rawa dan farin ciki yace.
“Gashi ina nemawa Aliyu Youseep Muhammad Mouley auren Khausar bisa sadaki dubu ɗari”.
Da sauri Bappa Jimeta ya gyara zamanshi tare da cewa.
“Na bawa Aliyu Youseep Muhammad Mouley auren ƴata Fatima Usman Abubakar Leewal bisa sadaki dubu ɗari.”
Cikin tsananin jin daɗin wannan al'amari da yazo musu da sauƙin aka ɗauka Auren Khausar da Modibbo a yau Litinin a cikin rugar Jauro yaya bisa shaidu Lamiɗo, Malam Arɗo, Malam Liman, da sauran ƙananan Hajja Nana baki ɗaya.
Bayan sun gama gudanar da ɗaurin auren kamar yadda shari'ar Muslunci ta tsara.
Cike da gamsuwa haɗin da tsananin jin daɗin ɗaurin auren Baffa Jimeta yace.
“Toh ba matsala Insha Allah duk abinda ake ciki zan gayawa Hajja Nana kuma zan taushi zuciyarta”.
Sai kuma duk suka juyo suka kalli Hajja Nana dake fitowa daga cikin rumfarta tana mai cewa.
“Uhmmm ta yara kyau take bata ƙarko, ai duk abinda kuke cewa dayi ina jinku badai kun ɗaya aurenba, toh ai hikenan maji magani”.
Cikin Sauri suka kuma kalli juna, ayi mace kunne kamar na maciji duk ƙantar sauti sai taji.
Sai kuma suka maida kallonsu kam Malam Liman dake cewa.
“Toh kisanya albarka kawai”.
Kai ta gyaɗa cike da takaici tace.
“Hmmm Allah ya sanya al'khairi Allah yasa yadda muka ɗauki mgnar marigayi da mahimmanci shima Modibbo a ɗauki mgnar da gsky”.
Bata jira cewarsu ba kuma ta juya cikin ɗakin,
Ida ta zubawa Khausar da tun lokacin da taji Hajja Nana nacewa badai kun ɗaura aurenba ta daskare a zaune, yayinda Mommy mgnar ta daki zuciyarta, dan batayi zaton abin da gaggawa haka ba. Sai kuma duk suka kalli Hajja Nana dake cewa.
“Wlh kinyi asarar ƙuruciyarki da kyanki ji yadda aka ɗaura aurenki kamar na bazawara mara gata”.
Zuwa yanzu Khausar kam bazata iya fahimtar kalaman Hajja Nana ba bare ta bata amsa. Ita kanta Mommy abin ya sata tafiya dogon nazari.
A can waje kuma
Anutse Lamiɗo ya gyara zama kana yace.
“Toh Alhamdulillah dama kwanan ake batun auren Amina nanda kwana goma, tunda an auren Khausar za'a haɗa bikin ayishi lokaci ɗaya, kana akai ko wacce gidan mijinta”.
Kusan a tare duk sukace.
“Allah ya kaimu lokacin”.
Amin Ya amsa tare daci gaba da cewa.
“Insha Allah zuwa gobe ko jibi Insha Allah zan dawo in muyi magana mahaifiyar yarinya”.
Nan dai suka gaba da tsastsara duk yadda abin zai kasance.
Sai Misalin ƙarfe biyar suka bar Jauro yaya ahanya sukayi sallar maghariba sai gab Isha'i suka isa gida.
Kasancewar ranan girkin Hajiya Bunayya ne yasa kai tsaye Mommy ta wuce Sashen ta tare da Khausar wacce take tafiya tamkar kazar da ƙwai ya fashewa, domin jin kanta take tamkar wacce aka rufe da ɗanyen fatan rago, wasu abubuwa na musamman ne ke yawo a jiki da zuciyarta ita kanta ta rasa yanayin da take ciki, kawai dai ta tsinci kanta da rayuwa da Modibbo a cikin zuciyata tun lokacin da taji wai an ɗaura aurensu.
Suna shiga kai tsaye ɗalibta ta wuce, duk da tsalle da Raudat keyi na ganinta ta gaza yi mata mgn.
Sai Mommy ce data ruggume Raudat ɗin.
Ita kuwa Khausar a hankali ta faɗa bisa gafonta, tare da rumtse idanunta da karfi.
Sai kuma ta buɗesu ganin fuskar Modibbo a ranar da sukayi robuwar ƙarshe jujjuya idonta tayi kamar yadda tayi mishi a lokacin, sai kuma ta lumshesu jin wasu