Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Sakayya Complete Hausa Novel by Aisha Aliyu Garkuwa

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Free Novels Online (Read & Download)

Chapter   76 / 140

225K to 228K   out of 417.8K words

Allah kada kayi min maganar kuɗin”.

Numfashi Abba ya fesar cikin sassauta murya yace.
“Aliyu kayi haƙuri dole muyi maganar kuɗin nan kaima kace baka son maganar kuɗin nan to ni kuma me zanyi dasu Aliyu kayi haƙuri kaji sannan dan Allah kayi ƙoƙari ka shirya ka tafi Marocco E PASSPORT naka zaka fitar dan Allah, mu fara neman damar fitan ko ta online zakayi komai, cikin makon nan nakeso ka tafin in Allah yasa ka samu buse”.

Shiru Moddibo yayi lokaci da yaji maganar Bashir ya dawo masa kunne na cewa yayi mafarki da M Jameel sannan yace ya faɗa masa cewa ya taya Abba harƙan kasuwancin sa dogon numfashi yaja mai sanyi duk da cewa baya so ya tafi ya bar Ummi da Innayi amma ji yake ya tsani zaman cikin Taraba da Gembila baki ɗaya Jahar Jaligo ta fita Aransa ga kuma tuno da abinda Bashir di ya faɗa ya sauƙe numfashi cikin sanyin murya yace.
“Toh shikenan Abba bari nayi magana da Innayi da Ummi”.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Toh shikenan idan kunyi maganar dan Allah ka kirani yanzu yanzu ina jiranka”.
Cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Toh shikenan ba matsala”.
Sannan ya katse kiran ya miƙe.

Acan ɗakin Innayi kuwa Hajja Nana na gama shan ruwan ta ajiye Cup ɗin tana sakin ajiyar zuciya.
Ahankali Innayi tace.
“Toh kici abinci”.
Girgiza kai tayi tare da faɗin.
“A'a bazan iya cin abinci ba barni kawai”.
Kallonta Innayi tayi kana tace.
“Toh Wai me ya tsananta ne har ya tayar miki da hankali haka?”.
Ƙwaffa Hajja Nana tayi tare da riƙe haɓa cike da takaici tace.
“Wai fa Khausar cewa tayi bata son Aliyu wai wani take so”.
Gyara zama Innayi tayi kana tace.
“Wai wani waye shi wanda take son?”.
Cikin fushi Hajja Nana taja dogon tsaki tare da cewa.
“Wai wani wai shi Moddibo take so Malamin Makarantar su inji Lamiɗo”.
Cikin sauri Innayi ta kalleta tare da jan dogon numfashi kana ta lumshe Idanunta tare da buɗe su cikin sanyi ta kalli Hajja Nana kana tace.
“Moddibo?".
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.
“Eh Moddibo?”.
Jinjina kai Innayi tayi kana tace.
“Kuma wai malamin su?".
Still Kai Hajja Nana ta gyaɗa mata.

Dai-dai lokacin Moddibo ya isa bakin barandar ɗakin Innayi yana son ya mata bayanin Abba ya kira sa akan yaje yasa yazo wurinta, yana taka step ɗin firko ne.
Ya jiyo sautin Muryan Innayi na cewa.
“Toh Moddibo ai jika nane Hajja Nana.”
Sai kuma tayi murmushi mai cike da jin dadi kana taci gaba da cewa.
“kinga shikenan faɗuwa tazo dai-dai da zama Aliyu jikana aishine Moddibon kinga sai muyi tuwonmu manmu”.
Cikin sauri Hajja Nana ta miƙe tare da kallon Innayi kana ta zare ido sannan ta buga hannunta aƙirji tare da cewa.
“Ji kanki?”.
Jinjina kai Innayi tayi tare da faɗin.
“Eh jikana ne Aliyu”.
Still Hajja Nana na tsaye cikin zare ido tace.
“Shine Moddibo kenan?".
Kai Innayi ta gyaɗa mata cikin tabbatarwa.
Ita kuwa Hajja Nana cikin wani yanayi tace.
“Sannan kuma shine Malamin nasu?”.
Kai Innayi ta kuna gyaɗa mata kana cikin sanyi tace.
“Tabbas shine jikana Moddibo”.
Cike da mamaki Hajja Nana tace.
“Kenan jikanki ne Moddibo wanda Khausar ke so?”.
Still Kai Innayi ta gyaɗaa karo na barkatai tare da cewa.
“Eh".
Cikin wani irin masiyacin kallo Hajja Nana ta kalleta tare da cewa.
“Aikuwa baza ta saɓu ba bindiga aruwa, ai wannan ma ta tsuniyace mara wanzuwa ai wannan ma zancen banza ne, wannan ƙarya ne wlh. Khausar bata isa ba mu zata lalatawa tushe da asalin zuri'a”.
Cikin sauri Innayi ta mike tare da zare ido ta kalli Hajja Nana cike da mmki tace.
“Wannan wace irin kalma kike faɗa?”.
Gyara tsayuwa Hajja Nana tayi kana tace.
“Toh Innare waye bai san cewa jikanki bashi da asali ba, wani mahaukacin ne zai ɗauki ƴa ya baku? waye zai so haɗa zuri'a da jikan ki da bashi da asali! ɗan shege da kika samu akwararo ɗan da ba'asan tushe da Asalinsa ba!!!”.
Cike da matsanancin mamaki Innayi ke kallonta Hajja Nana ta cigaba da cewa.
“Ɗan da ba asan tabbacinsa ba asan asalinsa ba. Yaron da ake da tabbacin cewa ba ɗan sunna bane ɗan zina ne. Shine za ahaɗa zuri'a ta dashi ai wallahi wannan ba zata yuba”.
Ta ƙarashe mgnar cikin yanayinta na ba shina ba sabo.
Cikin fushi da ɓacin rai Innayi ta watsa mata wani irin kallo tare da cewa.
“Ke dakata Hajja Nana ki kama kanki".
Dogon tsaki Hajja Nana taja tare da cewa.
“Bazan kama ba, tabbas abinda na faɗa gaskiya ne, idan har yana da uba to waye Ubansa tun da kuka zauna tsawon rayuwarku shekaru talatin da acikin Garin Gembila waya san Asalinsa wayasan Ubansa wayasan tushensa na faɗa na ƙara fada da ƙarfi shi ɗan shege ne ke kuma magajiya”.
Moddibo dake baranda atsaye ne, yayi wani irin jan numfashi tare da rumtse idanunsa domin tamkar sauƙan aradu haka maganganunta suka ratsa ƙwaƙwalwarsa zuwa dodon kunnensa.
Hajja Nana kuwa cikin fushi da ɓacin rai tace.
“Shegene jikan naki na faɗa zan kuma faɗa”.
Wani irin kallo Innayi ke binta dashi zuciyarta na wani irin tafarfasa ta kalli Hajja Nana kana tace.
“Tabbas babu wanda yasan asalin Jikana sannan babu wanda yasan ina ne tushen jikana amma ke dai baki isa ki jefe mu da mugayen kalamai irin wannan ba”.
Taɓe baki Hajja Nana tayi tare da watsa mata Harara kana tace.
“Na nawa kuma ance da kuturu Allah ya la'ance ka, jikan ki dan kwararo ne ɗa mara tushe da galihu”.
Cikin tsanananin tashin hankali da ruɗu da wani irin tsinkewar zuciya mai tafiya da nunfashi Moddibo ya dafe kansa da hannu bibbiyu tare da rintse idanunsa...!


Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi Hajia ba free book bane dan haka ki saya ki karanta cikin Aminci da salama 1k ne kacal kuɗin samun damar karantawa 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar
biyanki ta WHATSAPP 09097853276



By
*GARKUWAR MARUBUTA*SAKAYAH

36

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇



*Alamomin infection sune kamar haka*. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.
Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.
Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin yana kwaranya. Zaki kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.
KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA sai ya gama yi miki illah. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da sha'awarki, duk kyan kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin sherrin chronic infection ne yar uwa.
INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection cutace mai masifar naci, so yar uwa dole kema ki nace masa da maganin mu, set ɗin10k ne kuma maganin kala biyarne nasha kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin indai ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba dan kun kai mishi amarya a rarake bayan kun san kuɗin sadaki ya ƙara sama. Saboda yanayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi a 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA'AURATA.


Cikin yanayin ɓacin rai Mommy ta ture kanta dake kan cinyar ta babu walwala atare da ita tace.
“To ai shikenan Khausar hankalinki ya kwanta, zagine da abin kunya kunja min, kukan me kuma zaki zo kina min, in banda rashin hankali dama rashin kunya Khausar yaushe Moddibo yace yana sonki yaushe Moddibo ya taɓa zuwa wajenki?”.
Kasa cewa komai Khausar tayi sai hawaye dake cigaba da kwaranya a Idanunta Shar-shar.
Cike da takaici Mommy ta cigaba da cewa.
“Mutumin da ko Amakaranta tsakaninki dashi sai dai faɗa kyara da hantara. Duk abinda ke faruwa ina sane ai ana bani labari amma saboda tsabar shashanci ki rasa wanda zaki ce kina so sai mutumin da bakwa zama inuwa ɗaya!”.
Kuka sosai Khausar ta fashe dashi cikin sheshsheƙan Kukan tace.
“Wallahi Mommy ba haka bane dan Allah ki tsaya ki saurareni”.
Kai Mommy ta Girgiza tare da tsira mata Ido tace.
“Hmmm Khausar kenan me zan saurara kuma, ai babu abinda zanji daga gareki tunda ke kika haifi kanki ke zaki yankewa kanki hukunci sannan ke zaki zaɓawa kanki miji wai ki kalli tsabar Idanunmu saboda tsaurin Ido kice Modibbo kike so to yaushe yace yana sonki?”.
Girgiza kai kawai tayi cikin matsanancin kuka da tashin hankali tace.
“Dan Allah Mommy kiyi haƙuri wallahi ba rashin kunya bane dolene yasa haka Mommy ki sanya mana al'barka acikin rayuwar auren da zamu yi”.
Cike da takaici Mommy ta kalleta kana tace.
“Toh Khausar tambayar da zan miki Moddibo yace yana sonki ko kuma ke kike haukanki?”.
Girgiza kai Khausar tayi cikin rawan murya tace.
“Mommy I don't know either he love me or not”.
Miƙewa Mommy tayi tare da jan dogon tsaki ta fice daga ɗakin ta nufi Falon Lamiɗo.

Khausar kuwa kanta ta kife ajikin katifa ta fashe da sassayan kuka tana sheshsheƙa Ajiyar zuciya Haiydar ya sauƙe tare da kallon Khausar cikin sanyin murya da rashin fahimta yace.
“Addah Khausi ban fahimci abinda Mommy take faɗa ba wai Malam Moddibo kike so ko kuma wa?”.
Kai ta gyaɗa masa Muryanta na rawa tace.
“Eh shi nake so”.
Zare ido Haiydar yayi tare da sanya salati kana yace.
“Toh shi Malam Moddibo yana sonki ne?,”.
Kai Khausar ta girgiza tare da ɗago Idanunta dake jiƙe da hawaye cikin raunin murya tace.
“Ban saniba Haiydar I really don't know”.
Cike da matsanancin mamaki da damuwa Haiydar yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Khausar baki sani ba kuma?”.
Jinjina kai Khausar tayi cikin raunin murya tace.
“Bansani ba Haiydar Bansani ba Haiydar”.
Miƙewa Haiydar yayi cike da takaici yaja dogon tsaki tare da faɗin.
“Wallahi dama nasan hakane babu abinda zaisa in rakoki wajen Mommy”.
Ya ida maganar tare da ficewa cike da takaici da ban haushi.
Cikin rauni Khausar ta miƙe tare da nufar Bedroom ɗinta tana shiga ta faɗa bisa gado tare da sakin kuka mai masifar ɗaci da ƙuna.

Mommy kuwa kai tsaye falon Lamiɗo ta nufa bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon zaune ta samu Abba akan 2sitter.
Anutse Lamiɗo ya ɗago kansa tare da sakar mata da lallausan murmushi kana yace.
“Shatu Ikon Allah mai kuma ya ɓatawa Gimbiya Aysha rai”.
Fuska Mommy ta ɓata tare da narkar da murya kana tace.
“Na lura ma al'amarin Khausar dariya yake baka, baki ɗaya tun jiya Yarinyar nan ta ɓata min rai ta hargitsa min lissafi, sam kakarta bata da kirki tsohuwa ce mai zafi ta saba da iko da gadara akan ƙannenta ta saba da maganar ta kamar yankan wuƙace”.
Kallonta kawai Lamiɗo yake yana murmushi.
Cikin yanayin damuwa ta cigaba da cewa.
“Duk abinda ta faɗa haka ne babu wanda ya isa ya musan ta mata gashi Khausar tazo tayi mata abinda bashi neba ta tafi tana zagina yanzu tana zuwa Rugar nan zata baza sunan Khausar hakan zanji daɗi ne?”.

Murmushi Lamiɗo yayi tare da gyara zaman sa kana ya miƙa mata hannunsa tare da cewa taho nan zo nan Shatuna”.
Maƙe kafaɗa tayi tare da tura baki kana ta narkar da fuska.
Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa.
“Ki zauna mana”.
Kallonsa kawai take amma ba tace Uffan ba.
Ahankali ya sanya hannunsa ya janyo tsintsiyar hannunta tare da zaunar da ita agefen sa cikin sanyin murya yace.
“To amma ai akwai abinda baki sani ba”.
Asanyaye ta kallesa tare da cewa.
“Toh menene ban sani ba?”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da tsira mata ido kana yace.
“Jiya Hajja Nana bata bani dama inyi mata Magana ba saboda yanda ta ɗauki abin da zafi take ta ihu da kururuwa da Masifa sannan dole mu bita ayanda taso”.
Jinjina Kai Mommy tayi tare da sauƙe numfashi.
Cikin sanyin Murya ya cigaba da cewa.
“Tun da kinga tsohuwa ce sannan tana da ƙarfin iko akan Khausar babu yanda muka iya, amma Baffanta ya fahimta domin yau kafin ya koma Ɓadamaya yabiyo nan munyi magana dashi”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana ya kalli Mommy da itama shi take kallo yace.
“Sannan yace ba zai mata dole ba kamar yanda idan Mahaifinta yana raye ba zai mata dole ba kamar yanda zai yiwa ƴaƴan sa haka zai mata saboda yana da ƴaƴa mata da yawa kamar yanda bai musu dole ba haka itama ba zai mata dole ba dan mahaifinta baya raye”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana tace.
“Na sani shi yana da fahimta, amma ita tsohuwar ce gaba ɗaya ba zata fahimta ba”.
Lakace mata hanci Lamiɗo yayi kana da murmushi afuskarsa yace.
“Kada ki damu ɗan zai fahimtar da ita, dan yace ya bata haƙuri sannan idan ta huce zai sake dawowa ya bata haƙuri kuma Insha Allah zata fahimta”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da gyara zamanta kana tace.
“Toh naji ta wannan gefen an samu fahimta amma fa Moddibo baya Son Khausar din ita da bakinta fa tace min bata san yana sonta ko baya sonta ba, ka taɓa ganin Moddibo yazo wajen Khausar ne?”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.
“Eh na taɓa gani mana kwanaki sunzo da Asma'u”.

Girgiza kai Mommy tayi tare da fesar da numfashi kana tace.
“Zuwan da kaga yayi ta'aziyyan Ramadan yazo min domin yace alokacin da suka zo yimin ta'aziyya sun haɗu da Ori da ya muku bayani gawar Jameel toh sun fita bai shigo ya min ta'aziyya ba, shine suka zo da Asma'u yamin amma fa baice yana son Khausar ba hasalima Khausar da Moddibo basa zama inuwa ɗaya”.

Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe tare da gyara zamansa ya fuskanceta tare da cewa.
“Ki nutsu mana Ni nafi so ki nutsu Ayshatu idan kin nutsu sai in miki bayani”.
Marairaice fuska tayi tare da langwaɓar da kai kana tace.
“Toh ai yanzu ma Anutse nake ranka shi daɗe kai nake sauraro”.
Murmushi yayi tare da riƙe tafin hannunta acikin nasa kana ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“Jiya ma hargowar Hajja Nana ce ya hana in miki bayani shekaran jiya baki ji cewa nayi baƙi ba?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh naji”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauke kana ahankali yace.
“Toh Malam, Arɗo ne da Alh Bashir mai Dala Mahaifin marigayi Malam Jameel da kuma Malam Ahmad Baban Asma'u suka zo”.
Jinjina kai Mommy tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Ooh sune suka zo!?”..
Kai ya gyaɗa mata still hannunsa na cikin nata yace.
“Eh”.
fesar da numfashi yayi kama yace.
“Toh kinsan me yaka wo su?”.
Kai ta Girgiza kana tace.
“A'a sai ka faɗa”.

Atake yanayin fuskarsa ya sauya daga murmushi zuwa rauni cikin sanyin murya da rauni yace.
“Magana suka zo akan wasiyyar da Marigayi Jameelu ya bari”.
Saurin Kallonsa Mommy tayi cikin sanyin murya da damuwa tace.
“Wasiyya kuma!?”.
Jinjina mata kai Lamiɗo yayi tare da fesar da numfashi kana yace.
“Eh”.
Ahankali tace.
“Wasiyya kuma Jameel ya bari akan me!?”.

Zamansa ya gyara tare da janye hannunsa ɗaya daga cikin na Mommy ya dafe goshinsa cikin raunin murya yace.
“Jameel yabar wasiyya ne akan Moddibo da Khausar”.
Lokaci ɗaya idanun Mommy suka ciko da Hawaye cikin raunin murya tace.
“Wasiyya akan Moddibo da Khausar kuma to akan me?”.

Jinjina mata kai yayi still muryarsa Araunane yace.
“Tabbas Mahaifinsa ya faɗa min cewa akwai ranan da suka je shi da Moddibo gidansa alokacin saura kwana uku asace sa har yake faɗa masa yafa zaɓawa Moddibo matar da zai Aura Amma shi kansa Moddibo bai sani ba domin koda Jameel ya faɗa murmushi Moddibo yayi alokacin har yake cewa Alhaji Bashiru. Abba kaji fa wai ni J zai za ɓawa mata kamar wani yaro ko makaho”.
Lumshe ido Lamiɗo yayi cikin rauni ya cigaba da cewa.
“Alokacin Abban sa yace ya faɗa masa wace mata ce sai Jameelu yayi dariya yace sai ya dawo asirri zai faɗa masa to bayan da ya dawo sai yace wa mahaifinsa dan Allah Abba ina neman alfarma acikin kwanakin nan domin wata ƙila akwai abinda zai iya faruwa acikin kwanakin nan wataƙil agaban ido na wataƙil kuma abayan Idona”.

Cikin sauri Mommy ta rintse

76 / 140

Chapters