Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Sakayya Complete Hausa Novel by Aisha Aliyu Garkuwa

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Free Novels Online (Read & Download)

Chapter   83 / 140

246K to 249K   out of 417.8K words

tafasassun hawaye dake kwaranyo mata ba ƙaƙƙautawa.
Kamar a Film haka yanayin da suke rayuwa dashi a makaranta ya fara dawo mata, one by one, har zuwa ranar da suka kasance a mota, haka nan taji wani murmushin da batasan manufarsaba ya kumce mata, wanda kuma ya korowa hawayen da bata san ya kubce mata da kukaba.
Sai kuma ta saki sassayyan kuka jin Mommy ta zauna kusa da ita tana mai cewa.
“Toh kuma kukan me kikeyi Fatima”.
Ta ƙare mgnar da kiran asalin sunanta wanda bata cika kiranta da shiba.
Ita kuwa Khausar cikin ci gaba da sassayan kukan tace.
“Mommy kinaji fa wai sun ɗaura auren”.
Jawota jikinta Mommy da hawaye zubomata tayi tare da ɗaura kanta bisa cinyarta tana mai danne kukanta tace.
“Ba komai Mamana kiyi shiru, ai ba yau za'a tafi da keba ki share hawayenki, addu'arta bazata bari ki muzantaba a gidan aurenki”.
Ta ƙare mgnar tana share mata hawaye, daga nan taci gaba tausarta da kwantar mata da hankali dan ta lura gaba ɗaya ta ɗimauce abin ya daki zuciyarta ya kauda nitsuwarta.

Washegari Da safe Kai tsaye Bedroom din Mommy Lamiɗo ya shiga tare da yi mata bayanin duk yanda sukayi a Jauro yaya bayan sun dawo Sallar La'asar da batun auren da suka dauran.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe cikin sanyi ta ɗago kai tare da kallon Lamiɗo kana tace.
“Toh yanzu har an ɗaura Auren kuma ba jan lokacin asan yaron yana sonta, sannan kuma ace za ayi bikin cikin ƙankanin lokaci haka?”.
Ta ƙare mgnar cije da rauni.
Jinjina kai Abba yayi yana kallon yanayinta yace.
“Toh me za ajira Aysha ai abune na wasiyya kuma akwai damar yi sannan Already Khausar ta gama Secondary kawai tayi Aurenta tunda Alh Bashir yace a Marocco zasu zauna kinga shida kanshi yace zai kaita wurin mijinta”.
Kallonsa kawai Mommy keyi sabida tama rasa abincewa.
Ahankali Abba ya cigaba da cewa.
“Saboda ya lura yaron bayan son zaman nan sannan yana so yabar masa ragamar Company ahannunsa kinga idan sunje can sai ta cigaba da karatunta acan tunda dama yanayin makarantar su akwai cikekkiyar larabci kinga zata iya karatu a can, ta kuma yi zaman aurenta cikin aminci”.
Sunkuyar da kai Mommy tayi tana wasa da yatsun hannunta yayinda tausayin yarta yasa hawaye cika mata idanu A hankali tace.
“Kuma ba wanda ta sani a canfa, ya zatayi”.
Abba ya cigaba da cewa.
“Kada ki damu, ɗan naji Abban Jameel yace in Malam Ahmad ya yarda da rakiyar Ummin Jameel da Asma'u zasuje, ga kuma Hajia Bunayyah itama zan biya mata su kaita tare”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace.
“Hmmm abin ne naga kamar anyi sa da gaggawa Khausar fa yarinya ce, wlh tsoron yaronan ne fal zuciyarta jiya kwana tayi batayi bacciba”.
Murmushi Lamiɗo yayi tare da riƙe tafin hannunta acikin nasa yace.
“A ba wani yarinta aciki ai Insha Allah komai zai tafi dai-dai zakiyi alfari da Aurenta da Moddibo ke lokacin da aka aurar dake ai bakima kaita shekaruba, mijinta kuma bar tunanin tana tsoronshi a a bata sonshi ke dai ku zuba ido zakusha mamakin yadda al'amarin zai kance in dai Khausar ta ɗauke ki ai kiyi shiru kawai yaro zayi mubaya'a”.
Ya ƙare mgnar da cikin sigar wasa da son kwantar mata da hankali.
Kai ta gyaɗa kana cikin sanyi tace.
“Allah yasa”.
Amin yace tare da miƙewa ya fita.

Acan ɓangaren Ummi kuwa bayan Sallar Azahar bayan Malam Ahmad ya dawo daga gidan Abba ya zayyanewa Ummi duk yanda Abba ya faɗa masa.
Ajiyar zuciya mai nauyi Ummi ta sauƙe tare da fesar da numfashi cikin tsananin jin daɗin kana tace.
“Alhamdulillah yau dai burin Jameeluna ya cika sannan wasiyyar daya bari ta kasance kai baki daɗin wannan al'amarin”.
Jinjina kai Malam Ahmad yayi cike da farin ciki yace.
“insha Allah”.
Numfashi Ummi ta fesar kana tace.
“Toh Allah ya tabbatar mana da alkhairi ya kaimu lokacin tafiyar, shiru zanyi bazan gayawa Asma'u ba tukun sai naga yadda Khausar ɗin ta nufeta da mgnar”.
Ameen ya amsa kana ya fice.

Ahankali Asma'u ta fito daga Bedroom tare da kallon Ummi kana tace.
“Ummi wai maganar me naji kuna yi kamar batun Aure?”.
Kai Ummi ta jinjina da alamun farin ciki afuskarta tace.
“Hmmm”. Sai kuma tayi shiru, ita kuwa Asma'u cikin son tabbatar da abinda kunnuwanta suka jiyemata cike da kaɗuwa tace.
“Dan Allah Ummi ki gaya min na tuba”.
Cikin tsanananin jin dadin ɗaya kasa biya a saman fuskarta tace.
“Eh maganar Auren Moddibo mukeyi”.
Zare ido Asma'u tayi kana tace.
“Ummi Yaya Moddibo zaiyi Aurene?”.
Jinjina kai Ummi tayi tana kallonta tace.
“Eh yanayi Aure dai”.
Murmushi Asma'u tayi cike da farin ciki tace.
“Ummi Wacece matar?”.
Ummi na murmushi tace.
“Aminiyar kice matar”.
Asma'u kuwa cike da matsanancin mamaki da al'ajabi ta zare Idanunta waje kana tace.
“Khausar!?”.
Kai Ummi ta jinjina tare da faɗin.
“Tabbas kuwa da izinin Ubangiji Itace”.
Tafa hannu tayi tare da buga still da Mamaki da kuma al'ajabi tace.
_“Lahailah ha Illallahu Muhammad Rasulullahi (S.A.W)”_ Yah Moddibo da Khausar.
Kallon yanda ta zare ido da sallami Ummi tayi kana tace.
“Haƙƙun kuwa dan tuni an ɗaurama”.
Dafe kunci Asma'u tayi da matsanancin mamaki gani da kaɗuwa ɗoki da bai sake taba tace.
“Dan Allah Ummi yaushe aka fara wannan maganar?”.
Hannunta Ummi ta riƙe tare da zaunar da ita agefenta yace.
“Ki nutsu mana Asma'u me wannan kamar wanda akace an haɗa Auren mutum da Dodo!?”.

Sake baki Asma'u tayi cikin Mamaki tace.
“Tabb Ummi ai kusan Auren Dodo da mutum za ayi dan wallahi Khausar matsayin Dodo take kallon Yah Moddibo”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauke kana tace.
“Aikuwa da saninta”.
Zare ido Asma'u tayi tamkar zasu zubo tace.
“Ummi Khausar ɗin ta sani?”.
Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.
“Eh”.
Dafe ƙirji Asma'u tayi Idanunta akan Ummi tace.
“Shine kuma bata faɗa min ba iyeee Kam bala'i bari Inje in sameta”.
Ta Ida maganar tare da miƙewa.

Cikin sauri Ummi ta riko tsintsiyar hannunta tace.
“Zauna ai zuwa ta ƙarshe naji tana cewa tazo kuyi wata magana kuma ta samu kuna aiki sannan fitowar ku kenan taga Moddibo yazo kinga ai jikinta na rawa ta fita”.
Jinjina kai Asma'u tayi still Hannunta na cikin na Ummi tace.
“Eh dan na kirata awaya ma nace ta faɗa min shine tace idan inaso Inje gidansu inji labari ashe dama wannan ne maganar amma Ummi tasan maganar kuma ta yarda?”.
Cikin sanyi Ummi tace.
“Eh ta sani ta yarda kuma ta amince”.
Dafe kunci Asma'u tayi kana tace.
“To amma Ummi garin ya akayi haka?”.
Kallonta Ummi tayi tare da gyara zamanta kana ta sauƙe numfashi cikin sanyi tace.
“Wasiyyar Yayanki zata cika?”.
Cikin sauri Asma'u ta kalleta fuskarta ɗauke da mamaki tace.
“Wasiyya kuma Ummi ya bar mata?”.
Jinjina kai Ummi tayi tare da fesar da numfashi kana ta jingina bayanta da jikin kushin ɗin tace.
“Idan baki manta ba Ranan da yazo gidan nan na ƙarshe itama Khausar tazo sannan tare suka tafi”.
Cikin sauri Asma'u ta jinjina kanta kana tace.
“Ƙwarai kuwa Mommy na tuna aishine tace suna tafiya taga wata mota na binsu”.
Kai Mommy ta Jinjina kana tace.
“To awannan ranan ne ya bar mata wasiyar. Mommy ta ke sanar min yanda suka yi”.
Jinjina kai Asma'u tayi cike da tausayawa Aminiyar tasan yanda Khausar ke masifar tsoron Moddibo tabbas ta ɗauki al'ƙawari mai girma cikin sanyin murya tace.
“Allah sarki Khausar!, Allah sarki Aminiya!!, Ubangiji Allah yabar ƙauna Allah yabar ƙauna tsakaninta da Yah Moddibo”.
Sai kuma ta kalli Ummi da fuskarta ke ɗauke da murmushi tace.
“Ummi inshirya inje”.
Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.
“Kije mana Asma'u wa zai hana ki zuwa wajen Aminiyarki”.
Cikin sauri Asma'u ta miƙe tashiga Bedroom ta sanya hijabinta kana ta fito tayiwa Ummi Sallama.

Aɓangaren Hajiya Lami kuwa miƙewa tayi daga Bedroom ɗinta ta nufi ɗakin Samira zaune ta sameta Idanunta sun kaɗa sunyi jawur tamkar garwashi alamar tasha kuka sosai cikin sauri ta ƙarasa kana ta zauna gefenta cike da kulawa tace.
“Samira wai lafiya yau baki fito ba meya faru?”.
Ahankali ta ɗago kanta Idanunta da suka sauya launi ta kalleta Muryanta na rawa tace.
“Mommy ni baƙi ɗaya wari nake ji idan na tambaye ki kinajin wani sai kice min bakya ji Mommy kullum warin nan ƙaruwa yake ya zanyi da raina”.
Cike da tausayawa Hajiya Lami ta janyota jikinta cikin sanyin murya tace.
“Haba Samira ki kwantar da hankalin ki mana idan ya dawo sai mu sake komawa wajensa”.
Cikin raunin murya tace.
“Mommy wani irin in ya dawo zaku koma wajensa ni dai ina ganin mutumin nan ya lalata min rayuwa ne yanzu ayanda nake warin nan ko maigadin gidansu Modibbo ma zai yarda ya aurenki ne bare Modibbo da ɗan karen tsabta”.
Sai kuma sharce hawaye masu masifar zafi kana tace.
“Yanzu Mommy wani namiji ne zai kalleni bare yace yana sona! ga ruwa mai wari da ƙarni yana ta bina ko yaushe ina tare da ƙunzugu kamar mai jego”
Cikin sanyi Hajiya Lami tace.
“Bakomai Samira kasa ki damu Insha Allah yana dawowa zamu koma wajensa”.
Cikin muryan kuka da tashin hankali tace.
“Mommy Ni dai ina ji ajikina wannan al'amari ya zama min bala'i arayuwata na saɓi Ubangiji gashi ya kamani tun ba aje ko ina ba Wayyo Allah! Kaico na! Ni Samira”.

Asanyaye Hajiya Lami tace.
“Haba Samira kar ki karyar min da zuciyata mana Insha Allah burinki zai ciki”.
Kai ta girgiza kana tace.
“Mommy ni kam hankalina bai kwanta ba burina inga na samu lafiya wannan ruwan ya daina zuba shine kwanciyar hankalina”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da dafa shoulder ta tace.
“Kada ki damu Insha Allah Samira Zaki samu sauƙi”.
Jinjina kai tayi kana tace.
“Allah yasa Mommy Ina fatan hakan Allah na tuba Allah kayafemin Allah kaji ƙaina ka gafarta min”.

Acan ɓangaren Lamiɗo kuwa bayan ya fita ɗakin Mommy Kai tsaye sashen Gimbiya Dadu yashiga bakinsa ɗauke da sallama zaune ya ganta da ƙanwarta Hajiya Kubra.
Anutse ya ƙarasa tare da zama kana da murmushi afuskarsa yace.
“A Yafendo Kubra kin zo ne?”.
Kai ta gyaɗa tace.
“Eh Lamiɗo kana gida kenan?”.
Kai jinjina kana suka gaisa bayan sun gaisa Hajiya Kubra ta gyara zamanta tare da kallon sa tace.
“Toh yau dai kam nazo da aiken Ƙaninka duk da yace min iyayenshi maza sunzo”.
“Wanne ƙarin nawa”. Yayi tambayar a bauɗo domin babu wanda ya taɓa mishi mgnar.
Shi kanshi mahaifin Naseru cewa yayi yaji suna mgnar ne bakwai sun gaya mishi bane, to kuma shima sai abin ya kwanta mishi musamman da yasan Nasiru na biye-biyen mata shiyasa ya nemi alfarma a bashi Amina kuma ayi auren cikin gaggawa.

Murmushi tayi tare da Kallonsa tace.
“Naseeru mana”.

Kai ya jinjina kana yace.
“Ikon Allah Naseeru kuma ko ɗazun ma muna tare kuma bai faɗa min ba shine sai ya aiko ki? ai da kin kirani ma zanzo har gida in sameki”.

Kai ta girgiza kana ta kalli Gimbiya Dadu sai kuma ta kalli Lamiɗo tace.
“A'a ai aiken ne dole muzo da kan mu tunda iri muke nema”.
Jim yayi kana yace.
“Ikon Allah wani kalar iri kenan?”.
Ƴar dariya tayi ta gyara zamanta kana tace.
“Iyeee al'amarin ne ya sauya sheƙa”.

Gyara zama Gimbiya Dadu tayi kana tace.
“Eh aihakama shi yafi alkhairi Hausawa sunce naka sai naka daɗin zama sai bare gwara dai kome za ayi ace na kane” .
Ido kawai Lamiɗo ya zuba musu cikin rashin fahimta ko kaɗan bai taɓa fuskantar alaƙar dake tsakanin Amina da Naseer.
Ganin yanda yake kallon Hajiya Kubra tayi murmushi tayi kana tace.
“Akan al'amarin Naseeru ne da Amina”.
Cikin sauri ya kalleta ya girgiza kai kana yace.
“Ba dai Amina da Naseeru ba saidai Nasseru da Khausar dai ko?”.
Dariya tayi tare da gyara dankwalinta tace.
“A'a da Aminar dai”.
Ido ya zuba mata cike da son nazartansu yace.
“Da Amina dai?”.
Jinjina kai tayi ta kalli Gimbiya Dadu kana tace.
“Tabbas da Amina”.
Jingina Lamiɗo yayi da jikin kujeran kana yace.
“A'a baki fahimci maganarsa da kyau ba da Khausar ce kuma al'amarin ma dai gashi nan yanda yazo abirkice”.
Fuska Gimbiya Dadu ta ɓata kana tace.
“Babu abinda ya birkice sai dai sune ya birkice musu acan tunda Khausar ta nuna bata sonsa ai Alhamdulillah ga ƴar Uwarsa ta soshi”.
Cike da Mamaki Lamiɗo ya ɗago kansa ya kalleta yace.
“Da ita Aminar kenan?”.
Jinjina kai Hajiya Kubura tayi kana tace.
“Eh ai Amina da Nasseru sun daɗe da haɗa kansu soyayya suke sosai basu dai fito sun faɗa maka bane suna so sai angama shirya abubuwa komai ya kankama”.
Jinjina kai Lamiɗo yayi still da mamaki atare dashi yace.
“Allah mai iko shi kuma Naseeru ƴarsa zai Aura?”.
Cikin sauri Gimbiya Dadu ta katsesa da cewa.
“Ya haramta ne?”.
Murmushi yayi tare da girgiza kai yace.
“A'a a'a bai haramta ba na isa in haramta abinda Allah ya halatta ba wai ya haramta bane amma da yake tana sunan ƴarshi ce”.
Baki Gimbiya Dadu ta taɓe kana tace.
“To wannan dai ba wani abu bane aciki ka dai kayi fatan alkhairi Allah yasanya albarka acikin al'amarin”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.
“Kuma haka abin ya zama kenan?”.
Kallonsa Gimbiya Dadu tayi kana ta kalli Hajiya Kubura dake murmushi tace.
“Sosai ma tunda naji Kakar Khausar tana cewa ba zata bawa Zuri'ar Mayu ba tana ƙananun surutai shiyasa nace ya janye da nemanta ya nemi Amina ƴar Uwarsa shiyafi mana kwanciyar hankali”.
Ahankali Lamiɗo ya sunkuyar da kansa ƙasa batare da yace Uffan ba.
Dariya Hajiya Kubrua tayi kana tace.
“Ai shiyasa nace bari nazo da kaina muyi magana”.
Anutse ya ɗago kansa ya kalleta ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.
“Toh Yafendo Kubura ai wannan al'amarin Aure magana ce ta maza bata mata ba ai da Babban Naseeru ne zaizo muyi magana zai fiko sai insamu gamsuwa da sahalewar sa za ayi dukkan maganar?”.
Cikin sauri Gimbiya Dadu ta katsesa da cewa.
“Ai zaizo amma dai ta fara zuwane ta sanar maka saboda bakasan da Maganar ba”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.
“Toh shikenan Ubangiji Allah ya mana zaɓin alkhairi”.
Gimbiya Dadu kuwa cikin sauri ta tari numfashi ta hanyar cewa.
“Shine ma alkhairi Nasseru ya auri ƴar uwarsa ita kuma taje can ta ƙarara ta auri duk wanda taga dama da masifaffiyar Kakarta”.
Murmushi yayi kana yace.
“To Allah ya kyauta”.

Miƙewa yayi ya fita kai tsaye sashen sa ya nufa zaune ya samu Hajiya Bunayya da waya maƙale akunnenta tana magana da Hajiya Lami ganinsa yasa tayi saurin cire wayar kana ta katse ta juya ta kallesa zama yayi tare da tsira mata ido tamkar shine rana ta farko da yafa ganinta acikin rayuwarsa.
Ganin kallon da yake bin ta dashi ne tace.
“Ya dai Mai martaba naga kana ta kallona lafiya kuwa?”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe kana cikin tsira mata Ido yace.
“Wai me yake faru tsakanin Naseeru da Amina ne?”.
Cike da farin ciki tace.
“Meye kuma yake faruwa Lamiɗo banda lamarin Aure da muke fatan zai tabbata tunda sun daidaita kansu”.
Wani irin kallo ya watsa mata kana yace.
“Sun dai-dai-ta kansu Meyesa ban sani ba”.
Zare ido tayi tare da ɗage hannunta sama tace.
“Lalala nima Wallahi ban saniba sai kwanan nan bai kai sati ba Amina take cemin wai zai aiko ya gama haɗa kayan Aure su goro da kayan gishiri da kuma sadaki”.
Ido kawai Lamiɗo ya tsira mata bako ƙyaftawa ta cigaba da cewa.
“Hatta kayan rufi ya gama haɗa komansa yana so ayi auren nan da mako biyu nanne nasan da maganar toh tsoron yi maka magana nake ta yanda zan tunkare ka da maganar”.
Cikin wani irin yanayi Lamiɗo ya tsira mata ido tamkar mai son fahimtar wani abu.
Marerece fuska tayi kana tace.
“Ya dai ka zuba min ido Lamiɗo ka yarda dani ai danasan da maganar dana faɗa maka nima abin ya daure min kai shiyasa ban faɗa maka ba”.
Sai kuma ta sunkuyar da kanta ƙasa kana ta cigaba da cewa.
“Domin nasan da farko Khausar Naseeru yake so to amma shi Naseeru da kansa ya sameni yace Khausar tace bata sonsa to shi ya hakura sannan Gimbiya Dadu ma tace ya nemi Amina ƴar Uwarfashi Lamiɗo ya fesar kana yace.
“Allah ya kyauta amma batun kice baki sani ba zancene Bunayya magana kike”.
Cikin sauri ta kallesa kana tace.
“Wallahi tallahi Lamiɗo ban saniba”.
Cikin yanayin ɓacin rai da takaici yace.
“Dakata Bunayya kada ki rantse dan na lura kamar baki san girma da darajar rantsuwa ba idan kika ce baki sani ba magana ya ƙare”.
Cikin tsinkewar zuciya take kallonsa.Cike da ɓacin rai ya cigaba da cewa.
“Idan kika faɗa kona yarda ko kar nayarda wannan tsakanina ne dake akan abinda kinsan ƙaryane kinsani sannan nasani kuma inada tabbaci da yaƙinin ke kika ƙulla wannan alamarin”.
Cikin yanayin tashin hankali da damuwa tace.
“Fisabilillah taya zan ƙullah”.
Ƙwaffa yayi kana yace.
“Bunayya gani kike kamar bansan komai akanki ba ko?”.
Atake zuciyarta ya tsinke zufa ya fara wanke mata fuska duk da sanyin irin na garin Gembila cikin sauri tace.
“Toh yanzu dan Allah ni menayi?”.

Kai ya girgiza still Idanunsa na kanta yace.
“Hmmm jiki magayi tunda haka kika zaɓawa kanki, duk abinda ya kasance ku kuka da kanku acikin al'amarin nan ya kamata ace komai zakiyi kiyi shawara dani”.
Kasa cewa komai Hajiya Bunayya tayi sai zufa dake wanketa cike da takaici ya cigaba da cewa.
“Amatsayina na mijinki kuma Uba ga Amina amma bakuyi shawara dani ba sai kuka tura Iyayena ta yanda zasu tsareni acikin maganar tunda haka kuka zaɓa magana ta ƙare, kowa ya ɗeɓo da zafi bakinsa!!!”.
Cikin ɓoye tsoronta tace.
“Naseeru fa shiyace ya daina son Khausar”.
Cikin sauri ya katseta ta hanyar cewa.
“Khausar ko baice ya dena sontaba Ni kaina inada nufin bazan bashi Auren Khausar ba, tunda kuma yazo ya zagaya kukayi haka ke kika sani ƴa ƴarki ce shi kuma ɗan uwana ne babu abinda zance”.
Marerece murya tayi kana tace.
“Ni dai wallahi babu abinda na sani aciki kuma itama Amina tace in faɗa maka Babansa yace zai zo gobe”.
Wani kallo ya watsa mata Afusace yace.
“Idan kinga dama kice masa yanzu yazo aɗaure ba haka kike so ba?”.
Asanyaye ta kallesa kana tace.
“Toh fisabilillah dan Amina za tayi Aure shine zai zama laifi ko kuma so kake itama tayi ta zama kamar yanda Asiya take zaune?”.

Cikin tsawa ya ɗaga mata hannu kana yace.
“Ki kiyayi kanki kada ki yarda kijefi Asiya da mugun furuci, Insha Allah Asiya Ubangiji zai jiɓanci lamuranta Asiya zatayi Aure aure mai daraja da izinin Ubangiji baza ta taɓe ba”.
Kallon yanda yayi kicin-kicin da fuska Hajiya Bunayya tayi cikin fushi ya cigaba da cewa.
“Da yardan Allah tunda tayi haƙuri da jarabawar da Ubangiji ya mata za taci nasara baya ga haka duka-duka nawa Asiya take bare Amina dududu ba shekaran daya gabata bane ta gana Secondary ba?”.
Uffan batace ta lura aharzuƙe yake cikin rashin walwala ya miƙe yashiga Bedroom ɗinsa.

*MOROCOW*

Aɓangaren Moddibo Baki daya kansa ya ɗauki zafi aiki suke gadan-gadan Anutse ya fito daga masallacin dake cikin Company ya nufi ainihin inda ake buga Abaya, kama daga Dubai Abaya, Morocco Abaya, Saudia Abaya, da kuma Turkiya Sai kuma Veils,Bags,shoes da sauransu.
Babba wajene sosai ankafa manyan ijinina

83 / 140

Chapters