Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Sakayya Complete Hausa Novel by Aisha Aliyu Garkuwa

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Free Novels Online (Read & Download)

Chapter   78 / 140

231K to 234K   out of 417.8K words

buri sama da wannan Mommy yace min da ɗan Adam yana da zabi idan ajalinsa yazo to da zai roƙa ajinkirta masa ajalinsa yaga kasancewa ta da Moddibo a Inuwa ɗaya a gidan aure”.
Sai kuma tayi saurin dafe ƙirjinta jin yanda numfashinta ke fusga.
Ta sauƙe wani irin numfashi tare da dafe kanta kana ta cigaba da cewa.
“Yace min Khausy zanso naga wani irin zama zakuyi keda Moddibon.
Yace min zaiso ace Allah ya bashi Aron Rai ya rayu ya ganni gida ɗaya a Inuwa ɗaya da Moddibo yaga wani irin Rayuwar aure zamuyi koda na wuni ɗaya ne.
Allah sarki ya Jameel ashe bazai ganiba.
Dan Allah Mommy ki barni in cikawa Yah Jameel burinsa Mommy Dan Allah kiyi haƙuri ki barni in cikawa Yah Jameel Wasiyyar sa”.
Taƙarashe mgnar tare da fashewa da matsanancin kuka mai masifar ƙuna da ɗaci sai kuma tace.
“Mommy wallahi ina tsorin son Moddibo har Raina, kawai na faɗa ne domin kada Hajja Nana tace dole sai na Auri Yah Aliyu shiyasa na faɗa alokacin, amma bawai dan in kunya taki bane Mommy kinfi kowa sanin halina banyi hakan da wata manufa ba face cika wasiyyar Yah Jameel”.
Numfashi mai tsawo taja cikin Muryanta da baya fita tace.
“Mommy ina matuƙar girmama Yah Jameel Mommy Ina so in cika Masa burinsa wannan shine wasiyyar Yah Jameel na karshe kuma shine karshen maganarmu dan Allah ki tayani cika masa wasiyyar sa na roƙeki”.
Wasu irin hawaye masu zafi ne suka fara bin kuncin Mommy cikin sanyi da raunin murya tace.
“Insha Allahu Khausar da izinin Ubangiji za acikawa Jameel burinsa...!



*LITTAFIN SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama ba haƙƙin kowa a kanki 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. In dai baki biyaba kika karanta to na satane, kuma na Allah ya isane*



By
*GARKUWAR MARUBUTA*SAKAYAH

37

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇



Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.
Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.
Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya Zaki kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.
KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.
INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA'AURATA.



Khausar kuwa cikin sanyi da rauni tunowa da M Jameel da ya dawo mata sabo ahankali ta kife kanta abakin gado tafashe da kuka mai cike da fargaba da kuma tsoron Allah.
Kallonta Mommy tayi cike da tausayawa tace.
“Kiyi haƙuri ki daina kuka Khausar addu'a zaki yiwa Jameelu sannan Insha Allah za acika masa burinsa da wasiyyar daya bari in Allah ya ya nufa”.
Ta ƙare mgnar tare da sauƙe numfashi.
Idanta ta tsaida kan Khausar da har zuwa lokacin kanta ke kife jikin gado cikin tausasawa tace.
“Amma kisa Aranki cewa haƙuri zakiyi da duk rayuwar da zakije ki tarar, sannan wasiyya zaki cikawa Jameel, sannan ki sani shi zaman Aure kansa Ibada ne, koda ana son juna wata ran akanji babu daɗi, bare ke da dama kin san matsayinki a wurin wanda kike ganin kina da ƙarfin guiwar zama dashi,
dan haka kisa Aranki cewa ba lallai ne kiji daɗin zama da Moddibo ba, amma tunda kince kinji kin gani zakiyi abinda Jameel ya buƙata kafin barinsa duniya zan biki da addu'a Ubangij ya tabbatar da al'khairi tunda har iyayensa duk ya gayawa kuma tuni suma sun sa baki a mgnar, kinga ni bani data cewa tunda kun mamayeni”.
Cikin rauni Khausar ta sake fashewa da sabon kuka tabbas gaskiya Mommy ta faɗa ba Lallai tayi zaman daɗi da Moddibo ba tunda baya sonta hasalima koda kallonta ne baya sonyi tuno da hakan yasa wasu hawaye masu masifar zafi suka zubo mata tama sani tabbas cikin uƙuba zata rayu dashi, to amman ya zatayi rayuwa Yah Jameel al'ƙawarin amincewa da batun auren Amininsa.

Cikin sanyin murya Mommy ta cigaba da cewa.
“Sanin bake kaɗai Jameelu ya barwa wasiyya ba yasanarwa da Kakar Moddibo sannan ya sanarwa Umminsa da kuma Abbansa nima da farko hankalina ya tashi.
Amma yanzu barina ɗakin Abbanku yake cemin shekaran jiya da daddare Abban Jameel da Malam Ahmad da malam Arɗo sunzo da batun, abinda yasa baiyi mgnar ba Hajja Nana bata bashi dama bane daya mata bayani”.
Wani irin rauni, Kunya,damuwa da rasuwar Jameel ne suka dawowa Khausar alokaci ɗaya.
Cikin sanyi jiki ta miƙe ta nufi ɗakinta tana shiga ta faɗa kan gadonta kana ta cigaba da kuka cikin rauni tasan dai iyaye keyiwa ƴaƴansu auren dole a tarihin duniya, sai gashi ita dai itace zatayiwa kanta da kanta auren dole bisa wasiyar Yan Jameel malami na musamman mai matsayin babban Yaya wanda ita dai da fari har ranta shi takeyiwa kallon mai iya jiɓantan lamuranta.

Washe gari da safe Misalin ƙarfe 8:00 Anutse Moddibo ya fito daga falonsa cikin wani ɗanyen Boyel Sky blue Fuskarsa tayi fayau manyan Idanunsa dake lumshe sun sake girma sabida ramar da yayi, sajensa ya sake yawaita yayi fadi da cika, yana kuma ɗan hargitse alamun an kwana biyu ba'a gyarashi.
Kafadarsa na dama rataye da jakar laptop ɗinsa daga zip ɗin gefen wayoyinsa ya zira, sai hannunsa dake riƙe da jakar kayansa, a hankali yake tafiya, yayinda jikinsa ke fitar da sanyayyan ƙamshin tularen sa.
Kai tsaye sashen Innayi ya nufa ahankali Innayi dake breakfast ta ɗago Kai ta kallesa Anutse ya ƙarasa tare da zama gefenta.
Da mamaki take Kallonsa ganin kamar alamar cikin shirin tafiya yake.
Cikin sauri tace.
“Aliyu”.
Kallonta yayi da sauri domin bata fiye kiransa da Aliyu ba sai da babban dalili.
Cikin sanyin murya yace.
“Na'am Innayi”.
Hannunta riƙe da kofin tea tace.
“Ya haka? ya na ganka kamar mai yin tafiya?”.
Kai ya gyaɗa mata tare da tanƙwashe ƙafafunsa kana ya fuskanceta cikin ƙoƙarin danne damuwarsa kana yana mai jin farin cikin zai bar garin Gembila haka nan ya tsinci kansa da jin farin cikin yau dai zai bar Jahar Taraba domin baki ɗaya garin ya fice masa arai cikin sanyin murya yace.
“Innayi ba kama bace tafiyar ce”.
Cike da mamaki ta ɗago kanta kana tace.
“Aliyu tafiya zaka yi amma ban sani ba sai dai in ganka kana fita da jaka haka?”.
Ahankali ya riƙo tafin hannunta acikin nasa cike da mmkia yace.
“Kiyi haƙuri Innayi tafiyar ce nima tazo min a bazata kuma ba jiya Abban Jameel ya gaya mikiba”.

Kai ta girgirza tare da cewa.
“A'a bai gaya minba zakayi tafiya ba, ya dai cemin yana neman al'farma ni kuwa nace umurni kawai zai baka kamar yadda yake bawa Jameel ni na amince duniya da ƙiyama, ban bari yamin bayaniba sabida kar yaga kamar zan hanaƙa yaji ba daɗi. To waima Tafiya zuwa ina zakaje?”.
Cikin kwantar da murya yace.
“Tafiya zuwa Marocco!”.
Cikin tsananin kaɗuwa ta zaro idanunta baki ɗaya lokacin ɗaya ta ƙware tare da fara tari sakamakon ƙwarewa da tayi da dankalin dake bakinta”
Moddibo kuwa ganin yanda ta ƙware yasa yayi saurin daukan kofin ruwa ya miƙa mata tare da cewa.
“Sannu”.
Amsa tayi tasha amma still tarin bai tsaya ba lokaci ɗaya Idanunta yayi ja zufa ya shiga tsats-tsafo mata agaba ɗaya ilahirin jikinta shi kuwa Modibbo ido ya zuba mata tare da jera mata sannu da kuma ɗan bubbuga bayanta kaɗan-kaɗan yana mmkin wasu al'amuran a ranta domin ya sani tsawon zamansu da J ta hanashi zuwa Marocco wanda bai san me dalilntaba, kasancewar sa ba mutum ne mai yawan bincikeba yasa bai taɓa mata musuba ko bincike.
Ahankali ya ke mata sannu cike da tausayawa takai kimanin minti biyar kafin tarin ya lafa sannu Ahankali ta fara maida numfashi.

Tana sauƙe ajiyar zuciya ta juya ta kallesa kana tace.
“Marocco!!!! kuma Aliyu?”.
Jinjina kai yayi cikin sanyin murya yace.
“Eh Innayi Marocco zanje amma idan har kin amince, idan bakya so, bazanje ba sai in bawa Abba haƙuri”.
Ahankali ta gyara zama tare da fuskantar sa da kyau kana tace.
“Toh amma mai zakaje kayi a can?”.
Tayi tambayar zuciyarta na mai cigaba da bugawa da ƙarfi.
Lumshe Idanunsa yayi tare da sauƙe Ajiyar zuciya kana yace.
“Abba ne ya nemi al'farma da Inje in kula da Company'nsa sannan kuma jiya daya zo nayi tunanin kunyi cikekkiyar maganar ne dashi kafin ku shiga wurina, shiyasa ni ban faɗa miki ba, ya nemi taimako da Inje in taimaka masa akan batun Company sa buga Abaya, jallabiya, Carpet, Sallayu blanket's da dai sauransu”.
Kallonsa kawai Innayi keyi yayin da take ji tamkar zuciyarta zai fito saboda yanda yake bugawa.
Cikin sanyi Moddibo ya riƙe Hannunta dake cikin nasa yace.
“Akwai sabbin injinan aiki da za'a sauƙe na Company, sannan kuma za'a fara aikin dasa Injina za'a kakkafa toh akwai ɓuƙatar sa ido da kuma kula da abubuwan, amma Insha Allah bazan wuce wata biyu zuwa uku ba zan zo Innayi”.

Girgiza kai tayi tare da jingina bayanta da jikin bango ta lumshe Idanunta kana ta shiga maida numfashi.

Moddibo kuwa ido ya zuba mata kana Asanyaye yace.
“Amma Innayi idan har bakyason Inje zan kira Abba in Faɗa masa yayi haƙuri”.
Uffan bata ceba kana bata buɗe Idanunta ba daga ita sai Ubangiji kaɗai suka san mai take tunawa aranta takai kimanin minti biyar ahaka kafin ta ɗago Idanunta ta kallesa kana taja dogon numfashi ta sauƙe tare da sakin Murmushin mai tarin ma'anoni sannan tace.
“Bazan hanaka tafiya ba Aliyu, domin ko baka tafi yanzu ba, dama lokacin tafiyar ya ƙarato. na amince kayi masa duk kan abinda Jameelu zai masa daya kasance araye, domin hakan zai rage masa raɗaɗin ciwon rashin Jameelu”.
Kai Modibbo ya gyaɗa yana kallon yanayin fuskartar ahankali yace.
“Toh shikenan Insha Allah zanyi hakan”.

Innayi kuwa kallonsa tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Amma yanzu-yanzu tafiyar kenan Aliyu?”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh Innayi zanbi jirgi zuwa Abuja ne, in naga komai biza na ya fito zan wuce”.
Jinjina kai tayi tare da cewa.
“Shikenan Ubangiji Allah ya sanya alkhairi Allah ya tabbatar da alkhairi sai nazo”.
Saurin Kallonta yayi cike da Mamaki yace.
“Sai kinzo kuma?”.
Sunkuyar da kanta ƙasa tayi tare da Girgiza masa kai kana tace.
“Mantawa nayi sai ka dawo nake son cewa".
A hankali ya zaro ATM ɗinshi na Zenith Bank daga al'jihunsa, cikin tafin Hannun ta yasa matashi kana a hankali yace.
“Ga ATM ɗina na Zenith Bank, kin san pin number ɗin, akwai kuɗi a ciki kusan 5 Million”.
Da sauri tace.
“Ina ka samosu?”.
Gyara zamanshi yayi kana yayi mata bayanin yadda sukayi da Abba sannan ya ɗaura da cewa.
“Akwai wasu a wurina, wannan ki riƙe kiyi dukkan abinda kike buƙata kafin in dawo, in haɗasu muyi ƙoƙarin barin garin nan, domin ya fita raina”.
Yayi mgnar yana tuno kalaman Hajja Nana ita kuwa Innayi cike da sanyi tace.
“Uhmmm Aliyu in Sha Allah kamar ma mun barima ai kama barin kai kam”.
Cikin sanyi ya jinjina
Kai tare da miƙewa yace.
“Toh shikenan Innayi amma dai bakiyi fushi dani bako?”.
Da sauri tace.
“La la la Aliyu banyi fushi da kaiba”.
hannunta ya riƙo tare da ɗaurawa a kanshi kana yace.
“Toh kuma baki samin Albarka ba”.
Cikin sanyin Murya tace.
“Allah yasan ya Albarka Ubangiji ya tsare gabanka da bayanka Allah maidakai lafiya ya kuma tsareka da lafiyarka, Ubangiji ya rabaka da sharrin duk kan abin ƙi walau mutum ko aljan ko wani irin abune ya *Tsareka da Tsoffin magauta ya hanasu ganeka bare cutar da kai kafin isarka tushenka”.*
Lumshe Idanunsa yayi kana yace.
“Ameen ya Allah Innayi ni zan tafi”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh ka tsaya bari na zo".
Kai ya gyaɗa sannan ya tsaya ɗaki tashiga ba daɗewa ta fito sanye da hijabi, suka nufi wurin motarsa,
“Yau innayi zafa ki koma gidan Abba ko Ummi dan zamani ke ɗaya a nan bai minba”.
Cikin sauri tace.
“Eh toh gsky k nima ina tsoro Ni kaɗai a nan to amman, gsky gwara min gidan Ummin Jameel kaga ita kamar ɗiya take a gareni gidan Abba kuwa ba wani sabawa nayi da matansa ba, amman can zamu zauna ɗakin Asma'u nasam Malam Ahmad kuma baida matsala”.
Cikin gamsuwa da haka yace.
“Gsky kam hakan yafi, zan gaya Abban in kin gama haɗa kayanki Asma'u zata zo ku tafi”.
Kai ta jinjina cikin gamsuwa tace.
“Ba laifi”.
Jingina yayi da jikin motar bayan yasa jakarsa gefen mai zaman banza.
Ita kuwa Innayi a hankali ta matso kusa da marfin motar zira hannunta tayi ta ciki, zip ɗin jakarsa tabuɗe tasa jim kaɗan kuma ta maida ta rufe kana sukayi sallama ya mota ya tafi.

Kai tsaye gidan Ummi Moddibo ya nufa cikin nutsuwa yake Driving yayin da yake sauraran ƙira'ar Ahmad Sulaiman cikin suratul An'am yana isa gidan Ummi yayi Parking aƙofar kana ya fita ya shiga coumpund ɗin yana tafiya ahankali yana ɗaura ƙafarsa akan farandar sautin muryar Khausar ya ratsa Dodon Kukensa cikin sauri ya tsaya tare da rumtse idanunsa.
Sabida jin yadda tsikar jikinsa ya fara tashi tun daga tafin ƙafarsa har tsakiyar ƙwaƙwalwan kansa, ahankali ya jingina bayan sa da jikin bango yayin da zuciyarsa ta shiga bugawa da kaso Cassa'in da tara cikin ɗari.
Aransa yakeji kamar ya koma domin gaba ɗaya ya rasa meke sashi shiga wani yanayi da zaran yaji sautin Muryanta zaiji tamkar ana tsikara masa allura yama rasa ta wani irin yanayi zai misalta yanda yake ji akan yarinyar shin kunyarta yake ko kuma tsoronta yakeji, ko shakkarta shi kansa ya kasa tantancewa, taune Lip ɗinsa na ƙasa yayi da ƙarfi tare da buɗe idanunsa da suka sauya launi kana ya tura ƙofar falon tare da sallama yana mai tsare fuska.

Ummi dake zaune ta tsira masa ido tare da cewa.
“Babana har ka shirya kenan?
Kai ya gyaɗa tare da faɗin.
“Eh Ummi”.
Kana ya zauna agefenta ya zamana yana facing ɗin kichen.
Kallonsa Ummi tayi cike da kulawa tace.
“Amma dai ba kayi breakfast”.
Kai ya girgiza kana yace.
“Uhm-Uhm”.
Da Mamaki tace.
“Toh ya za'a ayi ka tafi da yunwa ba zaiyu ba Babana ba zaka tafi da yunwa ba”.
Langwaɓar da kai yayi tare da Marerece murya yace.
“Ummi bana jin yunwa fa”.
Fuska ta ɓata kana tace.
“Bafa zaiyu ba Babana baza ka tafi da yunwa ba”.

Khausar na fitowa daga kichen ta girgiza kai tare da kallon Asma'u tace.
“Toh ni zan tafi sai anjima”.
Da mamaki Asma'u ta kalleta kana tace.
“Bangane ba kamar ya sauri kike?
Dama ba nan kika zoba ne?”.
Khausar kuwa kai ta girgiza tare da kallonta kana tace.
“A'a ba nan nazo ba dama gidan Aunty Ruƙayya naje to da naje sai na sameta tare da baƙi shine na kira Mommy nace zan ƙaraso nan mu gaisa.
Mommy kam cewa tayi wai da safiyar nan zanzo”.
Moddibo kuwa tunda yaji sautin Muryanta akusa dashi ya kasa ɗauke idanunsa akanta duk da cewa kallon Kasan ido yake mata.
Cikin sanyi Khausar ta cigaba da cewa.
“Toh shine nace tayi hakuri ba daɗewa zanyi ba shine fa tace inzo amma kada in daɗe saboda mune da aikin rana zan koma in ta yata nazo muyi wata mgna ce, kuma nafasa”.
Da sauri Asma'u tace.
“Dan Allah muyita”.
Kai ta jujjuya tare da cewa.
“Ba damuwa in kin

78 / 140

Chapters