Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Sakayya Complete Hausa Novel by Aisha Aliyu Garkuwa

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Free Novels Online (Read & Download)

Chapter   137 / 140

408K to 411K   out of 417.8K words

gyada kana tace.
“Eh”.
Murmushi ta saki tare da faɗin.
“Momy dawa yake kama?”.
Murmushi Momy tayi tare da juyawa ta kalli Jaririn dake hannun Niyna kana ta juya ta kalleta tare da cewa.
“Da Ramadan yake kama Khausar”.
Wani Amintaccen Murmushi ta saki mai cike da jin daɗi kana tace.
“Alhamdulillah Momy na samu mai kama da Ramadan".
Kai Momy ta jinjina tace.
“Sosai ma”.
Fuskarta ta shafa tare da faɗin.
“Momy Kyakkyawa ne kenan?”.
Ta ƙarashe Maganar da alamar tambaya kana da Murmushi afuskarta.
Kai Momy ta gyada tare da cewa.
“Kyakykyawane Mamana ɗan ki kamar Balarabe”.
Tana Murmushi tace.
“Ai tunda aka ce da Ramadan yake kama nasan kyakkyawane Momy”.
Sai kuma ta Maida idanunta kan Moddibo tace.
“Yah Mu'allim kaji wai ɗan mu da Ramadan yake kama, kyakkyawane ko?”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Kyakykyawa ne yama fiki kyau ai?”.
Baki ta tura gaba tace.
“Ni dai bai fini kyauba”.
Murmushi yayi yace.
“Toh naji bai fiki kyau ba Rigimatu, ki Kwantar da hankalinki”.
Asma'u kam sai dariya suke mata.
Haka ta cigaba da surutu da Sambatu har kusan karfe huɗu zuwa lokacin already alluran ya gama saketa ta dawo hayyacinta.

Kallon Moddibo tayi tare da cewa.
“Yah Mu'allim zan tashi zaune”.
Sumar kansa ya shafa tare da cewa.
“Toh ki taushi ki zauna mana”.
Fuska ta narke tare da cewa.
“Ka tayani”.
Cikin yi mata kallo mai haɗe da zazzafan yanayi yace.
“Toh ki tashi ki zauna mana ai likitoci sun hana in tayaki, ki tashi da kan ki mana”.
Baki ta tura tayi ta ƙorafi misalin 4:15 ta mike ta zauna da kanta kasancewar ta tashi ta zauna da kanta yasa Dr cewa Moddibo ya tallafa mata amaida ta ɗaki ta taka da ƙafanta.
Da ƙafanta ta taka aka canza mata ɗaki wanda akwai step agabansu suna komawa ɗaki Asma'u ta zauna ta gabanta Moddibo kuma nata bayanta.

Kallon Dr Jameel Asma'u tayi tare da cewa.
“Dr”.
Yana gyara abin karfen gadon yace.
“Na'am my Dear”.
Kai ta langwaɓar tare da faɗin.
“In bata abinci?”
Kai ya dafe kana yayi Murmushi tare da cewa.
“Kai ke dai baki ɗaya na lura bama ta ɗan mu kike ba ta Ƙawarki kikeyi”.
Dariya Momy tayi kana tace.
“Da gaskiyar ta wa yake ta ɗan ku”.
Murmushi Moddibo yayi tare da faɗin.
“Momy harda kema bata ɗan mu kike ba wato ta ita kike ”
Cikin sauri Dr Eshaa tace.
“To ai har kaima bata ɗan ka kake ba ta ita kake tunda ka ɗauke sa aɗaki baka sake ɗaukar saba kana riƙe da hannunta yanzu dai lokacin sallar la'asar yayi atafi ayi Sallah.
Zuwa biyar a ɗan asa mata abinci.
Cheaps kaɗan da tea rabin cup”.

To sukace kana su tafi masallaci, su kuwa matan sukayi salla a nan.

Sai ƙarfe biyar dai-dai
Asma'u ta ɗan sa mata cheabis ɗan kaɗan sai tea rabin cup, kamar dai yadda sukace mata.

Bisa jagoranci likitoci ta matsa ta riƙa bata taɓa ci.
Moddibo kuwa kanta ya riƙa shafawa tare da cewa.
“Minha kinga muje muyi alwala muyi sallah na roki Allah ya baki lafiya ya raya mana ɗanmu”.
Lallausan murmushi ta sakar masa kana ta gyaɗa kai shi kuma ya zauna gefe, nan dai ta gama ci, kana ta ɗan gyara manta.

Dai-dai lokacin kuma Abualeey suka iso, bisa jagorancin Ibraahim m suka nufi dakinta dai-dai lokacin da suka shiga a kuma dai-dai lokacin Khausar ta fara wani irin....






By
*GARKUWAR MARUBUTA**SAKAYYA*

*71*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 08069423567 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.


GARKUWAR MA'AURATA




Tana wani sassayan tari, wanda take ta son danneshi, cikin sauri suka ƙara sa cikin ɗakin da sauri Dr Jameel yace.
“Ha'a ya dai?”.
Momy ce ta ɗago kanta tare da cewa.
“Kamar ƙwaruwa tayi”.
Cikin tsoro gami da damuwa Moddibo ya kalli Dr Jameel kana yace.
“Jifa tari take ba matsala ko?”.
Kai Dr Jameel ya girgiza tare da faɗin.
“A'a ba matsala bari nasa akawo mata wani magani tasha tarin zai bari”.
Ya ƙare maganar tare da kiran Line-line dake cikin wayar ya kira Pharmacy ya faɗa musu su kawo maganin jim kaɗan Norse ta kawo maganin karɓa yayi ya bata tasha cikin ikon Allah atake tarin ya bari.
Sai alokacin ta samu nutsuwa numfashi ta fesar kana ta maida kallonta kan Abualeey tare da cewa.
“Abu ina yini”.
Cike da kulawa yace.
“Lafiya lau ya jiki?”.
Ahankali tace.
“Da sauƙi ”.
Kai ya gyaɗa tare da faɗin.
“Masha Allah Allah ya raya abinda aka samu”.
Karɓan Jaririn yayi tare dasa mishi albarka kana ya miƙawa Waziri da Galadima dai-dai lokacin kuma kira ya shigo wayar Khausar Momy anutse ta duba ganin sunan Hajja Nana yasa ta ɗauka muryanta cike da farin ciki tace.
“Hajja Nana Alhamdulillah anyi Theater ancire ɗa namiji”.
Cikin jin daɗi da sauke ajiyar zuciya Hajja Nana tace.
“Alhamdulillah amma tana lafiya ko?”.
”Eh lafiya lau gata nan ma”.
Cewar Momy na miƙa wa Khausar wayar karɓa Khausar tayi suka gaisa cike da farin ciki Hajja Nana tace.
“Ƴar tsele da zaki kasheni azaune”.
Murmushi Khausar tayi cikin rashin jin karfin jikinta tace.
“Yaushe zaki zo?”.
Fuska ɗauke da farin ciki Hajja Nana tace.
“Kwanan nan in sha Allah kafin ayi suna”.
Murmushi Khausar tayi tare da maida kallonta kan Moddibo da idanunsa ke kan Jaririn tace.
“Ayiwa Hajja Nana shiri in Sha Allahu tana kan hanya zata zo”.
Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“In sha Allahu”.
Akuma dai-dai lokacin Dija da Yah Aliyu suka shigo Murmushi Khausar tayi tare da cewa.
“Dija”.
Cike da farin ciki Dija tace.
“Na'am Khausar ai mu bamu sani ba Khausar baku faɗa mana ba”.
Still da Murmushi afuskarta tace.
“Kiyi haƙuri Dija gaba ɗaya abin ne yazo min atsorace”.
Dariya Yah Ali yayi tare da faɗin.
“Raguwa gaba ɗaya kin gigice kin gigita bayin Allah”.
Langwaɓar da kai tayi kana tace.
“Hmmm ba dole inji tsoro ba Yah Ali abinda ance wasu da yawa idan an musu kafin afito dasu ta can suke wucewa”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“A'a ke kam in Sha Allahu kina nan sai kin kawo wasu ƙannensa goma sha ɗaya sun zama Dozen”.
Idanunta ta zaro tare da faɗin.
“Goma sha ɗaya”.
Baki ɗaya ɗakin suka sanya dariya.
Raudat dake zaune gefen Asma'u ta ƙyalkyale da dariya kana tace.
“Addah khausy idan kika haifi Dozen sai ki bani biyun saman na riƙa kulawa dasu kar suyi Miki yawa ai Yah Moddibo zaku bani ko?”.
Ta ƙare maganar tana kallon Moddibo kai Moddibo ya gyaɗa yana Murmushi.
A ranan haka suka yini suna kula da ita.

Bayan sunyi kwana uku aka sallame ta suka koma gida.
Haka Didi da Momy suka cigaba da kula da ita suna bata kulawa na musamman...
Washe gari da safe Misalin ƙarfe 7:30 Asma'u ta zo zaune ta samu Lalla Khadijah, Rahama, na zaune kan lallausan Darduma Yayin da Didi,Momy,Innayi ke zaune gefe ɗaya Hajja Nana kuwa na gefen Khausar da Moddibo dake riƙe da Jaririn yana masa addu'a kana su kuma suna hira.
Ahankali Asma'u ta ɗago fuskarta ɗauke da Murmushi ta miƙa wa Khausar wayarta tare da cewa.
“Kalli wani special abu dana ajiye Miki wanda nake da yaƙinin sai kinyi min kyauta na musamman”.
Ɗan ware idanu Khausar tayi tana kallon Rahama dake cewa.
“Aikuwa dai Addah Asmeey muma dake gefe muna sa ran samun khauta”.
Dariya Khausar ta sanya kana tace.
“Aikam dai zanso gani”.
Ta ƙare maganar tana playing video
Da sauri ta zaro Idanunta waje ganinta kwance kan gado tana surutai.
Moddibo kuwa wani Amintaccen Murmushi ya saki ganin yanda ta zaro Idanunta waje sai kuma tayi saurin ɗaga kanta cike da kunya jin yanda suka ƙyalƙyale da dariya cikin tura baki ta kalli Asma'u tare da cewa.
“Asma'u Ni ko?,Aikuwa kin ci bashi sai na rama”.
Ta ƙare maganar cike da kunya ganin yanda suke maimaita maganar.
Asma'u kuwa Gwalo Asma'u tayi mata tare da cewa.
“Aikuwa sai dai ki rame yarinya dama can abinda ke Ranki kika faɗa”.
Khausar kuwa juyawa tayi jin Hajja Nana na cewa.
“Yoh ai gaskiya Asma'u ta faɗa ke da wannan mijin naki duk ba kunya ne daku idan ke baki cikin hayyacin ki kika faɗa ai shi yana sane bare keɗin ma kina sane”.
Rau-rau da idanu Khausar tayi ta shiga bubbuga ƙafa daga zaune tace.
“Didi kiji fa abinda Hajja Nana ke faɗa wai bani da kunya”.
Murmushi Didi tayi tare da faɗin.
“Rabu da Hajja Nana am Khausar ɗina kina da kunya sosai ai bada sanin ki kikayi ba”.
Momy kam Murmushi kawai takeyi.
Daidai lokacin Jakadiya ta shigo tare da sanarwa Didi tayi baƙi ƴan Barka.
Miƙewa Didi tayi kana tace.
“Toh ganan zuwa”.
Sai kuma ta kalli Momy dake cewa.
“Mu tafi”.
Atare Didi Momy Innayi,Niyna suka fice.
Kallon Rahamah kalla Khadijah tayi kana tace.
“Rahama muje ki tayani haɗa Alawar Madara da gullisuwa tun jiya naso yi kuma ina zirga-zirga”.
Murmushi Rahama tayi tare da miƙewa Lalla Khadijah kuwa har taje ƙofa ta juya ta kalli kana tace.
“Ƙanwata kema zo muje”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tare da miƙewa suka fita.
Falon ya rage daga Khausar, Moddibo sai Hajja Nana da itama ta miƙe ta fita falon.
Cikin shagwaɓa Khausar ta kalli Moddibo tare da narke fuska kana ta tura baki tace.
“Yah Mu'allim”.
Murmushi yayi kana ya kwantar da jaririn ya janyota jikinsa bakinsa ya kai saitin kunnenta yace
“Na'am Minha Viddaaaa ya akayi?”.
Ya ƙarashe yana jan sunan.
Cike da shagwaɓa tace.
“Jifa yanda na saki baki naita faɗan magana gabansu Momy da Didi kuma baka hanani ba”.
Murmushi yayi yana shafa bayanta yace.
“Ya za'a yi in hanaki fallasa min sirrin dake Ranki?,Taya kike tunanin bakina zai iya dakatar da zinaren kalaman da suke fitowa daga bakinki suna ratsa kogon zuciyata?,Kin kuwa san farin ciki da shaukin dana kasance alokacin?”.
Ya fesar da sanyayyan numfashi mai cike da zallan so da shauƙi yace.
“A lokacin ji nake tamkar ina yawo a gajimare ji nake tamkar nafi Mazan duniya Sa'a da samun Nagartacciyan mace irin ki kin nuna min so tun baki san menene so ba shin mai zanyi in biyaki”.
Cikin wani irin yanayi na musamman tace.
“Ka ƙaunaceni ka kuma soni fiye da yanda nake son kaina kada ka haɗa ni da kowa atare da kai idan kayi min haka kaga yimin komai Yah Mu'allim”.
Ahankali ya ɗago kanta tare da ɗaura lips ɗin sa asaman nata yashiga kissing ɗin ta...

Alhamdulillah zuwa yanzu jikinta yayi ƙwari bazama ace Thearter aka mata ba kullum Asma'u da Dija anan suke yini ana I gobe suna Dr Zakariyya, Asiya Hajja Nana, Abban Jameel, Lalla Hafsat suka zo.

Hajja Nana da Innayi ce zaune da Khausar aɗaki yayin da Innayi ta zuba mata abinci ta bata taci Momy kuma na riƙe da jiriri tayi masa wankan Yamma ta saka shi cikin wasu fararen kayan sanyu masu masifar taushi pink and white collar.
Anutse Moddibo ya shigo ya same su Kai tsaye bakin gadon ya wuce gefenta ya zauna.
Kallonsa hajja Nana tayi tare da cewa.
“Wai kai kam baka jin kunya ne?”.
Juyawa yayi ya kalleta kana yace.
“Kin iso da sa ido ko? Idon ki be iya gani bakinki yayi shiru ko?”.
Hararansa tayi tare da faɗin.
“Ba dole ba idan bani nake taka maka birki ba babu mai taka maka birki”.
Kallonta yayi tare da cewa.
“Toh sai kiyi mugani in birkin zai taku”.
Anutse Khausar ta kallesa kana ta kalli Hajja Nana tace.
“Yah Mu'allim rabu da ita”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Aima na rabu da ita?”.
Khausar kuwa nutsuwarta ta tattara kana tace.
“Yah Mu'allim gashi har gobe suna in Allah ya kaimu”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh”.
Ahankali ta langwaɓar da kai tare da cewa.
“Kuma banji ka faɗa min sunan yaron ba”.
Murmushi yayi kana yace.
“Kuma tun a asibiti kafin ayi mishi wanka na masa huɗu ba tun kafin ki farfaɗo”.
Murmushi tayi kana ahankali tace.
“Kuma Yah Mu'allim baka faɗa min ba".
Juyawa yayi ya kalli Asma'u kana ya kalli Asiya dake cewa.
“Ai dai kam bamu san sunan yaro ba gashi har gobe Suna”.
Didi kam ido ta zuba mishi tana kallonsa Momy kuwa sunkuyar da kanta ƙasa tayi tana sawa Jaririn safan hannu tace.
“Toh menene sunan”.
Sunkuyar da kansa ƙasa yayi kana ya motsa laɓɓansa tare da cewa.
“Sunan shi Jameel”.
Cikin tsananin jin daɗi Asma'u ta kallesa tare da cewa.
“Allah sarki Yah Moddibo Ubangiji Allah ya saka da Alkhairi Allah yabar zumunci ayyah Yah Jameel ɗina Allah ya raya shi Allah ya mishi Albarka”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Ameen ya Allah Asma'u, Allah yasa ya biyo halin takwaransa”.
Ya ƙare maganar yana Murmushi.
Innayi ce ta amshi zancen da cewa.
“Naji Ibraahim kuna na kiranshi da *Keyan*”.
Kai Modibbo ya jinjina tare da cewa.
“Eh laƙanin kenan. Amman asalin sunan Jameel, Allah ya raya mana shi yayi nagarta irin ta mai sunanshi”.
Cikin tsananin jin daɗi Asma'u tace.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum ”.
Khausar na Murmushi tace.
“Ameen ya Allah yasa ya biyo halin takwaransa Allah yasa yayi Ilimin takwaransa”.
Cikin jin daɗi Didi tace.
“Ka kyauta Babana Allah Ubangiji ya raya mana Jameelu”.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum ”.
Cikin tuno da Jameel Hajja Nana tace.
“Ameen ya Allah ai Jameelu mutumin kirki ne”.
Asma'u kuwa cikin sauri ta ɗauki waya tare da kiran Ummi Ummi na ɗauka tace.
“Ummi albishir”.
Daga ɗaya ɓangaren Ummu tace.
“Goro”.
Cike da farin ciki Asma'u tace.
“Yah Jameel ya samu takwara”.
Murmushi Ummi tayi tare da faɗin.
“Hmmm Asma'u kenan kece baki sani ba amma ainin tun ranan Aliyu ya faɗa min”
Murmushi Asma'u tayi kana tace.
“Ummi shine baki faɗa min ba ranan muna hira ina cewa Ala'andi wani suna za'a sawa yaron kikayi shiru ashe duk kin sani”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Na sani mana tun ranan ya faɗa min”.
Murmushi Moddibo yayi tare da cewa.
“Ai TOH na rigaki yin albishir ɗin”.
Dariya ta sanya tace.
“Wallahi Yah Moddibo Ina sauri in rigaka ashe ka rigani”.
Haka sukayi yinin ranan anata shirye-shiryen suna, nan washe gari suna akayi raɗin suna da hidindimu kamar yanda al'adan masarauta take.

Bayan sallar la'asar manyan Fada ne a zaune saboda Aranar Abualeey yake son yin Murabus ya barwa Moddibo sarauta.
Bayan an zauna an cika a Fada anyi komai an taru Sarkin Al'adun Fada ne ya juya ya kalli Moddibo dake cikin wani irin shiga na alfarma da kawa da yayi masifar fitar da ainihin kyawunsa da ƙwarjinsa kana yace.
“Alhamdulillah kamar yanda al'adun Fada take sarki yana da dama da iko da zai yi Murabus tun yana da rayuwarsa ya danƙa Mulki a hannun ɗan sa da yake ganin zai iya gadon mulkinsa kana zai iya kula da Masarauta yanda ya kamata dan haka Sarki Youseef Mohammed Aliyu Mouley ma yayi alƙawari zai maida Sarauta ahannun ɗan sa Aleeyu Youseef Mohammed Aliyu Mouley”.
Cikin jin daɗi Manyan cikin Fada da Manyan Masarautu na gefe-gefe wanda baki ɗaya sun san da Maganar an samu sa hannunsu tun watanni hudu da suka wuce kowa cikin jin daɗi da farin ciki yake faɗin Alhamdulillah.

Cike da girmamawa Sarkin Fada ya juya ya kalli Moddibo tare da cigaba da cewa.
“Kuma a wannan ranane za'a ƙara wa Sarki Aleeyu Youseef Mohammed Aliyu Mouley mata kamar yanda atsarin Masarauta sarki bai kasancewa da mace ɗaya sai an masa biyu aranan da za'a danƙa mulki a hannunsa”.
Cikin sauri Moddibo ya ɗaga kansa ya kallesu sai kuma ya saki wani Murmushi dashi kaɗai yasan ma'anar sa juyawa yayi ya kalli Abualeey dake cikin matsanancin farin ciki kana ya kalli Sarkin Fada tare da cewa.
“Ina son magana da mahaifina”.
Kai Sarkin Fada ya gyaɗa kana yace.
“Toh shikenan ba damuwa”.
Kana suka shiga ɗakin Sirri Shida Abualeey, Waziri, Galadima Wambai Garkuwa...

A dai-dai lokacin kuma acikin gida Khausar ce cikin shiga ta alfarma sanye take cikin wani lafiyayyan Abaya Pinch colour mai masifar taushi da santsi da yasha duwatsu kana ta ɗaura Alkyabba ta Masarauta fari ƙall mai masifar taushi wanda al'ada ce ta Masarauta wanda ranan da za'a naɗa mijinka a Masarauta zaka sa.
Shima Jaririn sanye yake cikin shiga na alfarma wasu picnh colour kayane tausasa kana aka daura masa ƙaramin Alkyabba fari irin na jarirai.
Sai hotuna suke ta ɗauka dasu Lalla, Khadijah Lalla, Hafsat Asiya, Asma'u, Dija, Rahama, Raudat Asma'u kuwa kai tsaye take turawa cikin group ɗin su na class mate ɗin su da suka gama makaranta.
Nan da nan cikin group ɗin ya kace me da surutu kala-kala kowa na tofa albarkacin bakinsa wata ƙawarsu wacce lokacin da suke makaranta bencinsu ke kusa da nasu Khausar mai suna Hawwa Idris ne tace.
“Ikon Allah wai Khausar ce haka🤔 girma yazo rawan kai ya gudu?”.
Tayi typing da emotion na mamaki dariya Asma'u ta tura mata tare da cewa.
“Gashi kuwa kinga zahiri”
Cikin Mamaki tayi voice dan gani take typing ɗin bai mata sauri kana tace.
“Masha Allah shiyasa akace arayuwa kada ka taɓa wulakanta mutum domin baka san baiwar da Allah ya

137 / 140

Chapters