Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKAWARIN ALLAH Bayan Hawaye by HUGUMA

Author :  HUGUMA Category :  African Stories & Novels

Chapter   8 / 53

21K to 24K   out of 156.9K words

kirashi,saidai harta gama ringing bai daga ba
"kin gani ko anty?"shahidan ta fada idanunta na cikowa da qwalla
"Bari na kirashi da wayata" anty amina ta fada tana daukan wayarta,ringin biyu ya daga cikin girmamawa
"Anty amina...da kanki?" Ya fara fada cikin girmamawa
"To ya zanyi?,diyata ta dagamin hankali?"dariya ya danyi
"Shahida ko?"
"Ita mana"
"Karki qona katinki anty bari nazo"
"Da kuwa ka taimakeni karta fashemin gata nan ta cika fam" da haka sukayi sallama tana duban shahidan
"Shima a muryarshi kadai ya isa kasan cewa yana cikin damuwa da kewarki,wanne irin so kukewa juna shahida?" Kunyace ta kamata saita soma sinne kai.

Ba'ayi minti talatin ba cikakke d'aya daga cikin yaran anty amina suka shigo suna cewa ga uncle da yake haka suke kiranshi,anty amina ta saka hijabinta tace suce mishi ya shigo.https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos

*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*

07067124863

*KO KUMA*

09032345899

*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sabbabi,karku manta ky danna SUBSCRIBE,kuyi LIKE sannan kuyi SHARINGπŸ™πŸ½*
πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½πŸ‘‡πŸ½

https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos

*Alqawarin Allah*
1️⃣0️⃣


A nutse cikin sallama ya shigo ta daga kai a hankali ta kalleshi saboda ita kadai tasan yadda tayi missing dinshi,shi dinma idanunshi na bisa kanta ji yake kamar ya shekara dari bai ganta ba,amma duk da haka saiya gintse saboda tuno ganinta da yayi da wani,daya daga kujerun falon ya samu ya zauna suka gaisa da anty amina sannan ta soma tambayarsa
"Wai me ya hadaka da shahida?,duk ka firgitamin diya?"
"Ta firgitani dai anty...bakiga har rama nayi ba?" Murmushi anty aminan ta saki,yadda sukeson junan nasu na bata sha'awa,bai boye komai ba ya gaya mata sannan ya dora da cewa
"Wallahi anty wani irin kishine dani,ina da matuqar kishi kan abinda nakeso,ranar dana ganta wallahi anty ban iya bacci ba"
"To kayi haquri mr kishi....bari kaji me ya faru" ta shaida masa kamar yadda shahidan ta gaya mata,nannauyar ajiyar zuciya ya saki yana jin kaman an sauke masa qaton dutse daga zuciyarsa,sai a sannan ya sami salama
"A rude nake anty,shahida ba ruwanmu bace mu talakawa,hankalina a tashe yake kada wani ya qwace min ita"dariya ya baiwa anty amina sosai har sai data dara
"karka damu anwar,shahida taka ce in sha Allah,yo shahida muka bata wani bakaiba ai inajin fiya fiya zata sha ta mutum" sosai anty amina ta baiwa shahidan kunya,har sai data diba a guje ta shige dakin anty aminan,shima ya miqe ya fice yana dariya.

A dakin ta taddata ta dubeta
"To laila majnun,saikije ku sameshi tunda na kashe case din,saiki kula a gaba"
"Na gode anty amina ta"
"Eh kyace haka mana tunda na dawo miki da hasken rayuwarki ko?" Dariya ta tuntsire dashi sannan ta miqe ta zura hijabinta ta fice.

Yana tsaye a soron gidan amma qofar fita yake kallo,tadan tsaya kadan a bayanshi,a jikinsa yaji tana wajen saiya juyo a hankali idanunsa zube fes a kanta,takowa yayi har sai daya rage tazarar dake tsakaninsu sannan ya tsaya,a hankali cikin wata murya dake cike da mayen so yace
"Nayi kewar wannan kyakkyawar fuskar,wannan ruhin ya hana ruhina samun barci bare ya samu salama,na cika da fargabar cewa na rasa hasken idaniyata,ashe abun duka ba haka bane" sosai kalamanshi suka sanyaya mata rai cikin daqiqu kadan,tayi qas da kanta tana fidda murmushi
"A'ah dago kanki sosai don na samu qwarin gwiwar fada miki albishir din danaso yi miki tun rannan mai mota ya korani"
"Don Allah ka daina zancan mai motar nan honey haba"
"Na daina" ya fada yana murmushi
"Na samu aikin kamfani Allah ya taimakeki...wani maqocinmu ne ya sama min,kwana goma sha biyar zan dinga aikin kwana,kwana goma sha biyar aikin wuni,zasu dinga biyana albashi duk wata dubu sha biyar" sosai fuskarta ta washe da fara'a tana jin farinciki na ratsata,tana jin burinsu ya soma daukar hanyar cika,rasa inda tsoma ranta zatayi har sai daya tsaya yana kallonta cikin mamaki,sun jima a soron gidan anty aminan kafin ya sanyata ta tattaro kayanta tazo su wuce gida,napep ya tsaida musu har qofar gida,sanda suka sauka ta zaro kudi zata biya ya harareta ya ciro daga aljihunsa ya biya,dariya kawai tayi,ko yaya idan yana da kudi ko iyakarsu kenan jikinsa baya yarda tayi masa hidima da kudinta,nan ma sun dan jima kafin suyi sallama ta wuce gida shima ya wuce.

Cikin taimakon Allah ya soma zuwa aikinsa,saidai babban qalubalen daya soma fuskanta shine na rashin kudin mota,tafiya ce mai nisa tsakanin unguwarsu zuwa kamfanin haka yake niqar gari ya tafi,duk da cewa ya saba tun sanda yana makaranta amma tafiyar bata kai ta makaranta nisa ba,sai kuma abincin da zaici shima saiya dawo zai jiqa kwakinsa yasha musamman idan aikin dare yayi zai dawo da safe,duka wannan bai dameshi ba tunda yasan cewa komao lokacine,hakanan bai yarda shahida ko anty usaina sun sani ba saboda baiga dalilin da yana namiji zai dinga daura nauyi wa mata ba,a haka ya cinye watanshi guda,saidai kafin cikar watan ya fada yayi baqi,hakan ya sanya shahida ta sanya ayar tambaya a kanshi.

Ranar daya amso albashinsa yazo da daddare,duka ya zube mata albashin nasa yana dubanta
"Me zanyi dashi honey?" Ta fada bayan ta gama saka musu albarka
"Inason ki dauki iya abinda ranki yayi miki,a matsayin albashin mijinki na farko" kai ta girgiza tasan ko tace masa a'ah cewa zaiyi bata isa ba saiya dauka,saboda haka tasan maganinsa.

Da fari ta ware wasu kudaden tace wannan kudin kayan abinci da zai siyo ya dinga dafawa yana tafiya dashi kamfani,ta sake ware wasu tace ya sake dinka kaya kala guda duk wata zai dinka kala daya,ta sake ware wasu tace ya riqe ya kashewa ne,sannan ta cire wani abu a ciki tace wannan ya kaiwa anty usaina ita yafi cancanta ta sanya albarka,next month kuma idan ya sake amsa to ya fara ajiya saboda lalurorin yau da kullum,duk sai data gama kasafin ya cakude kudaden waje daya sannan yace
"Qurun qus kin gama tatsuniyar taki?,toni ba haka nakeso ayi ba,da safe me mike ci idan zaki makaranta?"baki tadan cuno
"Kome meye ya samu"
"Good" ya fada yana cire wasu kudi ya aje
"Indomie da qwai nakeson ki koma ci" idanu ta zaro tana kallonshi baki bude
"Honey...me kake fada ne?"
"Abunda kunnuwanki suka jiyr miki.....wannan kuma kudin kashewarki na wata gud....."
"Kaga...don Allah ka tsaya ka daina wannan lissafin mana" nan sa'insa ta kaure tsakaninsu,da qyar ya yadda da nata lissafin bayan ta masa alqawarin wata na gaba ta yadda za'a sata cikin kasafin,saidai duk da haka yayi cancel kudin kashewarsa ya bata dole ta amsa saboda ya kafa mata sharadi.

Koda ya kaiwa anty usaina ma itama cewa tayi ba zata soma amsa yanzu ba,ya aje wajensa zata masa magana idan lokacin daya dace yayi,haka ya dawo dasu ya miqawa shahida
"Shikenan...zan saya banki na dinga tara maka,duk sanda kake da buqata saika amsa" washegari kuwa ta sayi bankin ta zuba masa harda kudin daya bata,ta nuna masa sannan ta roqeshi
"Don qaunar da kakemin kada kace a'ah,za'a tara ne ka siya abun hawa ko keke ne,ko baka fadimin ba nasan tafiyar qafa kake" da qyar ya amince da shawararta,donshi a son ranta tayi hidimar gabanta kawai dasu.

Wata hudu cif da fara aikinsa komai ya soma tafiya babu laifi,ta wanni fannin abubuwa da dama sun soma sauqi,cikin godiyar Allah da yadda da cewa komai lokaci ne.

Cikin haka aka fitar da ankon bikin umaima,wadda take cousin ce a wajenta,ranar data kawo musu ankon wuni tayi a gidansu,har dare tana nan,sanda ta tashi tafiya anwar yazo shahidan na wajensa,mubina ce ta rakota tana nanata mata idan ta tashi dawowa ta kawo mata alawarta,qarasawa tayi wajensu shahidan tana mata sallama daga bisani tace
"Ina zuba ido saikinzo siyan ankon,kuma wlh baki isa ba ba wani daya da zaki duka biyun zakiyi"
"To ummata" ta fada tana hararta,don batason ta tada zancan a gaban anwar din,sun riga da sun gama maganar su tun cikin gida,da haka sukayi sallama umaima ta wuce.

"Wai ina bankin nan kuwa?"
"Yana cikin gida"
"Idan yana kusa daukomin shi idan yana kusa" bata ce komai ba ta shige gidan ta fito dashi,bankin qasa ne ya amsa saiya sakeshi ya fadi take ya fashe kudin ciki ya bayyana,baki ta bude tana zaton itace bata bashi dai dai ba ya riqe ya fadi haka,sai taji yace
"Yauwa yayi dai dai,tayani qirgawa" cikin mamaki ta duqa ta soma tayashi hada kudin,bayan sun gama hadawa ya miqa mata yace ta irga,cikin murna da mamaki tace
"Da gaske ne kudi wawayene....ban zaci zasu kai haka ba wallahi" murmushi shima ya saki,walwalar da take kawai ta isheshi farinciki
"Kije ki sayi ankon ko kala nawa ne,saura kiyi dinki,idan ba zasu isa ba kiyimin magana" ranta ta ba'ta sannan tace
"Me kake fada ne?,kudin keken naka zaka bani kace nayi anko bayan sunkai kudin keke sabo harda canji?,kuma ma tuni umma tace zatamin daya abba guda daya"
"Duk bansan wannan ba....abinda kawai na sani shahidana zata saka kaya kamar yadda kowacce mace zata saka...kada kice zakimin musu indai baso kike raina ya baci" kaita duqar
"Allah ya baka haquri" dole ta fidda kudin ta sayi ankon kala biyu mayafi da abun daurawa,cikin sati uku suka shiga hidimar biki amma hakan bai hanata ganin anwar ba,shima hakan ya masa dama tunaninsa rashin ganinta.

Ranar da za'ayi dinner tun safe suna gidan kwalliya,qarfe biyar da rabi na yammaci ya kirata yazo ganinta tana ina,itama yana ranta don jiya basu samu ganin juna ba basa unguwar kwata kwata suna can aikin snacks,ta kwatanta masa gidan kwalliyar,ya gane gidan saboda cikin anguwarsu ne.

Sanda ya iso tuni an gama mata tata,zata wuce kuma gidan bikin ta saka kayanta kafin a soma dibansu zuwa wajen da za'a gudanar da shagalin.

Dan kwalinta a hannu ta fito soron gidan don kada ya bata mata kwalliyarta,dubansa tayi yadda yayi mata kyau cikin wani sabon yadi blue black,wanda aka yiwa dinki irin na matasan zamani,bata mancewa da ita yayi shawara kafin ya sayi yadin ta kuma zabar masa dinkin qarshen wata sanda aka biya salary ya cira a ciki yayi,anwar nada wata baiwa ta daban,idan yayi dressing kai kace shi din wani ne,daga kai yayi daga danna wayarsa da yake yana dubanta,subhanallah ya fada a sarari,wani azababben kyau yaga ta qara masa,kai kace ba shahidarsa bace,sai yayi sak yana ci gaba da dubanta,abun ba qaramin dariya ya baiwa shahida ba har sai data d'an dara
"Yaya anwar wucewa zanyi fa ana jirana.....tun daxun kake kallona sannan kuma kai baka ce komai ba" ta fada a shagwabe tana langabe wuya,ajiyar zuciya ya sauke sannan ya dubeta
"Ba inda zan barki ki fita a haka shahida....gaskiya zuciyata ba zata iya jurewa wasu su kalleki a haka ba a filin Allah wajen bikin dake cakude da maza da mata"
"To a yaya kakeso na fita?" Ta fada tana cuno baki wanda hakan ya sake tafiya da imaninsa,dan qaramin bakinta mai dauke da pink din labba yasha maroon din jambaki
"Mafita kawai ki wanke fuskarki" idanu ta zaro tana dubanshi
"Haba yaa anwar....haba don Allah" ta fada kaman zatayi kuka tana dan buga qafarta,fuskarsa ya hade sosai,harga Allah yana da wani irin kishi akan shahidan,yana jin kaman zai mutu idan wani ya zuba mata idanu bare akai ga batun furta yana sonta
"Ashe kuwa zaki shekara a soron nan,don na rantse ba zaki matsa ko inaba indai fuskarki da wannan kwalliyar" tasan cewa da gaske yake saita rasa ya zata masa,hakan yasa ta juya ciki ta yiwa amarya umaima magana,ita tazo ta roqa mata alfarma wanda daga qarshe yace saidai ta cire eye lashes din da aka qara mata don nata ma ya isheta,sannan kuma a goge wasu abubuwan da aka sa mata a fuska,saida akayi hakan sannan ya qyaleta,duk da haka a gaba ya sakata tana gaba yana bayanta,sai faman sakin ajiyar zuciya yake,duk da an rage kwalliyar gani yake kowa ma kallonta yake,adaidaita ya tare mata bai barta ba sai daya rakata har qofar gidan bikin,yana mata sallama zai juya itama ta tubure kan dole yaje wajen bikin,yasan da biyu tayi hakan don bai fiya zuwa wajen fate fate ba,to amma abinda bata sani ba gata tayi masa,don har yanzu hankalinsa bai aminta ba da zuwanta wajen ita kadai,gani yake tafi kowacce mace kyau,hakanan idanun kowanne namiji yana akanta
"Zanje na dawo,idan kun gama shiryawa kimin magana" tana masa dariyar cin galaba ta shige ciki.

Qarfe shida aka soma daukan 'yammatan,a sannan tuni ta yiwa anwar waya,shida da rabi ya kirata yace ta fito yazo,su biyu ne ita da 'yar anty umma yayar ummanta,ga mamakinta yana jingine jikin wata qaramar mota mai kyau qirar kia,ya sauya shigar jikinsa,wannan dinma yadine wanda tare ya siyesu da wancan,saidai wannan ruwan madara ne lallausa,shima bamai tsada bane amma sai taga kaf mazan wajen ba wanda ya kamoshi a kyau duk dacewa jayan jikinsu yafi nashi tsada nesa ba kusa ba.

Shi dinma gaba daya saiya daina ganin 'yammatan dake kai kawo a wajen,ita kadai take gani cikin dinkin ankon da ya amshi fatarta fiye da zato,kowa idonsa cikin na dan uwanshi a haka ta qaraso,baice mata komai na sai gaban motar daya bude mata ta shige,shima ya bude sit din driver ya zauna bayan kubra 'yar anty umma ta shiga gidan baya ya tada motar.

Saitake jinsu yau kaman rana ta musamman ce a wajensu,wani farinciki taji yana ratsata,ta samu kanta da addu'ar Allah ya shiga lamarinsu ya buda ma anwar din,motar tayi masa kyau qwarai da gaske kaman tashi
"Wani abokina ne ya dage lallai lallai yau sai na amsheta na dana,tun tana sabuwa yamin tayi ban taba danawa ba,kinga kuma bai kamata naqi ba karya dauka wani abun ne na daban kuma" kai ta gyada yayin daya dinga satar kallonta lokaci zuwa lokaci,har bintu ta fahimta ta d'an masa tsiya,kunya ta sanya shahida daukan wani plate data gani ta saka jikin redion motar,tadan qaro volume sanda taji batajin me yake fita daga cd din,waqa ce ta hamisu breaker waqar jarumar mata,sautin waqar ya ratsa motar,kidanta ya fita sosai ta speakers din motar ya karade ko ina,har ta saka hannu zata kashe anwar ya daga mata hannu alamar ta barshi,shuru ya ratsa motar saidai gaba dayansu waqar na ratsasu ne,ji suke kaman su suke rerawa junansu,shurun yaci gaba da yi musu jagora har zuwa inda za'a gabatar da bikin.

Sai daya rakata har ciki yayi mata mazauni,ya kuma gaya mata bai yadda da shiga rawa ba sannan ya fito ya dawo cikin motar ya zauna,wanda ya faka ne a bakin titi,sai yabar murfin motar a bude iska na shigowa qafarsa daya a waje.

Awa guda da fara gabatar da bikin yana zaune yasa sauraren redio
"Yauwa ga wani can....salamu alaikum" yaji an ambata,kanshi ya dago yana dubanta sannan ya amsa,matashiyar budurwa ce wadda a qalla ta doshi shekara ashirin da d'aya,sanye cikin doguwar riga da siririn mayafi,fuskarta saye da tafkeken glass,gabanta ne yayi mummunar faduwa saboda cika mata idanu da kwarjini da yayi mata,uwa uba kyau data jima bata ganshi tattare da wani d'a namiji ba,da qyar ta tattaro miyan bakinta tace
"Don Allah bawan Allah ko zaka taimaka ka duba mana motarmu?" Tayi maganar tana qare masa kallo ta cikin glass dinta,sai daya kashe redion sannan yace
"Me ya sameta?"yarfar da hannu tayi cikin yauqi
"toh wlh ban sani ba,ina cikin driving ta soma slow sai kuma ta tsaya gaba daya" dan jim yayi kafin ya jinjina kai ya fito daga motar ya rufeta sannan yayi gaba zuwa inda motar tata take.

Tsahon wani lokaci yana qoqarin ganin ya gyara saita tashi saita sake mutuwa,saboda haka ya dago yana goge hannunsa da tsumma
"Gaskiya dole sai bakanike yazo"ya fadiwa nafisa dake gefe tsaye suna qare masa kallo ita da qawarta mima
"Ya salam...bari na kirashi Allah yasa yana kusa" ta ciro tsadaddar wayarta ta soma nemanshi,cikin sa'a yace yana kusa ta bashi adress din inda motar take
"Idan ba damuwa ko zamu dan zauna cikin motarka kafin ya iso saboda zama a wajen ba dadi" nafisa ta fada sanda anwar ke komawa zuwa cikin tashi motar,tsayawa yayi ya waiwayo,kaman yace a'ah sai yaga mata ne bai kamata ya barsu tsaye ba,tunda motar tasu ba zasu iya zama cikinta ba,shi kuwa diya mace ako ina take yana da kishi da qoqarin kare mutunci da martabarta bakin gwargwado koda bai santa ba
"Ba damuwa" ya fada yana sake yin gaba,idanu suka hada da mima ta kashe mata ido gami da sakin murmushi suka bi bayansa.

Ya tsammaci duka baya zasu shiga,sai yaga mima ce kawai ta shiga bayan,nafisa ta shiga kujera mai zaman banza,sai data zauna sosai sannan ta waiwayo ta dubeshi tana murmushi
"Suna na nafisa....kaifa?"
"Muhammad anwar" ya bata amsa a taqaice,idanu ta lumshe
"Nice name...sunan ya dace da maishi" saiya waiwayo ya dubeta kafin ya dauke kai,murmushi ta sake saki
"Dan wanne anguwa ne kai?,Allah yasa ban matsanta maka ba da tambaya" kai ya jinjina sannan ya gaya mata unguwar da yake
"Kai ai bamu da nisa sosai" itama tasu unguwar ta fada masa,kusan duk unguwannin nasu maqotan juna ne,shuru ne ya sake ratsa tsakani yayin data lula duniyar tunanin yadda zata sha kan anwar,don ba zata cuci kanta ba kallon farko taji anwar yayi mata,infact ma zata iya cewa ta kamu da sonshi ne kai tsaye.

Isowar mechanic din shi ya katse duk wani tunaninta,hanya daya ta rage mata saboda haka ta miqa mishi wayarta
"Idan ba zaka damu ba ka sakamin numberka mana,saboda nayi maka godiya" kai ya girgiza
"Basai kinmin godiyar komai ba" kai ta langabe
"Ya zama dole na gode maka,saboda alkhairi kayi min" baison jan zancan saboda ya gaji da surutunta,saboda haka ya amshi wayar daidai sanda shahida ke takowa zuwa inda motar take,tana iya hango komai saboda akwai haske cikin motar,mummunar faduwar gaba ta samu,saidai ta kasa hana kanta qarasawa wajen,saitaci gaba da takawa harta isa bakin motar,daidai sanda ya gama saka mata number

8 / 53