Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKAWARIN ALLAH Bayan Hawaye by HUGUMA

Author :  HUGUMA Category :  African Stories & Novels

Chapter   38 / 53

111K to 114K   out of 156.9K words

da kyautatawa a rayuwa,da yadda yake kallonshi tamkar danshi,saidai ko daya zuciyarsa babu nutsuwa ko jin dadin karbar da yayi,bayajin wani daidaito ko daya kan batun nafisan,duk da agefe guda ya sani yana da buqatar kulawar mace,amma,ta yaya wata zata sanyo kai cikin rayuwar gidan alhali ga yadda take?,ta yaya zai kawo gyara?,tuninsa ya sake tafiya kan hotunan dake aje har yanzu suna yankawa gami da qona zuciyarsa duk daqiqa ko sa'a daya da zata shude,duk lokacin da idanunsa suka kai kai,yaha shahidan tsirara tare da wani sai yaji kaman mai shirin haukacewa,duk sanda ya kallo hoton yaga shahidan rungume qirjin daya daga cikin masu saida kayan maye sai yaji dama makaho ne shi,Allah ne kadai da qarfin addu'a suka sashi ya rayu har yakai bigiren da yake kai a yanzu.

Sassanyar ajiyar zuciya ya saki sanda yake kashe motar shi,ya daga hannunsa ya kira maigadin,cikin girmamawa ya qaraso
"Baqi indai ba 'yan uwa bane na jiki duk wanda yazo kace musa bama nan"ya qarashe maganar cikin muryar dake nuna jiki da zuciyarsa duka babu qwari
"To ranka ya dade" ya wuce ya koma bakin qofa yayin da shi kuma ya fito,ya dinga takawa a hankali zuwa cikin falon.

Shuru yake kaman koda yaushe,saidai ya hangi abinci a shirye saman dining,hakanan yayi sha'awar xama a falon,idonsa kan wata tasha da suke nuno fasahar zamani da qere qere,suna wani shirin kan na'ura mai qwaqwalwa,tsohon mintuna idanunsa nakan allon talabijin din,wani bayani da baqon nasu yakeyi ya dauki hankalinsa matuqa,yadda ci gaban xamani yazo da sauye sauye,yadda za'a qirqiri abu a idanunka kaga haka yake,amma da za'a sanyashi a na'ura sai kaga abun ba haka yake ba,tsahon minti ashirin yana bayanin wanda yayi matuqar daukan hankalinsa.

A hankali tunaninsa ya karkata ga abunda zuciyarsa keson tuna masa tun daxun,saiya miqe da hanzari ya soma haurawa saman cikin sassarfa,bai tsaya ko inaba sai bakin safe din nashi,cikin sauri ya tsugunna,ya soma saka lambobin sirrin ya budeshi,envalope din ya ciro kaman ko yaushe ya zazzage hotunan ciki duka suka fado
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" ya furta kaman yadda ya saba sanda yake binsu da kallo daya bayan daya,duk sanda zai gansu yakanji kaman duniyarshi sama ta kona qasa ne,kullum yanajin kamar ranar ya soma ganinsu,saiya zauna sosai zuciyarsa na fata da kuma burin samun mafita,xuciyarsa ta cika da fatan dama ace ba haka bane,dama ace ba ita bace,dama ace ba shahida bace a jiki shine bai ganin dai dai duk sanda zai kalla,saiya sake gyara zamanshi sosai,ta ina zai fara?,bashi da wani qarfin sani ta wannan fannin,idan kuma yi masa za'ayi duk duniya bayajin akwao wani mahaluki da zai iya bari yaga hotunan,koda mahaifiyarshi data haifeshi ce inda tana raye.

Sake miqewa yayi da sauri saboda tunawa da yayi da makarantar computer da sa'ida ta mishi xancan ummi ta musu register xasu fara zuwa,idan bai manta ba ta gaya mishi akwai online classes da special classes da za'azo har gida a koya maka,system yayi nufin kunnawa,sai yaga kamar ba zata masa sauri ba,ya ciro wayarshi daga aljihunsa ya kunna data sannan ha fada google ya soma rubuta sunan makarantar,bai manta sunanta ba saboda kusan ma'abocin siyayya ne a shagonsu na yanar gizo wato www.rahamalls.com,bakin gado ya koma sannan ya rubuta sunan makarantar *RAHA COMPUTER INSTITUTE* ,cikin qaramin lokaci ya samu dukkan bayanai,kuma tsarin ya gamsar dashi,ya dauki number dake cikin bayanan ya kira.

Cikin sanin daraja da mutuntaka tadan adam ya sake samun bayanan da yake buqata,cikin abinda bai gaza awa guda ba yayi register dasu da komai da komai,ajiyar zuciya ya sauke sanda komai ya kammala,ya duba agogo yaga lokacin daya kwashe,ya miqe a hankali yana fidda kayan jikinsa,ya sauya wasu marasa nauyi,wando iya gwiwa sai jallabiyya daya fitar ganin lokacin sallah ya kusa,ya shiga bandaki ya daura alwala,sanda ya fito wayarshi na ruri,gab da zai isa gareta ta katse,saiya duba mai kiran,nafisa ce,miscal na shida kenan daga sanda ta fara kiransa zuwa yanzu,sai a sannan ma zancan ya dawo masa,ya duba saqon data tura masa wanda na godiya ne da kuma ya yaje gida,aje wayar yayi ya isa inda magungunansa suke ya cira yasha,sannan ya fesa turare ya qarasa bakin gado ya dauki jallabiyyarsa ya saka,hakanan yakejin kaman wani nauyi ya ragu daga zuciyarsa.

Cikin mamaki ta dubi table din sanda ta fito daga dakinta,taji kaman ya shigo amma bataga alamun hakan ba,kaman zata share sai kuma taba hakan bai dace ba,kodon jikinsa takega ya kamata ta duba,idan lafiya lau shikenan babu buqatar sake damuwa ko saka ido.

Zai fita ita kuma zata shigo,kusan lokaci daya suka murda handle din,baya tadanja kadan bayan ta dubeshi ta dauke idanunta,sai taga kaman ya fada kadan daga jiya zuwa yau da kuma fitar daya sakeyi da dawowarsa,ganin alamun fita zaiyi sallah saita juya ta soma sauka tana cewa
"Sannu da zuwa"
"Yauwa" ya amsa yana tsaye cak yana dubanta sanda take sauka din,yanajin kaman ya rintse ido ya bude yaga duk abinda ya farun da wanda ke faruwa a mafarkine,bai taba kwana ya kwatanta a ranshi ko sau daya rayuwar zata iya zuwa musu da wannan salon ba,dai gashi lokaci daya komai ya canza,komai ya tabarbare,komai yazo da cikin wani bahagon yanayi.

Karon farko tun bayan rabuwarsu dayaji wani abu mai kama da tausayi tausayi akanta saboda tuna cewa nan gaba kadan nafisa xata shigo gidan a matsayin kishiya a wajenya,ya tuna yadda mata ke komawa duk sanda zance makamancin haka ya shiga kunnensu yatuna yadda nafisa ta birkice a sanda labarin wanzuwarta qarqashin inuwa guda ya shiga kunnenta,a sannanma bata zama qarqashin ikonsa na,basu taba kwana qasan rufi guda ba,inaga ita?,duk da bashi da tabbacin cewa zataji wani abu ko zata damu,saboda dukkan dalilin dake sawa mace tayi hakan babushi tattare da ita.

"Kidan samu kifi ki dafaminshi idan ba damuwa,zanje sallah na dawo" ya fada cikin laushin murya wanda har hakan yaso bata mamaki,saita juyo tana kallonshi,suka hada idanu ta sake dauke kai ganin yadda ya kafa mata idanu,taji kallon nata har cikin jikinta,sai taba baiken kanta data sanya kaya irin wannan ta zauna haka ko mayafi babu bare hijabi,amsa masa tayi da to tana ci gaba da sauka daga benan,har sai dayaga bacewarta sannan ya sauko shima yawuce masallacin.

Sai data soma shiga daki ta samu dan qaramin hijabi ta saka sannnan ta wuce kitchen din har yanzu tana mamakin irin salon da yayi mata magana dashi,ta ciro kifi ta gyarashi,ta kauda wancan tunanin na farko ta fada tunanin yadda zata sarrafashi ta yadda zai dace da yanayinsa,wani gashi ta tuno mai kama da romo romo da takanga anty xubaida bayi,ba bata lokaci ta soma hadashi,wanda cikin mintuna qalilan ta kammala,qamshi kuwa ya cika gidan ko ina,ta gyara komai a kitchen din ta gogeshi sosai yadda ta saba sannan ta fito don barin kitchen din.

Tunda ya dawo yana falon a zaune yana shaqar qamshin kifin har cikin zuciyarsa,da mamaki tadan dubi sashen da yake din,don iya zamanta a gidan batace ga sanda ta ganshi zaune haka sosao cikin falon ba,kamar yasan da tsaiwarta shima ya waiwaya yana dubanta,yabi hijabin jikinta da kallo,shima hakan yayi masa don tamkar gata tayi masa,baisan me yasa takeson ta zame masa tamkar wani maganadisu ba ko mayen qarfe aduk sanda ya ganta?,baisan me yakeson sauyashi haka ba,bayan a baya yasan bai damu da dukka shigarta ba,amma cikin abinda bai gaza sati biyu ba yanason sauyawa gaba daya?.*Alqawarin Allah*
44



Komawa tayi da baya kitchen din ta shirya komai ta dauko kan tray sannan ta sake fitowa
"A'ina za'a aje maka?" Nuni yayi kata da gabanshi,ta qaraso nan ta aje ta shirya komai ta dauko sauran na wajen dining shima ta shirya masa,tayi sarving dinsa sannan ta yunqura zata miqe saiya dakatar da ita yace ta zauna,ba musu ta koma ta zauna din,saidai duka bata jinta dai dai,baiyi magana ba harya qare cin abincin sannan ya soma da cewa
"Da can kafin aurenki ina tare da wata yarinya nafisa wadda har an saka mana rana lokacin biki ya rage saura sati uku,to wasu abubuwa suka biyo baya wanda ya zama silar fasa auren namu a wancan lokacin,a yanzu maganar ta dawo wanda ina tunanin duka ba za'a wuce sati uku ba nan gaba" bata taba tunanin zataji irin abinda taji a zuciyarta ba'a yanzu,tunda ya ambaci sunan zuciyarta da idanunta suka haska mata ita,saita dinga binsa da kallo kawai sanda yake bayanansa,gaba daya saita daina fahimtarsa,duka bayanan da yake kawai tana ganin yana yine saboda radin kanshi,yarinyar daya aiko mata da hotunanta sanda take tsaka da radadin rashin mahaifinta?,yarinyar daya turo mata da fuskarta sanda take tsaka da jimami da alhinin rabuwa dashi?,yarinyar daya kawo mata hotonta ta gani cewa ya samu wadda ta fita?,ya sauya wata a madadinta,a yanzu ita zai aura ya kawo gidan?,shine yake wani rufa rufa dason yiwa zancan kwaskwarima?,tana ganin abu mafi sauqi kawai ya fito ya gaya mata zai cika muradi da burinsa ne,yanzune manufar da yasa ya aureta zai bayyan muraran baro baro,me yayi saura?,me xata xauna taji daga bakinsa,ai komai ya qare hakanan komai ya fito fili,sai kawai ta miqe sanda yake tsaka da bayanin nashi,binta yayi da kallo ganin ta soma tafiya zuwa hanyar dakinta ba tare data ko waiwayeshi ba,kiran sunanta ya soma yi abinda ya jima rabonshi dayin hakan,saidai ko daya bata saurareshi ba bare taji me yake fada,da hanzari ya miqe ya bi baya,taji takun tafiyarsa,saboda haka tana shiga dakin ta saka key,ta samu gefan gadonta ta xauna ba tare datasan me zata tuna ba,wani kuka ne mai sautu ya qwace mata wanda ta kasa tsaidashi,hannunsa saman kanshi yana yamutsawa jin sautin kukanta dake ratso har inda yake tsaye
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" ya furta yana kallon qofar dakin da yayi juyin duniya ta bude taqi,bai taba xato ko tunanin xata damu ba ko sau daya,me yasa ta damu?,me yasa ranta yw baci?,bayan ta gaya mishi cewa bata qaunarshi ko kadan?.

"Me yasa kike kuka shahida?,kukan me kike?,kins kukane saboda mutumin da kika dainaso xai qara aure?,ko kina kuka ne saboda mutumin daya daina sonki xai auro wadda yakeso?,muradin zuciyarsa?,haske rayuwarshi?,meye abun damuwa a ciki shahida?,har yanzu anwar na cikin zuciyarki ko kuwa?" Tambayoyin da zuciyarta ta dinga mata kenan wanda yasa ta soma tuhumar kanta da kanta.

🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍


Duban nafisan mima takeyi sosai da wani irin banzan kallo,cikin ranta ji take kaman ta tashi ta shaqe nafisan,cikin ranta tana ala wadai da sakacin da tayi har ta bari tunanin nafisa yakai gata nemi anwar karo na biyu,tabbas da tasan da irin wannan ranar da tunu ta saka almakashi ta datse alaqar da tayi saura tsakanin anwar din da nafisan,koda yake a yanzu ma bata baci ba,saidai kuma ba haka taso ba,dole ya saka taka tsantsan da nutsuwa dinta wargaza tsakaninsu,don a yanzu bata da burin daya wuce ta ganta itama gidan anwar din a matsayin matarsa,sake duban nafisan tayi a karo na biyu yadda taketa faman fara'a,bakinta kamar zai hade da kunnenta,irin kallon da miman ke mata yasanya jikinta yadan soma sanyi
"Ko bayi dai dai bane hajjaju?,bafa zan iya haqura da anwar ba matuqar ina raye shima yana raye" baki miman ta tabe tana ci gaba da dubanta
"Dama aida kin jira ni nidin xan miki wannan aikin,abinda yasa kika ji shuru ba'a kai gabar bane,naso mu gasashine harsai ya kawo kanshi da kanshi ta yadda koda kin shiga saikinfi daraja da qima a idanunsa,amma a yanzun yadda kikayi wallahi qimarki ta zube qasa warwas,kuma haki da wata fuffuka da xakiyi idan kin shiga gidan,hasalima ba baiyi matsuwar shigowarki gidan ba kinga baki da abun cewa sawa ko hanawa koda kin shiga gidan" sai jikinta ya danyi sanyi,taji maganar mima tabbas tana kan hanya,shigen maganar da mummynta ta gaya mata kenan,ita kuwa a rayuwa yanzu burinta na gaba shine ta shiga gidan anwar ta zama ita ke fada aji,ita zata sa ayi ta hana kuma a hanu,wanda daga qarshe take fatan shahidan ta fita tabar mata gidan gaba daya taci gaba dayin yadda takeso.
"Gaskiyar magana mima banason nayi rayuwar da bani zance ayi ba cikin wannan gida,saboda har yau ina tsoro kuma ina shakkar soyayyar dake tsakanin anwar da wannan mayyar yarinyar" abun nema ya samu wajen mima,hanyar da zata wargaza rayuwar auren nafisan cikin sauqi,duk da haka saita sake tsuke fuska ta kuma gum da bakinta harsai da nafisan ta sake magantuwa cikin mitar tayi mata shuru,fuska ta yatsina
"In sake shiga sabgarki ki watsamin qasa a ido?,ina qoqarin fiddo miki da daraja da martabarki amma ke baki gani,gwara kawao na qyaleki kici gaba da samawa kanki mafita" harara ta watsawa miman
"Banason wulaqanci wallahi mima,haba don Allah,sau daya dai don nayi amfani da shawarar kaina saiya zama matsala?" Sai data gama shan qamshinta sannan tace
"Shikenan,zaki samu yadda kikeso,zaki mulka anwar ki kuma juyashi shida waccar yadda kikeso matuqar zaki jure ki kuma bi doka da qa'ida,zan dawo next week randa kikacemin zaki fara rabon IV zakiji sauran qarin bayani" kamar ta goya mima haka nafisa taji,kudade masu yawa ta baiwa miman sannan ta rakata.

Dariya mima ta saki bayan ta gama irga kudaden,mota takeson sauyawa,kuma ba shakka lokacin da zata sauya motar da takeso din yayi,a jikin nafisan zata hada kudinta tsaf,daga qarshe kuma ta tashi a tutar babu,ba anwar din ba kuma kudinta,daga haka ta tada motarta taci gaba da tafiya tanabin waqar dake tashi cikin motar cikin nishadi gami da tsara yadda zata mallaki anwar ita kadai bayan ta fitar da shahida da nafisan ma daga gidan dukkansu.

🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍


Kaman a mafarki take jiyo sallamar anty xubaida cikin falon nasu,da sauri ta sauko daga gadon wanda ta maidashi wajen rayuwarta,idan kaga ta fito tota tabbatar anwar ya fita baya gidan sannan zata fito tayi aikace aikacenta a gaggauce ta koma,sam bata qaunar haduwa dashi ko daya,Suna shirin yiwa kansu mazauni ta fito fuskarta a washe
"Anty yau a gida na?,ashe xakixo?"
"Kamawa ai take,gashi ta kama shahida naxo" cikin walwala da farinciki ta tarbesu.

,sun jima sosai ranar,sunata hira dasu huda,duk sai yaji kewar gida ta sake kamata,kaman ta koma gidan haka takeji.

Saida suka dan kebe sannan anty zubaidan ta gaya mata abinda ya kawota,zancan auren anwar,kebe fuska shahidan tayi cikin nuna halin ko in kula,saidai can qasan ranta wani abu ke tsinkulinta,maganganu sosai anty zubaidan tayi mata,gami da jan hankalinta,suna gama cin abincin rana tace zasu koma,kaman shahidan tayi kuka amma hakan ta haqura,taso sosai antyn tabar mata hudan amma qememe taqi,haka suka tattara tanaji tana gani suka tafi.

Zuwan antyn yasa tadan sake ranta,ta koma sabgoginta kamar baya,saidai ta sake janye sosai daga anwar din,sati biyu da faruwar hakan anwar ya shigoda set din manyan akwatina guda hudu,da farko tayi burus amma daga bisani tayi tunani kada ya tsammaci kishinsa take saita karba ta masa godiya,yayin daya bita da kallon mamaki,da gaske bata jin kishinsa? Hakan na nufin bata sonshi?.

Cikin kwanakin ka'in da na'in ya maida hankalinsa ga koyon abinda yasa gaba daga raha computer instute,ya ware lokaci har gida yake iskeshi malamin,baisan me yasa abun ya tsaya masa a rai ba,bai san me yasa ya maida hankali fiye da yadda ya xata ba,wanda yake da tabbacin cewa cikin wata uku ya cimma abinda yakeso ya cimma din,ta bangare guda guda kuwa yayi qoqarin kawo sauyi ko yaya yake tsakaninsa da shahidan,don ko kusa baida burin nafisa taxo ta fuskanci komai dangane da zamansu,duk da qoqarin nasa sau da yawa yakan cimma tasgaro,saboda rashin samun cikakken hadin kai daga shahidan.

Ta bangaren amarya nafisa kuwa shirye shirye sun kankama ka'in da na'in,dukkan wani abu da aka sani na bidi'ar biki ba wanda bata tsara xatayi ba,harda ma wanda ba' saba gani ba,ko sauraren abinda anwar din zai bayar batayi,sha'aninta kawai take.

Qarfe shida saura malamin da suke karatu tare ya tafi,yarage saura shi kadai a dakin,ya shiga cumputer din sosai yayi shige da fice wanda ya tabbatar masa lallai ya soma nisa,hakanan yana cimma abinda ya nufa din,saiya kasheta yana sakin murmushi wanda yayi dai dai da shigowar kira a wayarshi,duban wayar yayi sai yaga nafisa ce,ya manta shaf cikin satin zasuxo jeran kaya,bai daga ba harta katse,saiya janyo wayar yana laluba inda ya aje numberta,cikin sauyin da aka fara samu wanda ada bashi da ita.

Har tayi ringing sau biyu tana katsewa ba amsa,sai ana ukun sannan ta daga,shuru tayi tana sauraren muryarsa wadda ko mutuwa tayi ta dawo ba zata kasa gane muryar waye ba
"Bakisan ina cikin gidan bane?" Ya tambayeta ganin tsahon zamansu baiji motsinta ko gilmawarta ba,shuru babu amsa saboda haka ya kautar da wancan zancan
"Ki sameni a dakin karatuna....am yana nan daga baya kaman zaki shiga qofar kitchen ta baya" ya sake mata bayani don ya sani bata sani ba,tunda bata taba zuwa ba.

Wayar ta sauke tana jin wani haushinsa na kamata,tome zaiyi mata,kiran me kuma yake mata?.

Har sai daya zaci ba zata zo ba yaci gaba da aikinsa sannan yaji an murda murfin qofar,ya daga kai yana kallon bakin qofar,itace cikin jar doguwar riga wadda ta yane kanta da qaramin mayafinta,idonsa ya dauke wani abu na tsirga masa,ba kwalliya a fuskarta amma tayi masifar amsarta rigar wanda ya kasa kubuta daga qyasata da zuciyarsa tayi.

Daga sallama bata sake cewa komai ba,ta samu gefansa ta zauna,saiya kashe wayar tashi da yake dannawa,ya juyo gaba daya suna fuskantar juna sosai yatsunshi sarqafe da juna idanunshi cikin nata,fuskarsa na nuna zancan da zaiyi mai muhimmanci ne,sai taji kallon da yamata nauyi,ta

38 / 53