Author : Na'ima Suleiman Sarauta Category : Romance
magana mana kasan yadda na keji a raina,kaga idan aikin da kake a nan da matsala kawai ka ajjiye aikin bawai kuɗin da zan kula dakai ne bana dashi ba maza ka fara shiri daga yanzu zuwa ko wanne lkc jet zai sauka gareka"
maganar Abbu ce ta dawo dashi daga tunanin daya tafi,wanda rabin tunanin na Zarinansa ne,wacce a kullum yake cikin tunaninta,har yanzu ya kasa yadda cewa bata garesa,kuma ya kasa yadda bata cikin masarautar,yaya zaiyi yana jin zuciyarsa na zafi da raɗaɗin,ji yake kamar ya buɗe baki yayta ƙwarara ihu sabida zallar damuwar da yay masa yawa a zuciya,amma taurin ransa da jajircewarsa ya sanya da wahala ka gane abinda yake damunsa a rai,baya son bai yana rauninsa ta dalilin hakan baya son akan mace ya gaza.
numfashi mai ɗan ƙarfi sabida maganar Abbun daya kuma yi a karo na biyu da yake faɗin.
"abokina ba zaka faɗamin what is going on ba?,ok good ka jirani"
yana faɗin hakan ya katse wayar cikin ɓacin rai,ɗan juya manyan fararan ƙwayar idanunsa yay tare dabin wayar da kallo.
"what should i do?"
ya tambaya cikin zuciyarsa,domin yasan Abbunsa kaifi ɗayane idan yace zai abu babu shakka sai yayi kuma babu wanda ya isa yay masa musu bare ya tankasa,yana dq zafin zuciya idan ransa ya ɓaci,shiyasa koda Saifune yay abu yakan masa uzuri domin yasan cewa kaɗan ya ƙwace daga cikin halayyar mahaifin nasa.
ƙara rolling eyes ɗinsa yay zuciyar fal tsoron abinda Abbun nasa zaiyi,to mezaizo yay a bilhas? shin kodai yaji abinda Mai martaba ya faɗane?.
ganin bashi da wata mafita akan hakan ya sanya ya cilla wayar cikin aljihu,a hankali kuma a nutse ya juya ya fuskanci Mai martaba wanda yake tsaye gefensa kuma su Tiraki ne,Chiroma,Waziri,Sarkin fada,da Fadawa sune sukaiwa Mai martaba ƙawanya suka sanyashi tsakiyarsu.
lumshe idanunsa yay few minutes kuma ya ƙara saukesu a fuskar Mai martaba daya kafeshi da idanu.
wani murmushi takaici Mai martaba yay ya tabbatar Saifu he never say anything,sosai yake mamakin jinkai da isar yaron,Numfashi ya sauke tare da ɗan matsuwa kusan Saifu ya gyara zaman alkyabbar jikinsa yace.
"Wanene kai?"
waro manyan fitinannun idanunsa waje yay,dan baiyi tunanin abinda ya kawo Mai martaban ba kenan,kallonsa kawai yake ba tare daya amsa tambayar da yake masa,bashi da amsar tambayar gaba ɗayanta,bawai dan shiɗin bashi da gata ko kuma a sali ba,a'a sabida rainin hankalin da yake cikin tambayar ne ya sanya bazai iya cewa komai ba.
wani huci Mai martaba ya sauke a fuskar Saifu,cikin tsananin ɓacin rai haɗi da tsawa yace.
"do i look like idiot to you?haaa harni ina maka magana kana ƙin amsani,kasan waye ni kowa?dukkan mutanan da suke garin bilhas iko nane kuma mallakina ne daga ciki kuma harda kai,domin a bilhas yanzu kake rayuwa,ya zama dole kabi umarnina and ina da ikon da kuma ƙarfin mulkin da zanyi ko mene nakeso babu abinda zai faro kuma babu wanda ya isa yay magana akai sabida ina sauraranka waye kai?
pouting lips ɗinsa yay yana jin tsawar da Mai martaba yay masa na hautsina kansa,bawai danga shigesa ba aa sabida azabar da ciwon kansa yake masa,ga kuma zallar damuwar rashin abokiyar rayuwa,tsaiwarsa ya gyara tare da sanya hannu ya shafi ƙwantaccen gashin dake manne gefe da gefen fuskarshi wanda suka ƙwanta lub lub abinda sai ƙyalli suke.
cikin wata cool and serious talk voice yace.
"Wow!! mai Saifudeen Bilyam ya tarewa Mai martaba Khalid Wazeer bilhas ne a rayuwa?"
(kada ku manta Wazeer ya haifi KHALID da SUFRAK,SUFRAK KUMA YA HAIFI SUDAIS).
yay tambayar yana mai ɗauke kansa daga kallon Mai martaba.
"hattara dai ɗan talakawa ƙarya kake"
cewar fadawan.
Mai martaba wani murmushi yay sosai maganar ta daki kansa,yau shine wani,waninma wanda ba ɗan garinsa ba yazu har gabansa yana kiran sunansa without respect,cikin dakiya yace.
"bana da matsala da talaka na,koda akwai zanyi amfani da ƙarfin mulkina wajan ganin na tarwatsata,matsalar kaine kakeso kunnuta da kanka ba tare daka sani ba,amma gayamin wanene kai shine zai tabbatar da abinda nake tunani gsky ne ko kuma akasin hakanne"
"Kaga yaro duk babu sa'anka a nan zaka faɗa cikin ruwan sanyine ko kuma saika koma ɗakin duhu"
Chiroma ya faɗin magnar yana me nuna Saifu daya tsa,
hannu Saifu ya saka a saman kansa tare da murza forehead ɗinsa wanda yake fidda gumi kaɗan².
kasa ce masu komai ba,dan gaba ɗaya bashi da lkcnsu gaba ɗaya hankalinsa ya koma indai ya fito tabbas a yau basai gobe ba,zai barmasu wannan masarauta barin da bazai taɓa dawowa cikinsa ba,sai dai idan a zanan qaddararsa aƙwai dawowa ɗin wannan ya san babu yadda zaiyi domin mutum baya taɓa gujewa qaddararsa.
cikin ɓacin rai da kuma gajiyawa da maganar da suke masa,hannu ya ɗaga masu tare dayi masu wata gigitacciyar tsawa wacce ta sanya gaba ɗayansu yin baya,girman tsawar da yayi ne ya sanya Mai martaba saurin runtsa idanunsa.
cikin wata kakkauciyar murya mai amoo ta sauti yace.
"Mene matsalata daku ne ayeee?aiki ya kawoni nan bawai neman magana ba,da nasu gaba ɗayanku ina da hanyar da zan sanya a ɗaureku cikin sauƙi,ina da sanin cewa ka tura har part ɗin dana sauka domin a ɗauko maka system ɗin,wow this is wonderful,baka samu wannan ba,ka sanyani abinda tunda nake a rayuwata ban taɓa yi ba,ahaaa burinka ya cika ka tuzar tani cikin mutane,hakan baiyi maka saida ka sanyani cikin ɗakin duhu na wajan watanni huɗu,tunaninka hakan zai zama ajalina baka san cewa Ubangiji shike kula da bawansa ba,shine mai iko da dukkan wani numfashi da ɗan adam yake shaƙa,bayan nafito wancan mahaukacin ɗan naka ya tsareni da shirmansa,wlh wlh idan kuka sake fushina ya kufce a kanki za kuyi bayani,hakan duk bai isheku ba saida kuka san yadda kukai kuka rabani da farin cikina kuma muradin rai da zuciyata,sabida kunsan cewa itane raunina,aikine daga yau na daina sai...."
"Ohhh shiiit pls dear"
Maganar mai babban ɗaki da katseshi daga abinda ya keson ƙara faɗa,huci kawai yake sabida tsananin ɓacin rai da kuma damuwa idanunsa har wani jan ruwa suke kawowa,gaba ɗaya jijiyoyin kansa sun fito sunyi raɗaɗa.
jikin Mai babban ɗaki ya faɗa yana maida numfashi gaba ɗaya jikinsa rawa yake,ƙara shigewa jikinta yay,lkc guda kuma wani zazzafan zazzaɓi ya shiga ratsa nama da ɓarkon jikinsa,sun haɗu da ciwon da kansa yake ba.
cikin azaba da kuma sauyawar yanayi ya soma fidda wani numfashi hqransa suka shiga haɗewa suna bada wani sauti na ƙasss ƙasss.
jansa tayi zuwa wani ƙawataccen bedroom yayinda shine ya zame mata jagora sabida ba gani take ba,suna take tana lalubar hanya,har suka ƙarasa cikin tsaftaccen bedroom wanda aka cika da kayam mure rayuwa na musamman,komai na ɗakin green ne,kana ganin ɗakin kasan mamallakin ɗaki ba ma'abocin fita bane sabida dukkan abinda ake buƙata komai aƙwaishi.
a gefen bed suka zauna gaba ɗayansu still kuma yana jikinta bai bar rawar sanyin da yake ba,rungometa yay sosai a jikinsa sai a lkcn wani wahalallan kuka mara sauti ya ƙwace masa sai ajjiyar zuciya yake saki.
shuru tayi masa domin tasan kukanne kawai zai masa maganin abinda ke damunsa a cikin ransa,bayansa kawai take bubbugawa tare da hautsina masa gashin kansa.
Mai martaba wata zufa ya sauke tare da kallon sarkin fada yace.
"aje a fara shirye-shiryen naɗa magaji sarauta a yau basai gobe ba zanyi murabus"
gaba ɗaya suka juyo suna kallonsa da makaki,tabbas dukkan abinda zai sanya Mai martaba ya faɗi hakan ba ƙaramin abu bane.
"Allah ya taimakeka ya ƙara maka lpa ya saka kafi haka zai a matsu da kayan naɗin kusa kasan sai dasi za'a ɗanashi, dole sai an kawo TAKUBIN NISFU,DA HULAR GARKA,DA ZOBEN GIRMA sannan za'a ɗura Magaji akan kujerar sarauta"
Sarkin fada ya faɗa yana mai ƙurawa Mai martaba idanu,wani shegen murmushi Chiroma yay kana yaja bakinsu yay shuru.
jinjina kai Mai martaba yayi tare da faɗin.
"Wannan duk suna wajan Chiroma da anzo naɗin zai kawosu,zoben kuma yana wajan magaji kaga babu abinda damuwa duka a ciki"
yana faɗin hakan ya juyawa domin fita gaba ɗaya suka rufa masa baya har zuwa ƙofar tirakarsa yana shiga suma duka suka nufi sashinsu zaman fada ya ƙare sai jiran zuwan gobe ai naɗi.
Lil prince kam bai san abinda ke faruwa hankalinsa gaba ɗaya yana kan Zarina,bashi da wani tunani sai nata,dukkan inda yake saka ran ganinta babu ita.
ƙwalbar giyar data zama wajan ta biyar ya sauke daga cikin bakinsa,a hankali ya ɗaga jajayen idanunsa ya kalli jama'ar da suke cikin makeken club ɗin wanda ya zama mallakinsa.
wata iska ya fesar kana ya kalli Yazeed dake gefensa yace.
"ina sonta,ina sonta yaya zanyi Yazeed?wlh dukkan namijin dana ganshi tare da ita nine ajalinsa zanci gaba da nemanta,zuwa gobe zanje inda muka sameta may be nayi sa'ar samunta,a wannan karan zance mata da yarda da kuma amana zannuna mata zallar so da ƙauna da kuma ƙyautatawa"
sosai yay bawa Yazeed tausayi lallai dukkan macen da Prince yace ya naso abinda dubawa ne,domin da ace dan sha'awa yake sonta aƙwai mata da yawa wanda suka fita,numfashi ya sauke yace.
"amma mai zai hana ka hqr da ita?ina ganin kamar tafi ƙarfinka ni a ganina kawai ka hqr ka auri Meyrah tunda kana jin daɗin taryya da ita amma banjin zaka samu farin cikinka Zarina am..."
shaƙar da Lil prince yay masace ta kasa bashi damar ƙarasa sauran maganar da yay niya.
da hannu ya nuna yana mai jijjiga kansa sai kuma ya sakeshi yay waje,yana zuwa ya faɗa cikin motarsa tare dayi mata key yaja da gudu yabar club ɗin.
a wani waje yay parking yana gama parking wasu ƙarti mutane sukazo wajansa,magana sukai kana ya nuna masu wani abu a waya,da dukkan alamar pic ɗin Zarina ne,kana ya ɗauki kuɗi da yawan gaske ya basu.
cikin sauri yaja motar ya nufi cikin Masarauta.
Saifu
sosai yay kukan daya ishesa,kana ya soma sakin ajjiyar zuwa,jajayen idanunsa ya ɗaga ya kalli Mai babban ɗaki ciki wata kasalalliyar murya yace.
"Ammi yaushe zan huta ne?yaushe farin ciki zai dauwama cikin zuciyata,mene ya saka babu wanda ya damu da damuwa sai mahaifina?mene ya saka matar dana amince da ita ta zaɓi da gujeni akan ta zauna dani?mene ya saka wannan mutanan suka sanyani a gaba nemai masu maina tare masu?..."hannunta ya kama ya ɗura saman ƙirjinsa wajan zuciyarsa yace.
"zuciyana ciwo Ammi dan Allah ki nemo Rinaaa itane maganin damuwata itace zata ɗaukemin ciwon da nakeji a cikin zuciyata ina sontaaa..."
kansa ya kifa saman cinyarta yana sauke numfashi,jiya yay gaba ɗaya zaman masarautar ya damesa gefe guda kuma yana jin faɗuwar gaba da kuma tsoro na ratsa zuciyarka gaba ɗaya hankalinsa yaƙi ƙwanciya yana jin kamar wani abu na shirin faruwa dashiii.
Mai babban ɗaki kasa magana tayi domin ita kaɗai tasan abinda yake mata zafi a rai,tana jin kamar ta fishi shiga damuwa.
Hadima Kaltume ce ta shigo bakinta ɗauke da sallama.
Mai babban ɗaki ta amsa kana ta zame kan Saifu dake cinyarta ta shafi sumar kansa tace.
"maza jeka part ɗinka ka ƙwanta kaga dare yayi da safe kazu ka saman"
kai kawai ya ɗaga mata yana ƙara lafewa jikin luntsumemiyar katifar.
hannunta Kaltume ta kama suka nufi part ɗinta domin lkcn dare yayi sosai wajan sha biyu da arba'in.
Misalin ƙarfe biyu da rabi na dare wasu ƙartin mutane majiya ƙarfine suke shiga part ɗin hannunsu ɗauke da manyan bindigo masu girman gaske,dukkansu sun rufe fuskarsu da baƙin yadi.
kimanin so goma suka shiga part basu tsaya ba saida suka shiga har cikin bedroom ɗin ƙwance suka sameta kan mamaken gadon yana bacci ya rufe jikinsa da duvet.
da idanu wani yay magana cikin sauri wani ya zaro wata injection daga cikin aljihunsa kana ganin allurar kasan aƙwai wani mugun abu cikinta.
wani yay murmushi yace.
"finally Captain Saifudeen Bilyam zai zama mahaukaci"
a kuma dai² lkcnne mutumin ya nufi wajan da yake a ƙwance yana zuwa ya saita baƙin allurar ya caka masa a bayansa.....
*NIMCYLUV🤏🏼🔥*
*67-68*
*_Littafin nan na kuɗi ne kada a fitarmin dashi waje,The New Emir zaku samu akan 200 dukkan maiso zai nemi wannan number 08119237616_*
injection ɗin da sukai masa irin mai ƙarfin gaske nance,wacce lkc guda take shiga cikin brain ɗin mutum ta hautsina tunaninsa,yadda allurar take da dafi ya sanya ba ko wanne asibiti ake ajjiyeta ba,wasu ma sai dai suyi oder nata daga ƙasar waje.
sau biyu suka samu nasarar saka masa allurar a kuma dai² inda ake buƙatar aiwa mutum ita,ba tare sunyi magana ko kuma sun ɗauki wani abu a part ɗin ba suka juya a hankali suka fice daga part ɗin gaba ɗaya.
suna fita suka nemi wata hanya ta baya ina a nan suka riski Lil prince yay masu jagora har suka fice daga masarautar baki ɗanya,domin ace da ɗan gari akanci gari.
kiraye kirayen sallar asubane ya farkar da Mai babban ɗaki daga baccin daya ɗauketa,sallati tayi tare da addu'ar tashi daga bacci,a hankali ta fara laluban hanya kana ta sakko da ƙafafuwanta zuwa ƙasa,hakan yay dai² da shiguwar Kaltume.
da sauri ta ƙarasa wajan ta taimaka mata tare dayi mata jagora har zuwa toilet,al'wala tayi kana ta bubbugawa ƙofar alamar ta gama hakan ya sanya Kaltume ta shigo ta kama hannunta tare da nufar cikin bedroom da ita
ladduma ta shimfiɗa mata kana ta sanya mata hijab ta ajjiye mata casbawa a gefenta.
cikin ƙasa da murya Mai babban ɗaki tace.
"jeki part ɗin dana kai Saifudeen ki ganemin ya tafi sashinsa,idan yana nan saiki tashesa"
da "to" ta amsata kana ta nufi part ɗin,shuru taji babu kowa tun daga ƙaramin ɗakin har zuwa ƙofar bedroom,ƙofar ta tura tare da sanya kanta cikin bedroom ɗin.
ganin ɗakin duhu ya sanya ta lalubi bedside inda lamp yake ta kunna wani blue light,ɗan waro idanu tayi cike da mamaki tace.
"he already left"
cike da rashin gamsuwa ta tura kanta cikin bathroom ɗin nanma shuru ne babu kowa ciki,hakan ya tabbatar mata da cewa tun jiya ya fice daga cikin ɗakin,cike da addu'ar sama masa nasara a rayuwa ta juya zuwa bedroom ɗin Mai babban ɗaki.
samunta tayi zaune harta iddar da sallar tana lazimi,cikin girmamawa tace.
"Allah ya taimaki Mai babban ɗaki aina lura tun jiya yabar part ɗinan gaba ɗaya domin baya nan"
jinjina kai Mai babban ɗaki tayi cike da gamsuwa,ba tare da ta kuma cewa komai ba ta sunkuyar da kanta ƙasa tare da lumshe idanunta,wannan lkcn casbahar kawai take jaa,amma a cikin zuciyarta ita kaɗai tasan abinda yake damunta a rai,wani tsoro da fargaba ne ya shigeta wanda bata san dalilin hakan ba.
Kaltume kitchen ta nufa domin haɗawa Mai babban ɗaki dafaffiyar madarar shano,duk safiya da ita take fara breakfast.
bayan fitarta Mai babban ɗaki kishin giɗewa tayi zaune a ladduma wani sabon baccin ya ɗauketa.
Misalin ƙarfe 11 na safe da sassarfa Lil prince yake tafiya domin amsa kiran Mai martaba,a kuma yau yake saka ran tafiya neman Zarina,wacce ya ɗauki al'washin aurenta a lkcn da yay arba da ita koda a court ne ya amince ya ɗaura masu aure.
gefensa kuma Meyrah ce sanya ta fararan kaya irin na kuyangu,hannunta riƙe da jakar Lil prince wacce ya sanya kayasan kusan kala uku ciki
yana tafe yana danna waya harya samu nasarar kammala transfer ɗin da yake na kuɗi kallonta yay yace.
"Be happy na maki transfer kuɗi na kimanin 2.m sai ai shagalin biki lafiya,tunda ba'a samu damar yin shagalin babbar salla ba ko?"
dry tayi kana ta riƙe hannunsa tace.
"thanks nima yau nake son tafiya gida,tunda kaga daman dominka nake zaune a nan,so kuma babu kai dole tasa zan tafi duk da zanyi kewanka cikin raina..."
"naso kin tsaya kinga yadda uban girman kancan zai dinga timamin hauka just imagine ace Captain Saifudeen Bilyam yana yawo naked babu kaya sabida zallar hauka,amma babu damuwa as soon as na dawo kema zaki dawo mu ɗura daga inda muka tsaya"
lil prince ya tari numfashinta ta hanyar faɗin hakan,a kuma lkcn suka kawo hanyar shiga Fada,jakar hannunta ta miƙa masa kana ta juya ta koma part ɗinsa ba tare da tace ƙala ba.
cikin fadar ya shiga yana zuwa ya zauna gaban Mai martaba tare da gaidashi.
gyaran murya Mai martaba yay tare da gyara zaman alƙyabbar jikinsa ya kalli Lil prince yace.
"Magaji ka shirya a yau da yamma za'a na ɗaka Sarkin garin bilhas,bayan nan za'ai bikin naɗi a kuma lkcn za haɗaka aure da wacce na zaɓa maka"
jinjina kai yay zuciyar fal farin ciki,domin burinsa a yanzu guda biyune,ga kuma guda ɗaya zai cika,shi kaɗai yasan irin zallar ikon dazai kafa a mulkinsa wanda ko mahaifinsa bai isa yay irin wannan ikon da kuma gadarar ba.
lallai kasan cewaraa Sarkin bilhas shizai bashi damar girmama night club ɗinsa ba tare da tsoro ko kuma shakka ba.
hatta aure da zaiyi dan yana son yarinyar ne banda haka babu abinda zaisa yay wani aure matan garima sun ishesa.
wannan rana ita yake jira domin samun damar amshe makarantar islamiyar dake ƙauyen bilhas domin gina event senter.
gyaran Mai martaba yayi a karo na biyu ya kuma faɗin.
"Ni Mai martaba Khalid Wazeer bilhas nayi Murabus daga kan kujerar sarautar a rana ta Litinin wanda yay dai² da 5/4/2021 inda ɗana Prince Najeyb Khalid Wazeer bilhas zai maye gurbina"
gaba ɗaya wajan ya ɗauki kabbara,sai a lkcn Lil prince ya fahimci jama'ar dake wajan kamarsu Hakiman bilhas,da kuma dagatai,haɗi masu unguwanni,sai kuma manya daga gida Gwamnati da kuma ƴan ɗaukan rahoto wato ƴan jarida,da kuma ƴan gidan t.v.
dukkan wani wanda yake da iko a ɗanin sarautar yana wajan.
a hankali Mai martaba ya zare rawanin dake kansa tare da ajjiyeshi gefe,kana kuma ya miƙe daga kan kujerar karaga.
idanunsa ya ɗaga ya kalli Lil prince ya sakar masa murmushi tare da ɗaga masa hannu alamar jinjina.
Chiroma ne ya kama Prince ya miƙar dasbi tsaye tare da nufar kujerar mulkin dashi yana ƙoƙarin ajjiyeshi Sarkin fada yace.
"Dagata Chiroma kasan babu wanda ya isa ya hau wannan kujerar sai an kawo shaidun dazai nuna cewa mutum ya gaji sarautar kamarsu Takobi,Hula,da kuma Zobe"
murmushi Chiroma yay yace.
"eh ƙwarai hakane Kai lil Prince saika kawosu"
sai a lkcn Mai martaba ya ɗaga kai ya kalli Chiroma cike da tuhuma yace.
"Kamar bayan kayan yana wajanka,bakai na bawa ajjiya ba?"
gyara tsaiwa Chiroma yay yace.
"ƙwarai ni kamawa ajjiya amma ka sani kamar yadda kake da iko da wannan kujera nima ina da ita,na daɗe ina neman hanyar da zanbi na samu wannan mulkin amma wannan lkcn shine yay dai² da ra'ayina,kada ka manta dukkan wanda ya kawo wannan kayan shine da mulki"
gaba ɗaya Mai martaba da Lil