Author : Cwt Sumiey Category : African Stories & Novels
mata ba,kin zo ne ki yi abinda kika saba sai kuma reshe
ya juye da mujiya".
" Mama dan Allah ki k`yaleta ki zo mu tafi,ki bar kula ta ",Cewar Hibba hawaye ma zuba daga idonta.
" Babu inda zani don banga dalilin da zai sa in barta ta cigabada da cin kashi a kaina ba,iya Wanda tai a
baya ma ya Isa".
"Aiko dai maganar ki gaskiya ce Yaya ai Baba Asabe bai kamata ace ita ce ke furta irin wannan laffuzan
ba,ita ma Hibba matsayin `ya take a wurinta bai kamata ta fad`i munanan kalamai akanta ba", Cewar
Umma Jamila.
Umma Hafsat ce ta amshe zancen da cewa" Anya kuwa kun fahimci lamarinnan dai-dai kuwa,ni a
tunani na gaskiya Baba Asabe ta fad`a, shin mene ne aibun zancenta anan,ku duba fa ku gani kaf
Gidannan ba wata d`iyar da aka haifa a cikin Gidannan da tazo tai irin wannan zaman da take"....
Umma Maimuna ce ta matso tana mai gyara d`aurin zanin jikinta tana mai cewa"A'a a'a Kema kin so
rashin gaskiya tun farko Yaronnan sai da ya baku uzirinsa,wacce ta ke matsayin mahaifiyarsa ce bata da
lafiya,kuma ba a wannan Garin take ba,ita kuma Hibba tana buk`atar kulawa,ta na buk`atar wani a kusa
da ita,shi kuma ba shi da kowa anan kuma ba mazauni ne ba,ko kun fi so ya barmu `yar ku ita kad`ai a
Gida duk abinda zai same ta ya same ta,shin haka ne manufarmu ku ko wani abu na daban ?".
"Bar su kawai su fad`i duk abinda suke so ,amma ina so su kwana da sani Hibba ba inda zata har sai
bayan ta haihu, maganarsu kuma ba abinda zata sa ko ta hana", Cewar Mama Hadiza ran ta a `bace.
Ummie Maryam ce ta matso kusa da ita tana mai cewa," Dan Allah Mama ku bar wannan maganar
haka a barta ta wuce,babu dad`i ace a Gidannan ake wannan hayaniyar, bai kamata ba",
Tunda su ka fara wannan hayaniya Hibba ba ta iya cewa komi ba sai faman zubar da hawaye kawai ta
ke,ita kanta ta rasa me tayi ma Baba Asabe da har ta tsane ta haka ko dai don rashin Auren d`anta da ba
tayi ba ne ba oho.
Shigowar Baba Malam ne yasa rikincin ya kwantawa bayan ya ba Baba Asabe rashin gaskiyar abinda ta
aikata, kana ya sallami kowa ya bar gun,Ummie Maryam ce ta tafi da Hibba d`akinta tana lallashin,gami
da janta da hira ko da wasa ba ta bar ta ita kad`ai ba balle har ta samu damar tuna abinda ya faru ko
barin shi a ranta.
*Bayan wasu kwanaki*
"Gaskiya wannan tafiyar ta ka ta yau tayi sauri ka iso da wuri".
"Na ta so da wuri ne,saboda ina son in yi shearing d`in happiness d`in da na samo tare da ke"," Masha
Allah na ta ya ka murna tun kafin inji me muka samu".
"Grandma ta samu sauk`i an sallameta yanzu haka suna Gida ita da Cecelia ,tana tafiya da k`afafunta ba
tare da taimakon k`arafa ba", ya kai zancen fuskarsa na washewa da mad`aukakin farin ciki.
" Kai Alhmdllh Masha Allah wannan labarin yayi dad`i,ko ba komi hankalin mu gabad`aya zai kwanta
tunda Grandma ta samu sauk`i komi zai koma normal ".
" Sosai ma wani k`arin abun farin cikin na yi magana da Mahaifin Samuel wanda zai Auri Cecelia mun
sasanta yanzu ya yarda za ai bikin su nan da wani lokaci".
"Ikon Allah wannan shi ake kira da dad`i kan dad`i ga Grandma ta warke kuma ga shi za ai Auren
Cecelia ba abinda zamu ce da Allah sai Godiya mara adadi domin hakan duk kad`an daga cikin
iko,buwaya,k`udira da kuma izininsa".
" Haka ne my wife nasani shi kad`ai ke da iko gami da izinin aikata abinda ba kai zato da tsanmani
ba,domin a cikin mu babu Wanda yai zaton Grandma zata sake taka k`afafunta, haka kuma babu wanda
ya sa ran Mahaifin Samuel zai sauko ya yarda ayi Auren d`ansa da Cecelia kasancewar sa mai tsananin
lafiya akan duk abinda ya ce,amma sai gashi Allah ya tankwasar da Zuciyarsa har ya amince da za ai
Auren ".
" Haka ne gaskiya domin ni kaina yanda kake bani labarin yanayin yanda yake behaving in ka je masa
da maganar dai-dai to a tsakanin ku abun har tsoro yake bani".
"Wallahi kam,hakan ba k`aramin imani ya k`aramin min ba"," Ai haka ake so,duk abinda ya faru da kai
a rayuwa ba hakanan banza ya je zuwa ya tafi ba, dole akwai wani darasi da ake so ka amfana da
shi,walau darasi mai kyau ko kuma akasin sa".
"Amm na kwaso gajiya ya kamata in zo in tafi, 9pm kar dare yai min sosai"," To shikenan my darling
husband Allah ya tsare min kai ".
"Amen amma kin san me ?", ya cigaba batare da ya tsaya ba," Ji nake kamar kada in tafi ko dai zaki
shirya mu tafi can Gidan mu mu kwana tunda kin ga Gobe Sunday,in ya so sai in dawo da ke ranar
Monday early in the morning".
Zazzaro Ido waje Hibba tai kafin ta ce da shi,"Ni dai babu ruwana ,ko ka manta Kaine ka kawo ni ka ce
sai bayan na haihu zamu koma","To mene ne Dan kin je kin kwana d`aya ko biyu kin dawo Gidan ki ne fa
can inda zamu".
"Wannan ai rashin kunya ce taya ma zan iya fuskantar Mama da irin wannan Maganar kai ko Ummien
Jaheed ba zan iya tunkara da irin wannan zancen ba".
`Bata fuska yai alamun bai ji dad`in abinda ta ce ba ya ɗora da cewa," To shikenan na hak`ura tunda
haka ki ka ce ya zanyi, I don't have anything to say tunda haka Macen da nake kira da My Woman ta
za`ba min".
Sai da Hibba ta kama hannunsa ta rik`a kafin ta fara bashi hak`uri, "Bayanda zan yi ne abun na da nauyi
ne sosai fiye da yanda za kai tunani,ko ka manta we are Hausa Fulani people an sanmu da kunya fa".
Murmushin gefan baki yai kafin ya ce," one day it may kill you,this shame ba hmmmmmmmm it may
kill you,in dai zaki cigaba da biye ma wannan k`ananun abubuwan na ku".
"Hhhhhh ba abinda zai same mu, ai halayya da d`abi'u ne masu kyawun gaske".
" Raba ni da su,ba gasu a ta dalilin su ba ,za ki bar Mijin ki cikin kewa da kad`aice ba,kuma alhalin ko ke
nasan kina son Mijin ki tunda gashi na gani a idon ki".
"Lah...lah..lah ni dai ban ce ba,yaushe ma na fad`i haka?"," Kin fad`a mana ni naji da kunnuwana","Na
fad`a kuma a yaushe ?"," Kin fad`a mana","Ni dai wallahi ban fad`a ba","kin fad`a mana","A'a ban fad`a
ba".
Rau-rau tayi da idanunta ganin dagaske yake,"Kin ga I'm sorry da wasa nake maki ba ki fad`a ba ni ne
na fad`a",Sai da ta kai mashi duka kafin ta ce da shi ni ba ruwana sa kai tunda haka ka koma ",ta kai
zancen tana mai mik`ewa tsaye.
" Haba Haba ke kaman taya za ai kice baza ki yafe min ba kefa Mace ta Gari ce fa","Hmmmmmm Na
gano ka dad`in baki ko, to ba za ai hak`urin ba","Haba ni ne fa kuma ina wani laifi don Miji yayi ma
Matarsa dad`in baki ?".
"Hhhhhh shikenan naji sarkin wayo Na hak`ura mu je in raka ka kar da kayi dare"," To mu je tunda
kora na ki ke.
Sai da Hibba ta ja gefe guda kafin ta ce,"Ya Salam wai yaushe ka koma haka ni ban sani ba".
"Afuwan kar ki ce kin fasa raka ni,mu je na tuba".
Kamar ta ce da shi wani abu kuma sai ta fasa ,amma sai dai me ko da wasa ta kasa iya d`aga k`afarta
guda.
Yanayin yanda ta fara yamutsa fuskarta ne ya sa ya tambayeta,",lafiya me yake damun ki,ko kina jin
wani ciwo ne".
Kafin ka ce me tuni Zufa ta rufeta da k`yar ta iya sanar da shi abinda yake damun ta," K`afata,marata
Na kasa ita tafiya".
"Innalillahi, mai ki ke so,me zan miki, da me zan iya taimaka miki",gaba ki d`aya duk ya rud`e.
Ka kira min Ummie Maryam ko Mama kai ni ko wa ma zaka Kira ka kiramin "..
A ruɗe gami da sauri ya fito,Allah ya tai make shi ya na fitowa ya hango Ummie Maryam ta taso k`eyar
Jaheed daga wajen Mama Hadiza, tun d`azu take neman shi ya zo ya kwanta ashe yana can ya addabi
Mama Hadiza.
" Lafiya nagan ka a cikin irin wannan yanayin ","ba lafiya ba Hibba ce....Hibba ce ban dan meke damun
ta ba".
Kafin ya k`arasa magana tuni Ummie Maryam ta kai cikin d`akin,sanda zau shigo d`akin har ta kamo ta
jikinta,"Ka ga maza je ka fiddo motor Haihuwa za tai,dama tun ɗazu na kula da ita,sai faman yamutsa
fuska ta ke,amma da na tambaye ta sai ta ce min ba komi".
Ko da ya fita daburcewa yai kamar Wanda ya manta hanyar fita Gidan,inda Allah ya taimake su ,tun
kafin su je ko ina nak`udar tai tsamari bayan wani lokaci ta haihu a cikin Gida ba tare da sun je asibiti
ba,ta haifi `yarta mace,zo ka ga murna bakin mutanen Gidan,karma Muhammad Jaheed da gani yake
kamar shi kad`ai akai ma haihuwar.
Sai washe gari sannan Abbakar ya samu damar ganin Babynsa sosai da sosai, sosai ya zuba ma ta idanu
sosai yake jin sonta na k`aruwa a cikin Zuciyarsa shi har wata ajiyar Zuciya yake.
"Lafiya na ji kana ajiyar Zuciya sai ka ce wanda bai ta`ba d`aukar Baby ba "," Na ta`ba d`aukar Baby
mana amma irin wannan ce ban ta`ba d`auka ba,idan na tuna wannan `yata ce sai inji kamar ba wani
wanda ya kai ni samun kyauta mai girma ,wacce ta can-canci alfari a duniya sama da ni,Na kan k`ara
gode ma Allah game da bani wannan kyautar da yai wacce ba kowa ya ke baiwa ba".
Hibba kam ba abinda ta ke sai binshi da kallo fuskarta d`auke da murmushi,"Kin ga matso mu gani
cikin ni da ke da wa take kama".
"Hmmmm wannan d`iyar taka na rasa da wa taje kama ga dai mutum nan amma ban san da wa take
kama ba,Na ga dai hancin ta kamar irin naka ne","Uhmmm haka ne idanuwanta ta kuma irin na ki ba".
Dariya Hibba tai kafin ta tambaye shi da gaske ya ke," Da gaske na ke, k`ara kallon ta ki gani,kin gani
shape d`in sa iri d`aya ne",cikin murna Hibba ta sake zuba mata Ido kafin ta ce,"Lah wallahi haka
kuwa,to bakin ta kuma na waye ?",su duka biyun suka sura mata ido don son gano bakinta kuma irin Na
waye.
Hibba ce tai zaraf ta ce,"Irin Na Cecelia ne",sosai Abbakar ya zaro idanun sa waje tare da ambaton
Cecelia kuma? "Eh mana kalla ka gani".
" Ta`b indai haka ne kina da aiki tun wuri ki mata nasiha kar ta biyo halin Cecelia because she so
disturbant, bata jin magana ga tsiwar tsiya".
"Ai Kaine zaka ji da ita in ta tashi tsiwar ta ta"," I'm out babu ruwana a ciki","Hmmmm da ruwanka kai
ba ma ruwa ba har ma da tsakinka akwai,kasan me ?".
" A'a sai kin fad`a","Jaheed na rok`on alfamar ka bar shi ya za`ba mata suna","Wannan ai ba wani abu
ba ne ba,ya za`ba mata in ya so sai ai mata hud`uba da shi ".
" Kai amma na ji dad`i Na gode sosai ban San da wanne baki zan iya nuna maka irin yanda na ji dad`in
wannan alfamar ba, domin jiya da ya zo ya iske ana mata wanka ya ga tawada a tsakiyar babban
yatsanta na k`afarta ta dama murna yai tayi wai da shi take kama tunda shima yana da tawadar".
Dariya Abbakar yai yana mai cewa,"Kin can-canci fiye da haka a gare ni shikuma Muhammad Jaheed
wannan Babyn tashi ce,in yace ba mai ta`bata sai shi ai ta zauna,tunda na ga kusan tare da shi akai
d`awainiyar da cikinta shima ya zama babban Yaya ".
Haka dai suka cigaba hirarrakin su Wanda rabi duk akan Babyn ne da kuma shieye-shiryen ranar
sunanta .
Sosai Hibba da Babynta su ke samun kulawa daga wajen kishiyoyin Mahaifiyarta da kuma Ummie
Maryam hatta da matan yayyanta ba a barsu ba,hatta da Yayanta Nasir wanda daga shi sai ita,da ke
karatu a Kaduna sai da ya zo ganin baby.
Ranar suna Baby ta ci suna *JADEEDA*,lokacin da aka kai Babyn ayi mata askin suna ne Baba Asabe ta
bi su ta sa Wazamin yai mata tsagar Gidan ta rumanci wato eleven eleven,sanda aka dawo da ita sai
faman canyara kuka take.
"Hibba na ga Babynnan kamar anyi mata tsaga ?", Cewar Anty Na'ima Matar Yah Mustapha ta biyu.
" Tsaga kuma akan me za ai mata tsaga in ba neman fitina da tashin hankali ba,to wai wama yasa akai
mata tsagar,tsagar da tun-tuni Baba Malam ya hana ya ce haramun ce".Cewar Yayah Hanne ta na mai
tambayar Jidda da ta shigo da ita.
"Ni dai babu ruwana Baba Asabe ce ta sa ayi mata wai ai ba ta da dangin Uba gara a rufa mata asiri a yi
mata tsaga hakan zai sa a rik`a zaton ko `yar wannan ahalin ce".
"Mene!? aiko yau ba zan kyake Baba Asabe ba,don naga abun nata k`ara cigaba yake,ta ya meye
had`in ita wannan Yarinya da wata tsaga,ba fa Mahaifinta aka haifa a cikin Gidannan ba Mahaifiyarta aka
haifa fa,yanzu me ki ke tunanin zai faru idan Abbakar d`in ya gani nasan ran shi ba zai so ba".
" Kin ga Yayah Hanne dan Allah ki k`yaleta tsaga dai an riga da anyita,ba kuma zata gogu ba,ko kun
manta haka ce ta faru a lokacin da Ummie Maryam ta haifi Jaheed duk da Baba Malam ya hana tsaga sai
da ta sa akai mashi,wanne irin tashin hankali ne ba ayi ba a ranar,kawai ku barta so take bikin sunan ya
watse,kun ga ita ba ruwanta mu ke da asara da bak`in ciki, kuma dama burinta kenan ace ba a tashi
lafiya ba,in dai don tsaga ce na samu Zuma mai kyau in rik`a shafa mata har ta `bace".
"Kuma da gaskiyar ki Hibba, abinda take so kenan ayi fitina din haka k`yaleta shine mafi a'ala ban
manta yanda dangina suka tafi da `bacin rai a ranar sunan Jaheed ba kuma duk saboda ita ba", Cewar
Ummie Maryam.
" Shikenan tunda haka kuka ce amma wallahi taci bashi kuma sai ta biya shi,in ba dan Mahaifin
Yarinyarnan yana da hankali da natsuwa ba ai da bamu san ina wannan abun zai tsaya ba ".
Haka dai su ka dunga tausar Yaya Hanne har Allah ya sa aka tashi taron lafiya ba tare da wata hayaniya
ba.
Sai bayan da su Hibba su kai Arba',in sannan suka koma a lokacin tare da Muhammad Jaheed suka tafi.
*JADEEDAH*
(It's a story of two love birds who are so different from each other )
STORY & WRITTEN BY :
(*Cwt~Sumiey*)
Marubuciyar littafin
MENE NE ABIN YI ?
KARAGAR MULKI
And now.....*JADEEDAH*
https://chat.whatsapp.com/CWkZfMqvD4H0mtd7WW6Xbz
https://whatsapp.com/channel/0029VapqU8C002T5Bz8RSQ0a
BOOK 1
PAGE 11 ❤
*After one year (Bayan shekara d`aya)*
"Auntynah barka da yamma", " Oh Cecelia ashe kin farka na lak`o d`azu na ga kina barci".
"Ke dai bari Aunty gajiya ce duk ta dame ni,tunda na samu na ci abinci nayi wanka sai barci ya kwashe
ni".
" Ah ai dole akwai gajiya duk da ban ta`ba zuwa Jos ba nasan zai yi nisa daganan Kano "," Akwai nisa
kam,wai ina my daughter take ne na ga ban jin motsinta ba ?".
"Ah Jadeeda na can na samu tayi barci, kar ki so ki ji dad`in da na ji dana ga za tai barcin da ya ke ba
gwanar barcin ba ce ba abinda ta kware da shi sai rikici da `barna'',dariya Cecelia ta saki kafin ta ce," ki
ce tana saki aiki da yawa?","Ke dai bari ai Abbanta ya ce ke ta biyo rikici da kukan tsiya duk d`abi'unki
ne".
"Kai³ sharri zai min,na rantse ba behavior d`ina bane,kawai dai yana son d`ora min laifi don ganin ba
idona,inanan zai same ni bari ya dawo ".
" Kun fi kusa babu ruwana,yanzu me ki ke son a girka for the dinner ina son in sauri in d`ora kafin
Jadeeda ta farka, ko kafin Jaheed ya dawo daga School,kin san yau weekend da yadawo zai aje kayansa
ya taho nan wani time d`in ma da uniform d`insa a jikinsa yake tahowa nan, nasan ko barcin me take in
yadawo sai ya tada ta,itama da ta ji muryar sa zata farka",Oh that boy da nake jin muryarsa in muna
waya ?","Eh shi fa kar ki so kika ga yanda suka shak`u da juna".
"Ki bari yau in muku Cooking,ki huta tunda ga k`anwar ki ta zo"," Ina wace ni ai haka ba zai yiwu ba
daga zuwan ki sai in bar ki da kitchen, just mention what you need to eat yanzu za ki gan shi a gaban
ki","Seriously ki bar ni in mana abinci I'm a good cooker za ki ji dad`in girki na","Na sani mana amma ki
bari letter on kin yi mana amma banda yau "," To shikenan I'm give off tunda kin ce haka amma
tomorrow ni zanyi,but duk da haka I need to join you,zan bi ki kitchen ɗin"," Ba damuwa Allah ya kai mu
goben,amma promise me ba abinda za ki ko da munje kitchen d`in tare".
Dariya Cecelia ta saki batare da ta d`auki alk`awarin ba kamar yanda Hibba ta ce, "Au ki ce baki shirya
bina kitchen ba,yauwa kin ga Abban Hibba ya ce in tambaye ki ko da akwai wani abun da ki ke son siye
anan Garin Kanon sai muje kasuwa mu siya ya bada kud`i yace ai amfanin da su".
" No.. No...no I don't need anything, ya riga da ya bani a lot money na yi amfanin da su,kawai dai na zo
ne inyi maku ban kwana ".
" Mun ji dad`i sosai kuma mun gode da wannan karamcin da ki kai mana,Na jima yana cewa mai yiwa
tare da ke za mu wuce can Jos d`in har a gama taron bikin".
Ba k`aramin mamaki Cecelia ta yi ba jin wai tare da ita za su tafi,cikin