Author : Cwt Sumiey Category : African Stories & Novels
yawa suna fahimtar addini daban-daban, suna ƙirƙirar tafsiri bisa son rai ko ra’ayoyi na wata
ƙungiya.
Hakan yana iya haifar da:
Ƙiyayya tsakanin mazhabobi ko sekto-sekto
Rarrabuwar kawuna
Tashin hankali da yaɗuwar ƙarya bisa sunan addini
2. Tasirin Tsattsauran Ra’ayi (Extremism & Fanaticism)
Wasu suna amfani da addini wajen:
Wuce gona da iri (radicalization)
Kisa ko tashin hankali bisa sunan jihadi, crusade ko tsarkakewa
Wannan yana bata sunan addini, duk da cewa mafi yawan mabiya su masu salama ne.
3. Amfani da Addini don Fa’idar Kai (Manipulation)
Wasu shugabannin addini na amfani da matsayinsu wajen:
Wawashe dukiyar mabiyansu
Yaudarar mutane da annabtar ƙarya
Wuce iyaka wajen karɓar sadaka ko kuɗaɗe
Wannan yana sa mutane su rasa amana da gaskiya a cikin addini.
4. Raguwa ko Fita Daga Addini (Secularism & Atheism)
A wasu ƙasashe, musamman masu tasowa, mutane da yawa:
Suna watsi da addini baki ɗaya
Suna komawa “Free thinkers” ko “Spiritual but not religious”
Saboda:
Ƙin amincewa da shugabannin addini
Son rayuwa mai 'yanci ba tare da ƙuntatawa ba
Wani lokaci rashin iya amsa tambayoyin zamani cikin hikim
5. Sabanin Addini da Kimiyya
Akwai tangarda tsakanin addini da kimiyya, musamman a batutuwa kamar:
Halittar mutum (evolution vs. creation)
Magungunan zamani da tsarin haihuwa
Fasahar jikin mutum (organ donation, cloning, IVF)
Hakan yana hana yarda da cigaban zamani a wasu addinai ko ke jawo matsaloli tsakanin matasa da
dattawa.
6. Matsin Lamba daga Zamani (Modernization & Globalization)
Rayuwar zamani tana ƙalubalantar:
Tsare-tsaren ibada
Shari’ar aure, gado, tafiyar da iyali
Kyakkyawan ƙyale-ƙyale da kyawawan ɗabi’u
A wasu lokuta, addini yana fuskantar koma baya ko barazana daga kafofin watsa labarai da al’adu na
kasashen waje.
7. Hadin Gwiwa da Siyasa (Religious Politics)
A wasu kasashe, ana amfani da addini wajen yaɗa siyasa ko mulkin zalunci
Idan gwamnati ta yi kuskure cikin addini, to mutane sukan ɗora laifi ga addinin
Ko kuma idan wata ƙabila ta ƙwace addini, hakan na iya sa sauran ƙabilu su ƙi bin shi
8. Rigima Tsakanin Addinai (Inter-religious Conflict)
Rikice-rikicen da ke tasowa saboda:
Tashin hankali tsakanin mabiya addinai daban
Ƙiyayya da zargi tsakanin musulmi da kirista, hindu da muslims, da sauransu
Rashin zaman lafiya da rashin haɗin kai Taƙaitawa:
Addini yana da matuƙar amfani, amma yana fuskantar matsaloli kamar:
Rashin fahimta
Tsattsauran ra’ayi
Kiyayya da siyasa
Barazana daga kimiyya da zamani
Haka dai taron na su ya cigaba da tafiya cikin natsuwa,. Da ya zo ƙarin fashin baƙi yayi gane da dogon
sharhuna Imam Jaheed yai inda ya ɗauki ɓangaren,Siyasa a Addinin Musulunci,inda yai bayani game
muhimmanci da hakan yake jawowa da kuma ,rashin fahimtar da ke ciki da kuma tashe-tashen hankalin
da hakan kan haifar,sosai taron ya faɗakantar ya wayar ma da mutane da kai game da abinda ya shige
masu duhu,daganan bayan a tashi Jaheed luggage ɗin sa yai parking ya taho gida Kano ,inda Allah ya
taimake shi by 8pm ya na Gida.
√√√√√√√√√√√√√√
Sosai ran Jaheed ya ɓaci sakamakon samun labarin tun tafiyar sa Ummu Nurain ta bar Gida,haka ba dan
ya so ba ya nufi Part ɗin shi ya watsa ruwa gami da haɗa ma kan shi shayin Coffee ya sha,ya dan
kishingiɗa saboda a matuƙar gajiye ya ke inda ma Allah ya taimake shi ya gama sauke duk wani Nauyi na
Sallah a kanshi.
Motsin da ya ji ne ya sa ya ɗan waigo don don ganin waye ke tafe,cikin zazzaƙar muryarta mai ɗauke
da ladabi da kwantar da kai wacce ke sanya natsuwa ga mai sauraro ta yi masa sallama,bayan ya amsa
ne ya ce da ita,"Ba dai girki ki kai min a cikin wannan daren ba ?","To ya zan yi ba dole na na shiga
kitchen ba don ka san ba zan iya barin ka kwana ba tare da ka ci wani abun ba,wa ma yasan yaushe
rabon ka daka ci wani abinci mai gina jiki",Duk Gimbiya Ayush na wannan zancen ne ta na haɗa masa
lafiyayyen girkin da ta haɗo masa.
"Allah ya yi maki albarka,na ji daɗin hakan da ki ka aikata,har ban san da wanne baki zan iya bayyanar
da hakan gare ki ba".
"Kar ka wani wahalar min da kan ka iya wannan farin cikin da kuma albarka daka samun sun
wadatar,bari in je Gimbiya Fadeela na jirana kadan tun zan dawo mu ka taho tare,ka santa ƴar daru
ce,ganin wai ka dawo shine ta ke son tafiya","A'a kar ki barta dare ya yi zauna har sai zuwa Gobe da safe
in Allah yakaimu in ya so sai ta tafin","Ni ma haka na ce mata amma taƙi,wata ƙila yanzu da kai ka sa
baki za ta haƙura,bari in je Ina dawowa".
"Amma da fatan dai kin fasa tafiyar?","Eh ya zanyi na kira Fulani na sanar da ita amma ta ce in bari sai
zuwa Goben".
"Hausa na ji daɗin haka to ta zamu yi da maganar zuwa Hospital ɗin,domin wallahi juriya ta ta fara
ƙarewa,domin ina jin jiki akan haka","Aunty Gimbiya laifin ki ne tun ranar da ki ka zo Fada na ce maki
washegari ki shirya mu tafi ki ka ce a'a,a bari sai lokaci kaza, to gashinan yanzu ya dawo ni kuma ban san
ya za ai ba kuma".
"Duk yanda zan yi zan yi domin in samu in fito cikin week ɗin nan in ya so da na samu damar haka sai
in kira ki,amma kafinnan wanne Hospital ne ki ke ganin ya kamata muje inda ba zamu haɗu da idon sani
ba ?",haka suka cigaba da hirarrakin su da yanda zasu tsara fitar ta su.
"Anya kuwa Nabila ki na da zuciya a cikin ƙirjin ki,ki tafi ki bar Gida tun kafin faɗuwar rana amma sai
yanzu za ki dawo,kina can kina yawan gal-gal ɗin ki,babban abun takaici da baƙin ciki ki rasa wurin
wanda za ki sai wurin waɗanda su ke son ganin bayan Ahalin ki, wallahi kin ɓata wayon ki"...."A'a ni
wallahi ki dai na danganta mi da mai gantali,ai gara ni ba da auren wani a kaina na ke yawo ba,wata
kuwa tana nan zaune Mijinta ya yi doguwar tafiya ya dawo ma ba tare da ta sani ba".......zumbur Ummu
Nurain ta miƙa,tare da cewa"Ke Nabila shin da gaske ki ke Abu Nurain ya dawo,ko dai tsokana ta ki ke,zo
kiyimin bayani yadda zan fahimta,"A kan me ki je ki bincika", Nabila ta faɗa ta na mai shigewa cikin ɗakin
don rage kayan jikinta.
Wata tsohuwar Hijabi ta Baba Asabe da ke sagale akan ƙofar ɗakin Ummu Nurain ta janyo ta na mai
sanya ta a bai-bai ba tare da ta damu da hakan ba,kai tsaye ta nufi ɗakin Mamasu tana mai cewa da
ita,"Mama dan Allah akwai ɗari biyar a hannun ki ki ba mi","Ɗari biyar kuma Zeenatu mai za ki da kuɗi a
cikin wannan daren,kuma ina zaki na gan ki sanye da Hijabi?".
"Mama Nabila ce ta dawo daga Gidan Baba Malam ta ke ce min Abu Nurain ya dawo shine zan koma
Gidana","Au au har kin huce ba zaki bari har ya gane kuren shi ya zo ya baki haƙuri ba?","A'a Mama
gaskiya ba zan iya zauna wa a Gida in bar Mijina shi kaɗai ba,da dai ace ba Gimbiya Ayush to da shi ne fa
zan iya zaunawa","Hmmmmm ke dai ki ka sani amma kar ki manta duk yanda za ki ki tabbatar da kin
rama cin amanar dasu kayi ma ki,amshi maza je ki ki samu ko mai adai-daita sahu ne ya kai ki,amma fa
kar ki bi hanyar da ki ka son za ki haɗu da Babanki","To Mama na gode sosai shiyasa na ke ƙara son ki",
Ummu Nurain ta faɗa ta na mai amsar kuɗin ta fita, Allah ya taimake ta bata wani ɓata lokaci ba,ta samu
abun hawa sanda za ta isa gida wajen tara da kwata,haka ta shiga Gidan sai faman baza sauri ta ke,kai
tsaye ya nufi Part ɗin sa ta na mai fatan Allah ya sa yana ciki.
"Abu Nurain barka da dawowa ya hanyar fatan ka dawo lafiya",shine abinda Ummu Nurain ta fara
cewa bayan ta gama bubbuga ƙafafuwan sa a matsayin hanyar ta da shi daga barcin da ya kwashe
shi,gefen kan shi kawai ya iya dafewa da ya ke jin ƙaruwar bugawar shi fiye da asalin yanda ya kwanta .
"Zeenat meye haka dan Allah,daga ina ma ki ke daga cikin dare nan",sai da Zeenat ta Turo bakinta
gaba kafin ta ce,"Na samu labarin ka dawo ne shiyasa ni ma na dawo".
Gyara zama Jaheed yai kafin ya ce da ita,"Yanzu dan Allah baki ji kunya ba ki sa ƙafa ki bar cikin Gidan
Auren ki na sunan ba tare da sanin Mijin ki ba,shin mi ye ribar da ki ka samu daki ka aikata hakan,me
zaman Gidan ya amfanar da ke?".
"Au laifina ma ka ke gani kenan,ba ka ga irin cin fuskar da ka aikata min ba,ka ɗauki Matarka ka tafi da
ita ba tare da sani na ba,shiyasa mi ma nai tafiya ta Gidan mu na bari in ka dawo sai in dawo","Oh really
tunda dama Auren kin ɗauke shi abun wasa ko,to fita ki bani wuri","Haba Abu Nurain kamar fa korata ka
ke,na dawo fa domin ka ne,dan Allah kayi haƙuri,bari in samu wani abu mai ɗan sauƙi in dafa maka na
san kana jin yunwa,ko Kanada wani abun daka keson ci dai in girka ma ka".....ya katse ta yanami komawa
ya kwantawa,",Kar ma ki wani wahalar da kan ki domin ba na jin yunwa a ƙoshe na ke","Kamar ya a
ƙoshe ka ke,me hakan ke nufi?","Wadda tasan daraja da ƙimata ta dafa min na ci,ta hutashshe ki,don
haka sai ki tafi ki kwanta ki huta domin na ga alamar ki na buƙatar haka".
Wani kuka ne ya kwace mata har sai da ya ba Jaheed mamaki ya tashi zaune ya na kallonta,,"Allah ba
inda zani ina nan", "Me ye haka baki san dare ya yi ba ne ba?","Dare kuma ni wannan bai dame ni
ba,kawai in ji dalilin da ya sa ka ci abincinta na ke son ji ","Au so kuke in zauna har kawo yanzu ba tare da
na ci abincin ba ko in ya so yunwar tai min duk illar da za ta min baki da asara da hakan ko,kin ga dan
Allah in har kin san tada min hankali ki ke son yi,ga hanya nan ki fita min a ɗaki ki tafi na ki ɗakin","Allah
Abu Nurain ba inda zani sai na ji dalili",ta faɗa muryarta na ta tabbatar da hakan.
"Na ce maki in har tashin hankali ki ke nema ki fitar min a ɗaki,na gaji ina buƙatar in huta kusan kwana
uku bana samun wadataccan barci,ki bar Ni in huta",ko motsi Ummu Nurain bata yi ba balle ya sa ran ta
ji abinda ya ce ba.
Ganin da gaske ta ke ne yasa ya sauko da kan shi ya ja hannunta tafiyar da ita da ga cikin yana jan ta
tana turjewa,har ya samu ya fitar da ita ya rufe ƙofar haka ta naji ta na gani tai ta faman knocking amma
ya shareta,dole ba dan ta so ba ta nufi na ta Part da ya ga yi ƙura,ba tare da ta kakkaɓe ƙurar wurin
kwanciyar ta ta ba.
Page 36
"Hello Anesa akwai matsala wallahi na kasa jure yanayin da na ke ji ajikina,kullum ni ce cikin kasala,amai
ga yawan ganin jiri dole akwai wani abun da ya ke faruwa","Subahanallahi ko dai maganin bai yi aiki ba
neba Gimbiya ?",ta faɗa daga can ɓangaren
"Ah haba Anesa sai dai wata matsalar amma ba wannan ba,ban fa taɓa bleeding kamar yanda ya faru
a wannan abortion ɗin da na yi ba,na gaji da irin pretending ɗin da nake a duk lokacin da na ke tare da
shi,ina tsoran kar ya fuskanci hakan".
"To zai fi kyau ki koma ki ga Doctor tun kafin ki yi ma kan ki sagegeduwa","Anesa ba za ki gane ba ba
lalle ya bar ni in fita a cikin waɗannan kwanakin ba,da zaran na gaya ma shi ina da buƙatar zuwa wani
guri ɗayan biyu ce zata kasance ko dai ya kai ni da kan sa ko kuma ya sa cikin jerin ƙannan sa wani ya kai
ni kin ga kenan ba a mutuba an karya wuya".
"Kar ki bani kunya mana Gimbiya sai ka ce ba Mace ba,wai ko dai an sauya ki ne daga asalin Gimbiya
Ayush ɗin dana sani ne, tambayar unguwa ya gagare ki,kin tsaya sai faman rayuwa da ciwo ki ke,to ki
tsaya kar ki nemi dabarar da zaki amfani da ita,har kwaɗo yai miki ƙafa,ko ƴar irin ƙaryarnan ta Matan
Aure da ɗan planing ɗin da su ke haɗawa ba za ki yi ki samu ki cimma burin ki ba,to ki zauna har abun ya
zo ya fi ƙarfin kan ki".
"Anesa ni da na kira ki domin ki bani shawara kuma ki jajanta min akan halin da na ke ciki sai kuma ki
ɓige da gaggayamin maganganu"....."Allah ya huci zuciyar ki Ran ki ya daɗe ni ba haka na ke nufi
ba,kawai dai ina son in nusar da ke kuskuren da ki ke son aikatawa kan ki da kan ki,amma yanzu duk ba
wannan ba,yana Gida ko bayanan?","Ba ya nan, Uncle ɗin shi ya kira shi zasu yi wata tattauna akan
kasuwanci su","To maza ɗau Car key ɗin ki da mayafin ki ki kama hanya ki tafi sai kin yi nisa sannan ki
tura masa text ki ce da shi,wani uzuri mai girma ya ta so maki kin fita inkin dawo za ki yi masa bayani","Ki
na ganin in na yi hakan ba abinda zai faru ?","In sha Allah ba abinda zai faru idan ki dawo ki Kirani ina
jiran ki",jiki a sanyaye Gimbiya Ayush ta aje wayar hannunta zuciyarta na kai kawo gami da aikata abinda
zai fishshe da rayuwar ta.
"Kai tafiya zan yi,hankali na ba zai kwanta ba ina son in san halin da na ke a ciki,ko ma me zai faru na
ji da shi daga baya, shawarar Anesa ita ce abun ɗauka bari ki gani",ta na kaiwa nan ta zari mayafin ta
fita,sai da ta tabbatar da ta yi nesa da Gida kafin ta fidda wayar ta,ta fara kiran Fadeela,",Hello Fadeela
kina Hospital ɗin ne ?","Eh Gimbiya ina fatan dai lafiya dai ko","Eh da sauƙin dai gani nan zuwa in na zo
zaki ji komi",ta na kaiwa nan ta maida hankalin ta wajen ta tura masa text kamar haka,"Habibi I'm so
sorry,na fita ba tare da izinin ka ba,wani lamari ne mai girma ya taso min da zaran na dawo zan yi maka
bayani yanda za ka fahince ni, Allah ya tsare min kai sannan ina maka fatan nasara game da abinda aka
fita nema" ,tana kaiwa nan ta kashe wayar gami da saita hancin Motar ta zuwa hanyar da za ta kai kanta
Hospital ɗin da Fadeela ke aiki".
Ko da isarta ba su wani ɓata lokaci ba ta shiga aka fara yi mata a scanning ɗin,gami da sauran tests ɗin
da zasu ƙara tabbatar da abinda ke damun ta,wanda su ne suka ɗan ɗau lokaci kafin fitowar su ,Office
ɗin Fadeela ta koma ta samu wuri ta kwanta dan kwata-kwata ba ta jin ƙarfin jikinta ko kaɗan,sai da ta
huta dan kanta sannan ta tashi,"Wai Fadeela har yanzu sakamakon scanning ɗin bai fito ba ?","A'a Aunty
Gimbiya tun ɗazu aka kawo kawai na ga kina buƙatar hutu shiyasa ban barki ki ɗan samu hutu","Okay
to mene ne sakamakon result ɗin ?","Ban buɗe ba na bari sai kin farka",Buɗe mana don mi na ƙagara in
san me ke damu na,idan cutar da zan iya rabuwa da ita ce,in rabu da ita in huta",ta faɗi hakan ta na mai
gyara zaman ta akan kujerar da take zaune a kai.
A ɗan firgice Fadeela ta kalleta bakin ta na motsi amma ta kasa iya haɗa harafin da zata yi mata
bayani da shi,kasa ce mata komi tai sai faman jujjuya papers ɗin hannunta ta ke,har dai Gimbiya Ayush
ɗin ta gaji ta ce da ita,"Lafiya na ga kin tsare ni da idanuwa sai motsa baki ki ke ba tare da kin ce da ni
komi ba ?","Gimbiya..... sakamakon ne ya zo ta fuskar da ba muyi zato ba","Kamar ya wata muguwar
cutar ce na ke ɗauke da ita ?","A'a ba wata cutar da ki ke da ita,kawai dai You are still pregnant,cikin jikin
ki yananan bai faɗi ba"....."What...Amma dai tsokana ta ki ke ko?",a kiɗime Gimbiya Ayush ta miƙe
tsaye tare da cigaba da cewa,"Haba Fadeela wannan wanne irin wasa ne,a gaban ki fa komi ya
wakana,ke shaida ce akan irin wahalar da na sha sai kuma ki zomin da irin wannan sankaran zancen".
"Wallahi Aunty Gimbiya ba tsokanar ki na ke ba, wannan shine gaskiyar scanning da kuma duk wani
test da akai maki ,cikin jikin ki bai fita ba,hasalim sai komawa baya da kwanakin da ya yi,"You are
pregnant,gaskiya ne hakan kina ɗauke da ciki na tsawon wata biyu da ƴan kwana ki","Innalillahi wa'ina
ilaihir raju'una wannan wacce irin masifa ce",shine abinda Gimbiya Ayush ta iya faɗa kenan ta na mai
komawa ta zauna akan kujerar da ta tashi.
"Kin ga Aunty Gimbiya ki kwantar da hankalin ki, wannan tamkar izina ce aka nuna miki ki natsu ki ki
yi ma kan ki faɗa da kan ki,ki ɗau ƙaddara ki, ki haifi abinda ke cikin ki,kamar hakan shine ya fi dacewa da
ke,wani na can da dukiya ya ke neman irin wannan kyautar da Allah ya baki amma bai samu ba,sai ke da
Allah ya zaɓa ya baki ba tare da kin wahala ba,mai zai sa ki wofintar da wannan kyautar, wallahi hakan
kuskure ne,gabaɗaya ba ki da wani dalili da zai sa ki ce ba ki son ki haifi abinda ke cikin ki,in ba tsantsar
nuna rashin godiya da kuma rashin tunani mai kyau ba"....
"Kin ga Fadeelah ki dakata da wannan dogon bayanin na ki,domin maganar gaskiya ba zan iya barin
Cikinnan a jikina ba,ban shirya haihuwa yanzu ba","Hmmmm Aunty Gimbiya ai ba ke ke da wannan ikon
ba,tunda har ki kai kuskuren samun cikin ki bari ki haife shi mana,in ya so sai ki ɗauki duk matakin da za
ki ɗauka mana a gaba"....
" Ki dakatar da wannan batun da ki ke domin ko kusa ko kaɗan ba za su sami muhalli a cikin Zuciyata
ba,tambaya ɗaya zan yi maki za ki taimaka min in fidda cikin nan ko a'a,shin kina tare da ni za ki tsaya a
bayana ko ya ya?".
"Ko kusa ko da wasa babu hannu na a cikin wannan lamarin,sai dai ina so ki sani ba zan daina faɗa
maku gaskiya ba kina kan ƙadamin da za ki aikata babban kuskure wanda ba ki san me zai iya haifar mi ki
anan gaba ba,kina ikirarin ki na son Mijinki sai dai kalaman ki da duk abinda