Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Wata Kishiyar Complete Hausa Novel by Maryamah Mrs AM

Author :  Maryamah Mrs AM Category :  Drama

Chapter   44 / 80

129K to 132K   out of 238.5K words

bazan iya ba. Haka kawai sena zauna kenan na
zuba ido se yanda akayi dani ai kuwa bazan iya ba ni indai wannan shine dabarar
gara ma nabi ta Addahn kenan a nemi inda za’a kaishi a mallake mun shi ta qarfi
amma indai se na zamar masa jaka babu ni a wannan tsarin” Amirah ta fada.

“Ai kuwa indai kina so ki samu yanda kike so a gurin namiji yanzu dayan biyu ne,
kodai ki zama kurma makauniya ki sakar masa ragama duk abinda yayi daidai ne bazaki
musa masa ba ko kuma ace ke kike wahalta masa da aljihunki to shine zaku zauna
lafiya ba tareda an ji kanku ba.
Dan muddin kika ce in ya bada umarni zaki kawo taki shawarar to kuwa kun ringa
samun sabani kenan. A cikin Maza yanzu kadan ne suka fita zakka da zaki ga sun bawa
matansu haqqin da ya kamace su,

Idan kuma yawon Malaman kikaga yafi miki seki daura aniya, ki dai sani wata rana
zanin da zaki daura ma se ya gagare ki tunda kullum kina kan hanyar kaiwa wasu daga
zaune kudin ki kuma shi Asiri ko kinyi se kin hada da kissa wallahi randa kuma ya
karye se kin fi kare wulaqanta”.

Shiru Amirah tayi dan gaskiya Sa’adah ta fada, yanzu dai gashi tun yaushe suke
yawon rabar da kudin daga can inuwar su tsugunna a waccen amma babu biyan buqata,
gashi yanzu cikin lumana komai yana tafiya yanda take so to amma kuma ita ai bata
zaci haka zaman ze kasance ba.

Cikin sanyin murya tace “Toh yanzu Anty Sa’adah ya zanyi dan gaskiya akwai matsala”

“Yawwa yanzu kika dawo kan hanya” Sa’adah ta fada kafin ta ci gaba da cewa

“Kina ji ko, batun gyaran gida wannan daman ai aiki ne dukda ban san Kishiyar ki ba
amma a yanda kuka bani labarinta mace ce data san kanta dan haka yanzu dole ki dage
idan baki zarta ta ba toh kuyi kan kan kan.

Tsafta dole ki dage gyaran gida ko ina yayi qal ki saka turare Allah na tuba ma
wane aiki ne a gyaran gidan keda ba wani wawakeken Mansion ne dake ba dan Duplex ne
fa, sharar palour, Kitchen da mopping dinsu dai wannan dole kullum kiyi.

Haka dakinsa, da kun tashi bacci ki gyara gado, yana shiryawa ya fita ki share ki
wanko bandaki kija qofar shikenan fa se kuma gobe. Naki dakin zaki iya ki ringa
tsallaken kwanaki tunda ke kadai ce babu me shigar kiki, kwanuka idan kina girki
daga kin bata ki wanke idan anci abinci ma ana gamawa ki wanke, dan girki dai cin
mutum biyu da safe ne fa se na dare ba shikenan ba duk meye abin wahala a ciki dan
Allah.

Sannan ki ringa wanka dan Allah sau biyu dai a rana meye a ciki kayan kwalliyar nan
gasu nan kina dasu kar kije ki ringa zama yanda kike a nan kamar wata me takaba da
zani da T shirt dan dole ki dauke masa hankali daga kan kowacce mace ta yanda ze
manta da tsohuwar matar sa ya shafeta daga lissafinsa tunda yana da ke sabon jini”.

“Toh ai Anty Sa’adah katangar mu daya fa da gidan data koma ga yaran tun jiya na
gaya miki suke zuruftu a gidan nan ko tunawa dani ma bayayi” Amirah ta sake fada,
se Sa’adah ta danyi murmushi tace

“Dadina dake komai se an koya miki, yo Allah na tuba ko a cikin gidan ku take idan
kinsan yanda zaki riqe shi tsaf ai wallahi bata ishe shi kallo ba, yara kuma da
dabara zaki janye su, daman karki basu qofar da zasu ringa shigo miki idan baya
nan.

In kuma yana gidan sukazo kar kiji kunya ko a gabansu ne kije jikinsa ko kiyita yin
abinda zaki ja hankalin sa dakansa ze ce su tashi su tafi, yana dawowa gida ki saka
abinki a daki yanda baze ma samu kansa ba bare ya gayyato miki su a hankali se kiga
shi dasu se in ya fita sun hadu ne ma ze ringa tunawa da zaman su, ke dai kiyi
komai yanda ya kamata zaki sha mamaki wallahi”.

Haka ta ringa yi mata huduna data tsiya data kirki sukayi sallama. Da yake dai
quiya a jininta take kayan dai gasu nan haka ta shirya masa dan ma ya sake kaiwa an
goge dan haka zuba su kawai tayi. Tana cikin jera masa Suits ya shigo dakin,

“Har kin gama kenan” ya fada yana kallon ta hannun ta wadda kuma ita ce ta qarshe
da zata rataye. Seda tayi fari da ido ta lankwashe murya kafin tace

“Na gama fa, duk na gaji wallahi hannuna ya qage kayanka yawa Yaya kamar na mace”.

“Koh?” Ya fada yana wuceta ya bude bangaren da ake zuba masa manyan kaya, Amirah
kuwa kumbura baki tayi, a ranta tace

“Ba sannu ba komai ze ce mun wani Ayya, Aa Ayyo mutum dai besan gwaninta ba.” Baya
ida tunanin ba taji shi cikin fada fada yana cewa

“Meye wannan kikayi? Haka ake jera kaya daman ji yanda kika loda su se kace wani
motar kasuwa, malama sauke su tas ki gyara komai da kika gani irinsa daban zaki
jera.
Shaddoji daban kuma kalolin su zaki duba kiyi su a jere sannan dayaj side din ki
saka yadi ka, nan gurin Neck tie ake ajiyewa kin wani cusa mun hula baga inda suke
can ba

Mtsw komai ke baki iya ba se kinyi wa mutane shirme, kina tsaye ki fara sauke su
yanzu ki gyara” ya qarasa da daka mata tsawa.

Amirah da tayi mutuwar tsaye, yanzu duk wannan uban aikin data sha ze ce basuyi ba
seta sake aikuwa bazata iya ba, haka kawai me ya hana shi yayi da kansa tunda ba
haka akeyi ba, tsawar daya daka mata ya saka ta fara sauko da kayan ba shiri, haka
tana ji tana gani da hawayenta da komai seda ta mayar dasu tsaf yana tsaye akanta
sannan ya saka ta share dakin ta goge qal ta kuma wanke toilet kafin ya rabu da
ita. Tana gamawa kuwa ta wuce tsohon dakin Ma’u inda ya saka mata sabon Gado ta
ringa rusa kuka.

Indai kuwa haka zaman Lagos din yake kuwa wallahi bazata iya ba sedai ya maida ita
can Gombe ya zauna shi kadai, ta zata da ta ke kukan ma ze bata haquri amma se gani
tayi yaja Laptop ya kunna ma ya shiga aikinsa haka data gama ba godi bare na gode
ta wuce tana kuka be tankata ba qarshe ma se jin tashin motar sa tayi alamar fita
ma yayi.

ASMA’U

Se bayan La’asar yaran suka shigo da ledoji niqi niqi na kayan da suka siyo. Kallo
daya nayi musu gaba daya suka shiga nutsuwarsu, karadin da suka fara na bawa su
Faridah labari kowa ya kama kansa.

“Wallahi Jafar na sake ganin qafarka ka jasu kunje gidan can sena saba maka, idan
banda shegen kwadayi me zakuci da bamu dashi a nan, ina shekaran jiya da kuka Raka
Yaya Airport seda ya fara kaiku kuka siyi kayan kwalamar duk ba gasu can kun cika
mun Fridge da tarkace ba ko kuwa wani sabo kuke so da ni baza ku gayamun ba wa ma
kuka tambaya da kuka dibi qafa kuka tafi har wani guri” Na fada ina tsare su da
ido, duk sukayi shiru Yan Biyu har sun fara yar kwalla ganin ina musu fada kuma na
daure fuska, Jafar ne ya marairaice yace

“Mami kiyi haquri dan Allah bazamu sake ba, na zata ai tunda Abbi ne bazakiyi fada
ba kuma shi yace muje bamu muka roqe shi ba ko Abdallah?” Se Abdallan ya yi saurin
daga kai yana cewa

“Seda ma mukace mu baza muje ba Anty Amirah tace se munje Allah kuwa ki ma tambayi
Abbin kiji”

“Naji, karku sake” na fada har sannan fuskata a hade. Ni ba fitarsu da Bashir ce ta
bata mun rai ba akan me Amirah zata fitar mun da yara shine haushi na.

Waiwaya wa nayi na gansu har sannan a tsaye nace “me kukeyi kuka kun tsaya mun aka,
kuje ku ajiye mana idan kuma ci zakuyi to se ku zauna”.

“Toh Mami ai baki ce kin haqura ba tukunna” Jafar ya sake fada, se nace masa

“Na haqura mana Jafar, ku wuce ciki”
“To Mami ai baki saki fuskar ki ba, kuma gashi har wannan Shawarman da kike so na
siyo miki, naje na dumama miki a microwave?” Ya sake fada yana marairaice fuska,
nasan nacin Jafar yanzu idan ban saki fuskar ba se ya kai dare anan yana mun magiya
dan haka nayi murmushi nace

“Je kayi toh” da sauri suka wuce Kitchen da kayan, haka badan raina yaso ba naci
Shawarmar da aka siya da kudin Bashir, tare muka qarasa wunin mu dan sallar Magriba
da Isha ma a gida sukayi saboda ruwan sama daya sakko.

Washe gari ma muna gida har yamma se bayan da akayi sallar La’asar suka fita qofar
gida suka raba ball. Ina zaune akan kujera ina jin Dramar Amna da Farida akan
kwalliya ala dole ita Farida wai tafi Amna sanin Fashion tana zabarwa Amnan kayan
da zata saka na prom din su ita kuma tace basuyi mata ba.

Wayar Faridah ta miqo mun tana cewa “Kalli fa Mami dan Allah ai wannan ne zeyi mata
kyau ko, itafa Yah Amna bata san me ake yayi ba”

“Aike kin sani naga alama” na fada ina karbar wayar daga hannunta, shigowar da
Abdallah yayi da gudu ce ta sakani dagowa daga kallon wayar nace

“Kai kuma menene haka, bana hana ku wannan guje gujen ba se kaje ka fadi ko”. A
gaba na ya tsaya yana haki yace

“Mami Abbine, gashi can a qofar gida wai se mun dakko kayan mu mukoma can gidan, ga
Baba can ya tsayar dashi suna magana”.

Ina shirin bashi amsa Anty tayi sallama ta shigo daga tsaye take cemun

“Asma’u Bashir ne, gashi can yana rantse rantsen se yara sun koma hannunsa, dan
Allah karki tsaya tashin hankali dashi, idan dai ya kafe ki barshi nan da can din
ai duk guri daya ne”.

Miqewa nayi nima har ina fatali da wayar Amna ban lura ba nace “Bazan bashi yarana
ba Anty, Be auri matar da zan barwa tarbiyyar yarana ba kuma ko mutuwa nayi badai
dangin Bashir su riqe mun yara ba wallahi”.

Daga waje nake jiyo maganarsa yana gayawa yaran su shiga su dakko kayansu, zan fita
Anty ta ruqoni tana cewa

“Karki fita, kijira idan ya shigo da kansa se kuyi magana kuma ni banga abin tashin
hankali ba akan yara dai bayan kuna guri daya a zaune”.

Yaran ne suka shigo Aliyu akan Gaba suka wuce can ciki suka tsatstsaya sega Bashir
a bayan su yana jaddada musu dasu hada kayan su su wuce gida.

“Harke zaki hana mun yara shiga gidan ubansu ko, toh dake da itan duk zan nuna muku
baku isa ba, zan dauke yarana ita kuma dole ta riqe su tunda gidaj ubansu ne bana
uban wani ba” ya fada yana kallona, daman jira nake yi dan haka nima a fusace nace

“Seka gorantawa wanda ubansa bashi da gida, Ÿaya kuma tunda ba wani ya haifar mun
su ba banga wanda ze dauke su ba, ita kanta matar taka bata wadatu da tarbiyya
balle na a bata kula da wasu”.

“Kar ki zageni Ma’u, Ÿaya kuma nawane halak malak ke din yar karere ce dan haka
dole su koma gidan ubansu yanzu kuma ba da bata lokaci ba”.

Zan sake magana Baba ya dakatar dani da cewa
“Wai me kukeyi haka yanzu daga ke harshi kenan baza’ace ku bar abu ku bari ba kunzo
gaban yara kuna irin wannan abun me kuke koya musu kenan?

Kai Bashir ka wuce muje, ke kuma Asma’u ku hada musu kayan ku tura masa Ÿayansa
tunda yana da mata daman ai haqqin ruqonsu a hannunsa yake”.

Kuka na fashe dashi ina cewa “Akan me ya sake ni sannan yace ze raba ni da yarana
wannan ai rashin Adalci ne”.

Wayata na dauka na shiga kiran Alhaji Qarami, kira biyu na masa be dauka ba dan
haka na juya akalar kiran zuwa Goggo. Tunda yanzu tana goyon bayana gara na gaya
mata ko zan samu wanda ze tsaya mun dan gaskiya bazan bawa Bashir yara ba sedai ayi
duk yanda za’ayi.

Tana daga wayar na fasa mata kuka ina gaya mata yanda akayi, seda ta gama jina tsaf
kafin tace

“Toh Ma’u Menene a ciki tunda yana da yanda ze riqe yaransa se ki bashi, kin fiya
son damun kanki wallahi ke kanki ai sauqi kika samu seki nutsu idan an kwana biyu
ki nemi wani mijin kiyi aure dan kinsan zaman ki haka baze yuwu ba tunda yayyenki
sun daure miki gindin ki zauna a can to ki bashi yaransa ki raka su da Addu’a, a ko
ina suke Allah ya tayaki tarbiyyantar dasu”.

Kashe wayar nayi dan na manta ma Goggo duk abinda ya tashi ai bayansa take bi, ina
shawarar kiran Alhajin su Bashir din kiran Alhaji Qarami ya shigo.

“Asma’u ki tattara su daga kan Aliyu har zuwa Tukur ki bashi yaransa, bana son wata
doguwar magana ki rabu dashi. Yara ko bangwan duniya ya kaisu dole wata rana se sun
nemeki da kansu dan haka dan Allah karki tayar da hankalin ki ki tayar da na wasu,
mun gaji da Bashir Bashir kullum babu fashi.

Bafa akanki aka fara sakin Mace ace ta bada yara ba dan haka please Ma’u ki bashi
ki kuma sararawa kanki haka haba” Alhaji Qarami ya fada tun kafin nayi masa
qorafin, daga jin yanda m yake magana na tabbatar da ransa a bace yake maganar ta
ishe shi, daman shine dogarona da ze tsaya mun To gashi shima yabi bayan su dole
bani da zabi na bawa Bashir yarana.

Ina Kuka sunayi Baba ya tasa su a gaba har qofar gidan Bashir ya barmu muna hada
musu kayansu, tas muka tattara komai wani abun ma a hannu aka dauke shi Anty
dacAmna suka kai musu.

Dakina na shiga na ringa riskar kuka wannan rashin Adalcin da akayi mun.

AMIRAH A DAREN JIYA


Assalamualaikum Barkanmu da wannan lokacin AUNTY ZEE TAKU CE ,Ina uwar gida Amarya
da yanmata albishir gareku

BONONZA; BONONZA;BONONZA;

Nazo maku da SAHIHIN MAGANIN CIRE TUMBI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI,KINCI GAYU
ANA TAMBAYARKI YAUSHE ZAKI HAIHU TUMBI YA HANAKI ADO DA KWALLIYA SHA KURUMINKI NAZO
MAKI DA MAGANI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI ZAN DANDANA MAKU SHI AKAN RABIN
KUDINSHI DAGA NAN ZUWA SATI DAYA 7K DUK ROBA DAYA KI BIYA 3500 KI MALLAKI NAKI NAN
DA SATI DAYA ZAI KOMA 7K
MAGANIN BREAST WANDA ZAICIKO MAKI DA TUWON NONO DAN ALLAH KIJARABA ZAKIZO KINA
GODIYA DAN DUK WADDA TA GWADA SAITA DAWO MANYAN MATA SUKE GYARA KAMAR YANDA
KUKASANI 8K YAKE ZANKARA TALLATA MAKU SHI KI BIYA 4K KI MALLAKI NAKI
KI BIYA TA WANNAN ACCOUNT DIN KITURA MAN SHAIDAR BIYA
3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
08162859027

🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 43

AMIRAH A DAREN JIYA

Se dare Bashir ya koma gida har sannan tana nade tana jiran yazo ya rarrasheta.
Bayan sallar Isha ya shiga lokacin ta gaji ta fito palour tana zaune tana kallo ga
yunwa tana ji amma ta kasa tashi ta girka abinda zata ci, jira takeyi ya dawo se
suje su siyo abinci.

A sake ya shigo gidan tayi masa sannu da zuwa ya amsa kafin ya ajiye ruwan
dispenser daya siyo ya dawo palour ya zauna yana cewa
“Kawo mun Abinci yunwa nake ji”.

Seta tsaya tana raba ido, wane abinci kuma yanzu ita da take jira ya dawo su siyo
shine ze zo yana wani tambayarta dan haka ta gyara zama a shagwabe tace

“Nima fa Yaya yunwa nakeji, kai nake ta jira tun dazu ka dawo se muje muci
abincin”.

“Saboda babu kayan girki a gidan nan ko kuma baki da hannun da zaki dafa ko yaya?”
Ya fada cikin muryar bacin rai, zata qara magana ya daka mata tsawa yana cewa

“Ki wuce ki samar mun abinda zanci Yanzu bana son bata lokaci, sannan daga yau ma
idan zakiyi girkin dare ki ringayi tareda yara anan zasu ringa cin abinci”.

Harta miqe ta koma ta zauna tana cewa
“Wane Yara zan ringa girki dasu ba a gidan su suke ba sannan kuma ni zan ringa musu
abinci gaskiya bazan iya ba”.

“Ba wai shawarar ki na nema akan zakiyi ko bazakiyi ba umarnine tunda gidan ubansu
ne dole ki dafa abinci ki ajiye musu ko bazasu ci ba, kuma kitashi ki samar mun
abinda zanci yanzu karki bata mun rai”.
Miqewa tayi ta tafi Kitchen din tana mita “haka kawai wallahi babu dan da zan yiwa
girki yaran ma suna gurin uwar su ace ni zan basu abinci wannan ma bame yuwu ba
bane ai”

Haka ta dora ruwa ta saka kwai guda biyu sannan ta dora wata tukunyar ta hau dafa
musu Indomie, a maimakon ta jajjaga attaruhu ta zuba se kawai ta saka dakakken Yaji
ko Albasa bata saka haka ta zuba masa a plate da kwai kwalli daya a gefe ta saka
fork ta kai masa.

Akan centre table ta ajiye, ta koma ta dakko masa ruwa da lemo sannan ta dakko nata
abincin harta fara ci sannan Bashir ya fito daga dakinsa ya chanza kaya da alama
wanka yayi.

Seda ya zauna akan kujera kafin ya kalleta yace “Ina abincin nawa?”

“Gashinan tun dazu na gama baka fito ba Allah yasa ma bata huce ba”.

Wani kallon banza yayiwa farantin da abinda yake ciki kafin ya saka hannu ya dauka
ya tona Indomin da cokalin ciki yana kallonta yace

“Ni zanci wannan abun? Meye wannan kikayi? Idan ma Indomin zaki dafa haka akeyi duk
kayan hadin da suke a cikin Kitchen kika gagara sakawa shine zaki kawo mun abu
kamar na yan birsin ga wani kwai guda daya akai”.

“Wallahi Yaya ka fiya qorafi kaci mana kaji ai tayi dadi ba gashi ni har na kusa
gama cinye tawa ba kuma wane hadi za’ayiwa Indomie bayan wannan harfa yaji na zuba
a ciki dan tayi dandano....”

A mugun zuciya ya wulla mata farantin Indomin Allah ya taimaketa be qarasa kanta ba
ya fadi a qasa ya tarwatse abinka da tangaran, a tsorace ta kalle shi, ya miqe yayi
yo kanta se kuma meya tuna ya kaiwa Iska naushi kafin ya zari key din motarsa yana
cewa
“Allah yasa na dawo na tarar da gurin nan a haka” ya juya ya fita.

Badan tana tsoron abinda kaje ka dawo ba babu abinda ze sakata gyara gurin haka ta
dakko tsintiya da mopper ta kwashe fasashshen tangaran da Indomin ta kai shara
kafin ta saka ruwa ta goge gurin.

“Haka kawai mutum se baqar zuciya kamar kuturu ina laifina dan Allah dama na dafa,
ni da yasan baze ci ba se ya bani na qara dan ban qoshi ba yanzu ya wa mutane Asara
aikin banza kawai” haka dai ta gyara gurin tsaf ta wuce dakinta ta fada wanka, tana
fitowa ta shiga shiri shafa wancan goga wancan ta gama ta saka wata hadaddiyar
Night gown ta gyara gashinta tsaf ta wuce dakin Bashir dan har ga Allah a matse
take.

Tana kwance tayi daidai tana chatting ya shigo dakin fuskar nan kamar hadiri, to
jiki da jini

44 / 80