Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Sanadin Accident Complete Hausa Novel by FASMA

Author :  FASMA Category :  African Stories & Novels

Chapter   21 / 32

60K to 63K   out of 94.8K words

kama da aljanan baki kai ko rabin sweetbaby na
ba...mtsssss

Ta dan jima nan tsaye se kuma ta shiga nema kitchen da kyar ta samu inda yake.
Komi na bukata akwai aciki kama daga..har zata dafa wani abunci dan wata bala'in
yuwa takeji. ..se kuma tayi dariya tace baride na bashi wahala bade ni yayiwa
kishiya ba ..to ai shima ze dandana yaji...


Itama mara mishi baya tayi tana fadin wly dani kake zancen ..

Dakin dake kallon wanda ya shiga itama ta shiga ..ganin daki tsaf dashi komi a
gyare agoge tsaf..bude wardrop tayi taga kayan mace acikin wani abu yazo ya tsaya
mata amakogaro tace kenan de da gaske bangaren matarshi ne ya kawoni dan tamakar
banida galihu awajenshi...

Duk seta ji bazata iya zama ma a dakin nan bare har ta kwana ciki ....
Tana ta wanin ya mutsa fuska da kyar ta shiga tolet tayi wanka tare da doro
alwala ..jakar ta ta dauko ta saka rigar bacci wacce da kadan ta fice guiwa ..tayi
shafe2n ta ..sannan ta fice a dakin ....

Direct dakin data ga ya shiga ta shiga babu ko sallama ..

Shikam lokacin fitowarshi a wanka kenan daga shi se towel ....

Maysam kallo daya ta mishi ta kauda kai direct gado ta hau ba tare datayi me magana
ba...

Shikam yanzu tsoro ma take bashi..

Shima shirin shi yayi tsaf ya kwanta a dayan bangaren....batare dayace ufan ba

Can da kamar minti 20 cukin Maysam ya fara kukan yunwa kuuuu kuuu...
Tun tana daurewa har ta kasa nan ta fara kiran yaya ...yaya..

Yana jinta yayi mata shiru...
Tace pls yaya yunwa nakeji....
Nan ma shiru...

Nan tashiga shure2 tana fadin ita yunwa takeji tama meda abun waka

Yace ke wai bakiga dare yayi bane kije kichen ki dafa abunda kike so ki banni ni
nayi bacci na

Dan galgal ta zauna bisa gadon ta shiga rera mishi kuka ita yuwa takeji.kuma ai
shawarma take son ci yanzu

Ganin fa da gaske ba barinshi yayi bacci ba zatayi ya sa ya daka mata tsawa...
A memakon taji tsoranshi se kawai ta koma ta kwanta tare da rushewa da wani sabon
kuka tana fadin yanzu da Momy ce da ta san yanda tayi dani ...ke koda su Mufeedah
ne da sun tashi komin dare su girka min amman abunda nake so kawai an kawoni ne
daman dan a azabtardani da yunwa..

Dafe kanshi yayi ..yarinyar nan fa ta fara caza mishi kai ..yace wai ke bakya ganin
dare yayi ne kibari har zuwa safe mana..

Maysam tace nide a'a wly yunwa nakeji kamar naci babu..da kasan baza na kulawa dani
ba donmi ka kawoni....
?

Babu shiri ya zari jallabiyarshi tare da key ya fita..ai kuwa mi Maysam zatayi in
ba binshi ba.ta zaro hijab ta kuwa goge hawayen da dama na rigimane kawai...be lura
da ita ba seda yazo fita a fallon ...ze kulleta tace a'a tsayani mana mutafi
tare...

Kare mata kallo yayi hijab ne kawai ta dora a bisa rigar yace ke ina zaki
kuma ....da. Wannan kayan kuma....

Kai tsaye tace rakiya kawai zanyi maka ...
Be kara cewa komi ba ya shiga motar itama tashiga ya tada me gadi ya bude musu suka
fice....

A wani restaurant yayi paking ..yana kokarin fito wa yaga itama zata fito da sauri
ya koma ya zaune tare da kama hannunta yace ke bakida hankali ne zaki fita ahaka ?
Turo dan bakin nan tayi tace wai komi se kace bani da hankali...

Kallonta yayi yace to inba rashin hankali ba ya za'ayi ki fita da wanna shigar
mtsss ya ja tsuka..

Maysam tace inde har baka so na fita to kiss me ...sena hakura nayi zama na a
mota ...kai ko masu ficewa ma bazan kalla ba..

Waro ido yayi yace wai ke yaushi kika fitsare ne haka...

Far tayi da ido batare da ta bashi amsa ba tace pls yunwar fa se karuwa take .kai
kuma se wani bata min time kake..tayi tirjin kamar zata bude ta fita ..

Da sauri ya jawota ya shiga kissing din nata ..su oganniya Maysam har wani lumshe
idanu take burinta ya cika dan ita kam da zaya ciro bakin ma ya bata da ta
yarda ..sun dan dau lokaci sanna ya saketa..

Maysam tayi Murmushi tace kokai fa ...yanzu jeka ina nan bazan fitaba ..

Bece komi ba ya fita a ranshi kuma fadi yake wai taya akayi yarinyar nan ta fitsare
haka.shi yasa fa bayason karatun turan nan..?(ni kuwa nace babu wani turai ai renon
kace ...ko ka manta tun bata san sunan abunba ma kake mata shi ,,ka saba mata da
dorata cinya a kowani time ..se yanzu dan tana ramawa kace baka san ya akayi ba ku
jiye mun shi....๐Ÿ™„)

Ice cream ,shawarma,snake ne ya sayo musu ..da kuma gassasun kaji๐Ÿ˜‹..dan gashin su
yana yi mishi dadi

Suna dawo wa dan iya shege irin nata shawarma daya kawai taci se ice cream shima
roba daya tace ya ishe ta ..

Murad yace kai amma yarinyar nan kin raina duniya .. ..yunwar kenann...
Oya sauko kice ya bude kajin.....kikam tayi tace bataci ..
Murad yace walahi baki isaba dole se kin ci.. ki sani na fita da daren nan amma ki
ki ci...
๐Ÿคฃ๐Ÿคฃwai fans kusan miya hana ta cin kajin ne?
Wai fa ita tsoro take ko na amarcinta ne shiyasa ma taki ci bayan ta hada miyanta..

Daga baya kokarin guduwa daki ma tayi ..aman Murad yayi saurin kamota ...ya dorata
bisa cinyarshi(to baga shi nan ba๐Ÿ™„ )ya shiga bata tun tana dari2 har ta sake jiki
taci abunta..

Bayan sun gama ta tattare komi takai kitchen ...
Brosh sukayi sukabi lfyr gado...

Maysam kam matsawa tayi ta shige mishi jiki kan kace mi bacci me dadi yayi awon
gaba dasu..
Tun asuba bata koma bacci ba kamar kullum...
Murad yana shigowa ya ganta bisa sallaya se karatun alqur'ani take..sata gaba yayi
ya tankwashe kafafu ya wani rufe ido wai muryar tayi mishi dadi..a hankali yake
bin ta suna yi tare..

Seda takai aya ta Rufe ta ajeshi tace yaya g. morning...da fatan ka tashi lfy...

Murad yace ina fa na tashi bayan duk kinyi ta laftamun kafa ni duk jikina ma ciwo
yake mu..kai dole ma ki koma dakin ki.

Maysam ta turo baki gaba sede batace kalaba..amma a ranta fadi take babu inda zani
ina nan .dan bazan iya kwana a dakin waccar abar ba ehe

Sun danyi shiru .Maysam tace kai yaya babu ko dan Morning kiss din nan ma ..

Kallonta yayi yayi yar dariya yace waike bakya gajiya ne..

Kara turo bakin tayi ta tashi ta shige tolet tana zuwa dede kofar ta murguda mishi
baki tace e din ai duk renonka ne kai ka koya mun...

Wanka tayi koda ta fito baya nan ya fice dayan dakin yin wanka tunda taki zuwa
ita.haka tayi shirin ta na school dan gudun magana se tayi irin shigar dayake so
wato hijab nikaf da safa....

Dukda kuyangin da suke nan sun yi musu abun break aman Maysam da rigima seda ta
sake girka wani a ranta tana fadin kenan ma harda kuyangi ya samarwa matarshi
ko ...humm..(kya de ji da kishinki๐Ÿ™„)

Mafi saukin break tayi wainar kwai,da plainted se ruwan tea ..nan palo ta saka
kuyangi suka jere mata su...

Ta zauna kenan ya fito daga room da shirin shi shima ..zama yayi a kasa kusa da ita

Maysam tace yaya ga naka can fa wannan nawane wanda na girka fa ...

Murad yace to nakin zanci nima me rowa kawai.
Shiru tayi mishi nan suka fara break din ...suna gamawa ya kaita har kofar school
din su ..ya shiga wurin principal din yayi mishi bayanin komawar su can gidan
shi...

Abunku da jami'a kuma ma ta turai dan haka sugaban be wani nuna wani abuba ya bashi
autorisation din zasu iya komawa ... Daga nan ma ya fice wajen aikin shi...

Haka kuwa akayi bayan sallar isha'i suka tattara komi nasu suka zuba a motar Murad
hann se gidan shi...

Ganin barin mata su kad'e a bangare daban hatsarine duk da akwai dedekun dogarai a
gidan amma it is a risk dan haka ya basu dakuna biyu na nan kasan bangaren dayake
ikirarin na kishiyar Maysam ne ...

Shikuma suna dakunan sama da Maysam ..

Har Maysam na tambayar shi to in me bangaren ta dawo fa mi ze ce mata ne...

Ya bata rai yace ke ina ruwanki ne..

Haka sukayita zama a nan gidan Murad cikin kwanciyar hankali suna kuma karatunsu
sosai da sosai....shakuwar su ma kam se abunda ya karu

Ana haka bayan two week ya shirya ze tafi ganin gida ..Maysam kamar tayi hauka ba
dan ta kwallafa rai a karatun nan ..da babu abunda ze hanata zuwa gida ganin
fulani..ranar daze tafiya sha kuka har yaji kamar ya tafi da ita da kyar ya samu ya
lallabata ya tafi ..


Ko su su fulani dirar bazata yayi musu dan ko jiya Mahmud daya kirashi kan cewa
yana so in ze taho ya zo mishi da camera kamar goma haka hight class nacan ...koda
ya tambayeshi yaushe zezo se ce mishi yayi kawai se sun ganshi ..
Zo kaga murna wajen Fulani kamar mi tama rasa inda zata saka shi nan suka gaisa ya
kara neman yafiyar ta...

Tace dashi yanzu de ya shiga ya gaida dadyn shi se ya tafi yayi wanka yaci abinci
ya huta daga baya sa yi magana ..

Babu bata lokaci ya cika umarnin ta ..

Fulani se kara godiya take ga Allah ..tana me kara addu'ar ya kare su daga sharri
masu sharri..


Yana shiga wurin Sarki ya tarar da Madina acan da alama de wani muhimmin abu ya
kawo ta dan basa shigowa fada a yini rana sede da dare..
Wata zabura da babu shiri Madina tayi cike da mamaki take kallon Murad a ranta fadi
take yau ni naga jarababbe dawo kayi..in ba ma mas...

Bata gama fadiba Sarki yace lfy de ko..?
Wayence wa tayi da fadin farin cikin ganin d'ana ne nake yayi mana zuwan bazata ne
tana wani dariyar yake amma da ka ganta kasan bata da gaskiya se wani fiki2 da ido
take.
Sarki ma shareta yayi dan murnar ganin Murad din ya rumgumeshi yana jin dadin ganin
tilon dan shi..

Madina ta danne abunda ya taso mata tare da cewa bari na baku wuri zamu karasa
maganar daga bayama ..sum2 ta fice tana saka da warwara...


Sun jima suna hira da dadyn shi .....sanna yayi mishi sallama ya fice..Yana zuwa
bangarenshi ya tarar da Mahmud yana jiran shi..

Rumgume juna sukayi suna me jin dadi ..nan ya sake bashi hakuri kan abunda yayi
mishi ..

Mahmud ya nuna mishi komi ya fice ......
Murad yace ga camerorin ka daka damen da zancen su ..

Cikin sauri da hanzari Mahmud ya karbe yana fadin kai amman na gode Allah ya
biyaka ..

Murad yace wai ni mi zakayi dasu ne haka da ka wani azalzaleni ne akansu. .kaida ko
budurwar taka ma na can England se ko yan gida zakana dauka halan ..

Mahmud yayi dariya yace kaide yanzu ka yi me wuyar sauran zance zakaji shi wajen
Momy ..yana fadar haka ya sa kai ya fice tare da fadin Allah ya hutas da gajiya..

Murmushi yayi shige bathroom..

A bangaren Maysam kam bata san ta shaku da yayan ta ba se yau ta saka waya gaba
tana kallo.. jiran kiranshi kawai take ya shigo amma shiru...ta kirayi Fulani bayan
sun gaisa take sheda mata mijinta ya iso lfy ..sun fan tattaba hira tukon suka
kashe.wayar..

Shikam Murad dayayi wanka yaci abinci sanna yazo yabi lafiya matela amma kuma se
bacci ma yaki zuwa se lokaci tunanin yar renon shi yazo yayi mishi katutu besan ya
kara shakuwa da ita ba se yanzu ..duk se yaji gadon yayi mishi fadi..wayarshi ya
jawo ya danna mata kira ..

Maysam da rigima wayar na hannunta fa aman se akira na ukku ta daga ...

Sallama yayi kafin ma ta amsa yace ina kika shiga ne kikabar wayar ina ta
kiranki...

Turo baki gaba tayi kamar yana gabanta tace ina na shiga ko ina ka shiga ..bayan ma
kai ka manta da ni din..

Dafe kai yayi yace inji wa kekam bakya rabuwa da rigima. Fa..

Ai nan ta shiga zaba mishi shagaba kamar ba gobe da kyar ya lallabata ......
Suka taba hira sanna ya kashe wayar
Se lokacin ya samu baccin ya dauke shi ....bashi ya tashiba se gabbanin azahar
alwala yayi ya fice masalacin masarauta....

Daga nan kuma ya fice bangaren Fulani..
Tana lazimi ya shigo da alama itama yanzu tayi sallar seda ya bari ta gama sannan
ya sake gaisheta ...nan suka cigaba da hirar su har tana tambayyar yar ta Maysam
tace inji de baka matsa mata ko..

Murmushi kawai yayi aman a ranshi fadi yake ai yanzu kam ita take matsa min abu
kadan se take kiss me ..gashi ko kallon banza bana iya mata ...

Fulani ta katseshi da fadin nasande Mahmud ya sanar maka da komi ko..

Kalar tunani yayi yace akan mi fa ?

Nan fulani ta sanar mishi da komi kan su Madina kafin ta gama hawaye na
tazuba ..kamar karamin yaro ya rarafa ya dora kanshi bisa cinyar ta yana kuka ..

Nan ta kara yi mishi nassiha tare da gaya mishi plan din su sosai yayi na'am da
shawarar nan yakara shima tashi fasahar .......sosai yaji dadin irin yanda Mahmud
ya nuna bajintar shi lallae ya cika aboki.......

A washe garin ranar aka saka camerorin anan bangaren Fulani dana Murad ..kai harda
na bangaren Murza ma ..na Madina ne kawai yayi musu saura...
๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน. ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน
A bangaren Madina kam tana fita ta dannawa Murza kira ...babu bata lokaci da shigo
bangaren nan cike da zafin rai da bacin rai take sheda mata Murad ya dawo gida
yanzu nan ..

Murza tace kai ni wannan jaraba da mi tayi kama ..yaro nan dan bala'i ne ..yakama
wanna karon muyi mishi me kan kat kawai..

Madina tace kawai kice ya haukata muna shi kiga kawai ma may be mota ta kadeshi ma
ya mutu a yawon haukar tashi ......

Murza tace karai kuwa kawai hakan ma za'ayi....

Nan ta sake zube mata kudi .Murza ta faki idon mutane tayi satar hanya ta
fice ...se gidan boka yankan adda...


Tofa ya kuke gani ?shin zasu sake cin nasara ne akan Murad?

Senaji comment dinku๐Ÿ‘†



Fasma ๐Ÿ–Šyar mutan Zinder
[9/11, 8:50 AM] A A Dboy: *_POST BY GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP
08064400100_ ๐Ÿ“š๐Ÿ“š_*
[9/11, 8:51 AM] A A Dboy: ๐ŸŒŸ *STAR WRITER'S ASS* ๐ŸŒŸโœจ๐Ÿ–Š
( _Home of spรฉcial ๐Ÿก&extraordinary writers_ )


๐ŸŒน๐ŸŒน *SANADIN ACCIDENT* ๐Ÿ’ฅ๐Ÿš‘๐ŸŒน๐ŸŒน

S.W.Aโœ

๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ชStory&Written
by
*FASMA* ๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ช

*Ohh my Aisha tu me manque dรฉja ...wish you all the best๐Ÿ˜โคโคโคโค...* love you irin
sosai din nan

_My Mimsqueen Allah ya baki lfy ya sa zakkar jiki ne...๐Ÿ™.._



Dedicated to all my fans๐Ÿ˜โค




๐Ÿ…ฟ 89__90




```Manzon Allah (SAW)ya ce''idan wani daga cikinku ya tashi daga wajen zamansa
sannan sai ya dawo to shiyafi dacewa da wajensa.
Bukhari ne ya rawaito shi.```




[06/08/18 ร  20:29]Ba ta dau lokaci ba se gata gaban boka yankan Adda ....nan ta
kwashe dawowar Murad ta gaya mishi tare da sabon kudirun su....
Ya dan jima yana dan tsibacce2 shi har wata zufa take karyo mishi........can ya
dago yace wannan aiki baze yiwu ba dan yaron a tsare yake ya fice inda kuke
tammahani..

Murza tace to kawai ka haukatar mun da matar shi Maysam. .

Sake yan tsubucce2 yayi yace ita kam wannan tama fishi sammun kariya dan ta rike
addu'oi baza mu iya yi......ganin irin kallon da Murza ke mishi irin kallon nan ne
na in bazaka iya ba kawai bari na nemi wani....a ranshi yace wannan fa batada
mutunci yanzu seta tafi abunta batare da taban komi ba ...amma bari na mata irin ta
mu ta yan iskan gari..

Wata dariya ya kwashe da ita lokacin har tana batun tafiyarta jin bukatar ta bazata
biya ba gwara ta nemi wani gun..

Yace koma ki zauna aikin ze yiwu amma za'a kashe makkudan kudi dan wannan aiki ja
ne..

Washe baki tayi tace yanzu naji zance me dadi.....to ina jinka..


Wani turare ya bata cikin kwalba yace gashi wanna asan yanda za'ayi ya shaki kamshi
nan ..to ina tabbatar miki yana shaka kamshi ze gusar mishi hankali...sede wani ba
shiba...

Murza jitake kamar tayi fiffike ta ganta a wurin Madina ta sheda mata wannan daddan
labari .......

Tana fita bokan ya kwashe da dariya yace zaku san dani kuke aiki ... Ba'ataba kawo
min aikin danaga bazanyi nasara ba se wannan .kawai har kunsa na fara ji akwai
abunda ze gagaren a duniyar nan..hhhh..

Yayi wani kirarin shi can kuma yace se kai dan hatsabibi ka bita kawai tana fito da
turaren ka kwabeshi ya zube sanna ka bayyana siffarka ga wanda duk ya shaki turaren
nan dan suyi hauka me degree kowama ya huta..dan in shi Murad din ne babu abunda
zeyi mishi ..ni kuma bazanyi asarar turaren nan ba...fuuuu ya fice dan cika
umarni..

Tana zuwa direct bangaren Madinar ta fice bakin nan se wageshi take ...
Madina tace da alamade anyi nasara yau..

Murza tace kwarai kuwa dan kinga ma abunda ya bani ta fito da turaren zatayi wa
Madina bayani ai kuwa Hatsabibi ya kwabeshi kwalba ta tarwatse a kasa turare ya
zube anan..

Wani waro ido Murza tayi se kuma ta dauke numpashinta a million ta bar bangaren
Madina dan ita tasan hukuncin wannan turaren...

Ko iida fita daga palon batayi ba taji Madina ta kwalla wani uban ihu e kuwa se
takara gudun ta har seda ta fita tukon ta dedeta nutsuwarta dan kar wani ya
ganta.....gidanta ta shiga can kuryar daki har da saka sakata. . jikinta banda
karkarwa babu abunda yake..kamar ace mata ke ta arce se wani waware ido take.....

A bangaren Madina kuwa hauka turben takeyi kuyangi duk sunyi cirko2 a kofar dakin
dan kana shiga inta damke babu me rabaka da ita dukan kawai zatayi ta lakada maka
duk abunda ta rarima buga maka zatayi ..ga dariya ka-ka-ka tana fadin nice nan
ajalinshi kamar yanda na zama ajalin dan uwanka da sweetbabyn ka..da waziri hhh

Walahi yau sena kashe ka ..tun kana cikin zanin goyo nake bibiyar rayuwar amma kaki
mutuwa to yau sede wani ba kai ba..
Lokacin labari har ya isa ga sarki dama suna zaune ne a fada harda Musa da
Murad.dakula Mahmud .ai kuwa a tare suka shigo fulani ma isowarta kenan..sukaji
tana tonawa kanta asiri ..kaf makircin datayi seda ta fadeshi yau .gaba daya aka
dauki kabbara tare da da fadin inna lillahi wa inna ileyhi rajou'oun.......Malam
Musa duk jikinshi yayi sanyi jin harda Diyar Maysam a harinta amma se ya shiga
yiwa Allah godiya daya kubutar mishi da ita....

Fulani kam har ta fara hawaye jin itace ta kashe mata danta data haifa na Fari wato
yayan Murad wanda ko sunanshi ba'ayi ba ya mutu ......kasa tsayawa tayi ta koma
bangarenta cike da tausayin kanta da kuma tausayin Madina jin irin rayuwar data
saka kanta saboda kishi kawai.....

Murad nan ya zube ya shiga rera kuka jin da sa hannunta ya rasa rabin
zuciyarshi ...,,,Mahmud

21 / 32