Author : FASMA Category : African Stories & Novels
réussit et plein de succès.. Today is your day so profite bien.because
ça ne vient qu'une seule fois par an hbd
*Ohhh Allah ashe haka masoyan Maysam kukeda yawa ... hakika ina alfahari da
ku ..Maysam na meka dubun* *gaisuwa zuwa ga fans dinta tace tana yinku irin sosai
din nan lol..Fans wly* *kuna da yawan bazan iya lissafo kuba dan se na cika page
din nan . .amma fa sako daga MUHEEBA tace kada ku sake hanya ma ta gama ku* ..
*Mussaman ma ke Maman SS ...Amma fa tace na gaishe mata da masoyan ta mussaman My*
*Zee (Zaynab Idris ba ) tace tana yinki* ..
_Welcom back Momyn Mufeeda Allah ya kara lafy ya sa zakkar jiki ce ._
*My in law(Xaynap queen),,my Arfat,and Ummu Usman ,i miss you a lot pls come back
soon
*
Dedicated to yo my SAMBABY
71__72
```Manzon Allah (SAW) yace''wanda duk ya yi imani da Allah ,da ranar karshe to ya
kyautata wa makocin sa .''
Mislim ne ya rawaitoshi...
```
[ Washe gari da wani farin ciki marar misal tuwa masarautar mussaman oga Murad da
yar renon shi Maysam..
Abangaren fulani ma duk jitake kamar an sauke mata wani abu akanta..
..wajejan goma na safe suka fito cikin shirun su na fita yawon ...lokacin da suka
shiga gaida Fulani ba karamin kyau suka mata ba sunyi matukar burgeta sun kuma dace
da junan su matuka kai yau har wata kama ma taga sun mata ...bayan sun gaisheta ne
yake sanar mata za su fita cikin gari ...
Fatan alheri kawai tayi musu har da tsokanar Maysam take ..ita kam bada dariya da
sunne kai babu abunda take ..gwanin ban sha'awa ...
Dede zasu shiga mota Muheeba ta tsinkaye su fito warta kenan ...da sassarfa ta iso
tana fadin good Morning my future ....
Daga Murad har Maysam Kallon mamaki suke mata bama kamar Maysam ba data ke ma Murad
kallon tuhuma ganin haka yasa shi Wayencewa da fadin morning too kamar me ciwon
baki (to fa mulkin ya motsa )a ranshi kam dariyar mugunta yake yi wa Muheeba dan
yana da yakinin bata ji labarin fasa auren nan ba......
Maysam kam ta cika tayi fam ..
Dogarai kam suna ganin Muheeba suka zube nan se kwasar gaisuwa suke ..
Cike da mamaki yake kallonsu a ranshi yace yaushe har ta samu matsayin nan ...
Koda ya kalleta seyaga ita kuma se wani sham kamshi take tana wani dadaga kai...
Shi abun dariya ma ya bashi
Da fari su biyu kawai ya so su fita amma gani irin kallon da Maysam take mishi ya
sa driver jan su cikin wata mota kirar Prado 2018...gaba da bayan motar kuwa an
rubuta Yarima Murad12 ..
Dogarai ma suka shiga motocin su
Gidan baya suka shige suka bar Muheeba nan sake da baki ..kwafa tayi tace oho de
kuyi ku gama kafin na shigo ...tana wata tafiyar ta ta kasaita ta shige part dinsu
wai ita a dole ga futur wife din YARIMA me jiran gado ..
Duk inda ta gilma to se kuyangi su duka har kasa su kwashi gaisuwa in ba haka ba su
fuskanci hukunci...
Kaf gidan babu me sonta kai hatta kuyingin ta sun gaji da halinta kawai dan dole
suke mata biyyaya
A mota kam Maysam anci kip ta juyawa murad baya tana kallon waje ta glass banda
turo baki babu abunda take....
Shi kuma duk ya wani rasa nutsuwar shi ...driver ya bawa oder inda ze kaisu se kuma
ya danna wani buton nan kusa dashi a take wani bakin ''rideau''(labule) ya rufe
duka glass din motar banda da nan tsakanin su da drivern .gaban motar ne kawai babu
labulen
Murad yace ke!!
..
har cikin ranta taji kiran sede batan amsa ba kuma bata juyo ba ....
Nan fa shima zuciya ta fara dibanshi ya shiga mata fada wai mi aka mata dazata saka
mutane gaba tana hushi ...da karfi ya sa hannu ya kama dantsen ta ya jiyo ta yace
ke wai yaushe reni ya fara shiga tsakanin mu dake ne da har ina miki magana ki ki
amsawa ..
Mi Maysam zatayi inba kuka ba daman jiran kiris take ta kuwa fashe mishi da kuka
dan wurin jiyo tan karfi yasa mata abunka da jikin daya ji hutu gashi abun dama ba
wani kiba ba....sosai taji zafi a damtsen...tana kuka take murza wurin tare da
fadin kayi hakuri bazan karaba...
To fa an taba zuciyar maza nan shima ta fara yi mushi zut .. shima daurewa kawai
yayi amma fa ji yake kamar yayi kukan shima besan miyasa ba baya son kukan ta ko
kadan. .....
Rungumeta yayi ya shiga lallashin ta. Ga electric shock na ratsashi aman ya daure
yana mata massage din damtsen..
Tsit maysam tayi dan tunda ya rungumeta ta ji wani électric shock wanda bata taba
jiba a da..
Kokarin kwace kanta take amma ba rikon ragon namiji yayi mata ba ...dole ta hakura
ga zuciyar ta data sauya rythme fat2.....
Jin ta nutsu .yasa ya kwantar da ita ya shiga kokarin kissing dinta wanda zuciyar
shi take kitsa mishi kan tana son dan karamin bakin nan ..shiyasa ma yake biye mata
..
Maysam na ganin haka ta kauda fuskar ta gefe.
juyota yayi .yana kallonta
Ta kuwa rumtse idonta kam
Jin an tsaya yasa ya fasa dan yana da tabbacin sun iso wurin shopping din daya bada
oder akawo su...
Maysam kam hamdala tayi ganin ya fasa dan ita tana ganin kazantar yin hakan....
Haka suka wuni yana kaita wuri2 a takaice de yau Maysam ta gama wa garin
kallo ....se daf da magarib suka dawo inda suka tarar da labarin abunda ya samu
waziri .......
.
Wato bayan futar su da kamar awa guda SARKI yane mi Waziri tate da sauran yan
fada....
Shi kam lokacin ji yake ko an bugo kati ne ma..da sassarfa ya amsa kiran..
Fada tayi tsit kaf makaraban fadar sunan nan zaune jiran jin abunda me martaba zece
dasu ....da farko se da yayi mu su nasiha tare da jan hankali..can de ya sanar musu
cewa an fasa auren nan ...
Be gama rufe bakiba Waziri yayi cuwat tare da fadin to baka isa ba ....aure kamar
an yi shi an gama..
Nan aka fara kallon2 ..
Sarkin hukunci har yayi wata irin wawura ya iso gaban wazir jiran umarni kawai
yake..ya zartar
Fadawon gaba daya suka shiga bawa Sarki hakuri
Gyara murya sarki yayi fadar tayi tsit banda waziri daya ke fadace2 kamar wani
sabon kamu...se wani fizge2 yake..
Da karfin tsiya aka zaunarshi amma bakin nan ya kasa rufuwa .....
Shiru akayi ana sauraron shi ..wai kun san mi fans?
Gaba daya sirri shi dana Madina ya shiga tonawa kaf duk abunda sukayi seda ya fada
da irin makircin da sukayi ...kan kace mi fadar ta kacame da hayaniya..
Gyaran murya sarki ya karayi bacin rai karara a fuskar shi ya bada umarnin da aje a
tsare waziri har se an yi bincike akanshi ...dan abun nashi ba sauki da alama ma ya
fa haukace...
Lokacin da labari ya isa ga muheeba sumanta biyu da kyar ta dawo normal ...ga
rashin cikar buri .ga waziri ya haukace abun ya game mata biyu ..mahaifiyar ta ma
banda jimami babu abunda take..
To fa Abangaren Madina kam dadi kasheta ne kawai beyi ba dan ita jitake aikin bokan
su ne yaci ....ranar kam bayinta ma sun san tana cike da murna ,,...tace kowa yaci
tuwo dani to miya yasha harni ze ci amana ta kadan ma ya gani....
Sede tashin hankalinta guda ..shine yanda waziri yake fallasa asirinsu amma dayake
ta jima tana makirci babu wanda ya zargeta ...dan tana nuna tana son Murad a gaban
mutane so babu wanda zeyi tunanin ta aikata hakan... Gashi kuma an sheda cewa
waziri ya samu tabuwar hankali da wannan take kwantarwa da kanta hankali..
Murad kam beyi mamaki ba dan dama yasan akwai wata a kasa ..Sede yayi addu'ar Allah
ya qara kare su daga sharrin masu sherri.
Haka rayuwa tayi ta tafiya yau sati cur da faruwa wannan al'amari amman jikin
waziri se gaba yake yi kai yaneu har da bugo ma ya fara ..
Bayan bincike me zurfi da sarki yasa akayi mushi a ka gano irin makircin da waziri
da iyanlanshi sukai amma abun bakin ciki ba'a gano nasu Madina ba ...haka aka yanke
wa su Maheeba hukunci barin garin itada su waziri bayan an yi musu horo me tsanani
itada Mahaifiyar ta...
Haka suka fito daga masarautar da kullin kayan su Miheeba se waiwaye take tana ma
masarautar kallon karshe..Mahaiyar Muheeba fadi take duk ke kika jawo muna da baki
kwallafa rai ba da duk hakan bata faru ba ..dama boka yace kada mu bari asirin nan
ya karye ka irin ta nan yanzu mahaifinki ya haukace..
Muheeba kam kukan ta na rashin aure nan ne takeyi aka ma bata kawo da rashin lfy
waziri .....keken naped suka shiga ze kaisu aéroport su shiga jirgin zuwa ghana
wajen dangi su...dan sun kwaso kudi..
Suna tsaka da tafiya ..abunka da mahaukaci ya faki idon su ya karkata musu
sitiyarin ..naped dun ..jikake katsam..sun gamu da wata babbar motar .....
Kuyi manage da wannan ..
Fans nasan kuna min uzuri aman ku kara akan nada ....ina yinku irin more totaly din
nan..
Fasma ce
[9/2, 10:16 AM] A A Dboy: *_POST BY GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP
08064400100_ 📚📚_*
[9/2, 10:41 AM] A A Dboy: 🌹🌹 *SANADIN ACCIDENT* 💥🚑🌹🌹
🇳🇪Story&Written
by
*FASMA* 🇳🇪
73__74
```Manzon Allah (SAW) yace'kumya tana daga cikin imani'
Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.
```
Jikake kwatsam sun gamu da wata babbar mota .......
Me babbar motar ya kuwa tsere ya barsu nan ...
Gaba dayan su a sume suke ...da kamar minti goma me a dedetan shi ya fara farfadowa
cikin ikon Allah be ji wani ciwo sosai ba se dan gurje kafa dayayi ...Muheeba kam
da wani irin taratsi ta farka ...ganin ta nan shaye a kasa komi ya dawo
mata ...kuka ta shiga rerawa gashi tana son tashi amma ta kasa wani irin radadi
takeji a kafarta da fuskar ta ...hannu ta kai ta shafa fuskar wani razannan ihu ta
saka jin wani bala'in zafi ga kuma jini ya bata mata hannun..
Wannan ihun shi yayi sanadin farfadowar Mahaifiyar ta ........
Ita kam da alama bataji ciwo ba itama se karayar data samu a hannu ...rarafowa tayi
kusa da Muheeba ..nan suka shiga rera kuka .....ganin duk glass ya yanyakewa
Mufeedar fuska kuma da alama kuma ta samu karaya a kafar hagu.....me adedeta kam
fada ya shiga yi musu sun san mahaukaci ne miyasa zasu shigar me a dedeta ..nan ya
dinga bala'i kan se sun biyashi adedetar shi.dan baze dsuki asara ba....
Ganin abun bana karewa bane yasa suka bashi. kudi me yawa .dan sun kwaso kudi ..ba
ko kunya ko tausayi ya karbe a bunshi ...da kyar ma ya dan ja adedetar ta bar
titi ..yayi tafiyarshi...
Can Muheeba ta lura da waziri fa baya numpashi iya karfinta ta ce Abbaaaaa ..tana
kokarin jan kafar ta isa...Maihaifiyar tata ta daure da sauri ta isa kusa da shi
tana fadin waziri2 amma ina baya ko motsi .....daya ke sun kusa eareport din shiya
sama babu gida je nan kusa ...baya ta koma cikin gari dan neman temako.....cikin
sa'a ta gamu da wani me adedeta ...shima da farko ya so kin daukar su amma seyaji
tausayin su ga kuma kudi me yawa da zasu bashi in de har ya kaisu cikin gari...
Da kyar ya iya saka waziri a motar ...suma suka lallaba suka shiga ...
dede wata clinik ya kaisu yana ajesu yayi tafiyar shi dan ma kada ace se yaje
police station yayi reporte. ..
Dayake abun na masu kudine nan danan aka anshe su akayi emergency da su ...akayi
musu dorin karaya da duk wanin abun da ya dace...tare dayi musu allurar bacci dan
su sami hutu...
Lokacin da suka farfado daki daya aka kaisu..bayan doctor ya shigo ya kara dubasu
har ze fice Muheeba tace ya jikin Abbana...
Seda ya share gumi tukon ya fara yi musu nasiha sanna ya sanar musu cewa waziri ya
rigaye mu zuwa gidan gaskiya Allah yayi mishi cikawa se de kuyi mishi addu'a dan
har an bunneshi ..
Wani irin ihu Muheeba ta saka se kawai ta sume nan..
Tashin hankali mahaifiyar ta shiga ga Mutuwar miji ga diya ta sume se kawai ta
shiga rera kuka itama..
Can zuwa dare ta farka babu wata addu'a sema kiran Abbata datakeyi ..nan mahaifiyar
ta shiga lallashin ta ....
Tana kuka take fadin duk nice sila da ban nuna ina soba da duk haka bata faru ba
gashi yanzu SANADIN ACCIDENT na rasa Abbana wanda na fiso ...ga kafata ta
karye ..kaico na ni Muheeba naga rayuwa .
Mahaifiyar ta shiga lallashin ya itama tana me tausaya wayar tata..
.
To fa a bangaren Madina da Murza ba karamar murna sukayi ba dan duk ji suke aikin
bokansu ne yaci...Murza harda zuwa yi mishi godiya tare da kara mishi kudi daga
Madina..se kuma suka fara shirye2 yanda za suyi asirin ya kama Murad..
A bangaren su kuwa rayuwar jin dadi suke ...yana kula da ita matuka wai saboda
Fulani taji dadi yake yi a cewar zuciyarshi fa....
Tana cika sati ta fara shiryen2 komawa ecole ..wannan gamin ma seda ya rakata har
Maradin .
Lokacin da zuyi bankwana shi ze dawo dan so yake washe gari shima yayi ficewar shi
England....
Suna mota a aereport se shagwaba take mishi ..shi kuma se lallaba ta yake kan ta
yarda suyi tafiyar su England ....
Da farko har ta amince amma jin wai in ta tafi baza ta cigaba da karatun ta yasa
tace ta fasa zuwan ..wai rayuwar can da nan ba daya bace...itade jinshi kawai
take...se turo dan karamin bakinta take ...dan tana son karatun ta..gashi a
islamiyya ma sun yi nisa
Batayi aune ba taji Oga Murad ya shiga kissing dinta ....
Tureshi take amman kamar batayi .dan mayen electric shok din nan se ratsata
yake..shima wannan karon dauriya kawai yakeyi .....tun tana jin dadin abun har yazo
bakinta banda zafi babu abunda yake yi mata. .
Kokarin tura hannushi yake cikin rigarta(ni kuwa nace to mi ka aje ne a wurin kaida
kace babu su
...)...
Rike hannun tayi tana girgiza mishi kai kukan ma ya kafe..
Amman shi kam se kara turashi yake ...
Ganin ana shirye2 fara kiran ma su tafiya yasa da kyar ta rabashi da jikin ta se
haki take tace nide gaskiya2 ...se kuma tayi shiru..dan azahirin gaskiya bazatace
ga abunda take jiba
Yana mede numpashi yace kede gaskiya mine?
Cike da yarinta da tsoro tace nide bana son wannan abun muryarta har sarkewa take
Kuri ya kafeta da ido yace miye din bakya so ...
Tace kawai se ayi ta durawa mutum miyau gashi bakin ma se zafi yake mun...
Jim yayi can ya kalleta yace bade ba kya so ba..
Ta gyada kai..
Yace shikenan bazan kara yi miki ba..
Cike da yarinta kuma ta fada kanshi tana Merci beaucoup yayana(thanks alot)..
Goshinta ya ma kiss sanna ya fita ...ya nufi wurin da ake kiran passengers...
Tana daga mishi hannu har jirginsu ya daga ...duk kuma se taji ba dadi
Driver ya dawo da ita school dinsu . suka hade da kawayenta nan suka shiga
revision'(review)din karatun su dan shugaban makarantar yace inde har sukayi kokari
suka kawo maki excellent to ze yi musu tsallaken Ss2 direct kawai suje Ss3 ..dan
haka sun dauri niyar yin karatu na ban mamaki ..
Haka Murad ya dawo jiki ba kwari dan be ji dadin abunda Maysam tace mishi bs. .....
Tun nan aereport din ya ciri ticket zuwa England gobe...
Yana zuwa ya sanarwa da fulani f......fatan alheri tayi mishi
Zuws dare kuma Yana sanarwa da me martaba zancen tafiyar Madina ta shigo karaf se
akkunan ta ...
Wata dariyar mugunta tayi ta koma bangarenta...
Jakadiyarta wacce tayarda da ita ta bawa magani a turara mishi..tace tayi maza ta
tafi yanzu kan ya dawo daga wajen sarki
Cikin sa'a kuwa bata sha wuyar shiga bangaren Murad ba. ..nan ta turara tafice
abunta..
Yana shigowa ya shaki kamshi .nan ya fara jin kanshi yana juya mishi tare da wani
irin ciwo..sunan Allah ya shiga kiran ..se yaji abun ya lafa amma mi se yaji duk
garin ma ya ishe shi ...gaba daya Allah2 yake gari ya waye ya tafiyarshi ...baccin
kirki ma beyiba
Garin na wayewa dama jirgin 9h ne ze bi ..dan haka tun takwas ya shiga yayi wa
Fulani da Sarki sallama ...ya fice cikin sauri..
Fulani kam wanna karon ma a jikinta taji kamar ta hanashi tafiya .amma se ta bishi
da addu'ar Allah ya tsareshi ya kareshi da duk wani abun cutarwa daga mutum ko
aljan..
Madina dadi kamar ta mutu ..se boka ta ke zumbudawa albarka...(hum .)....
Bayan sati da faruwar haka.. Da dare Sarki da matanshi suna hira dan kullum su se
zuwa dare suke samun ganin shi. ..
Fulani tace dama akwsi wsta shawara dana keson badawa ....
Sarki yayi dan murmushi yace ai ke duk dhawarar da zaki bada me amfani ce dan haka
kafin ma naji miye na amince ...
Fulani ma dariyar marar sauti tayi dan tana jin dadi irin confidence da sarki ke yi
mata..
Madina wacce ta kullu jin furucin sarki tayi kwafa tare da yi tsaki kasa2 a ranta
tace shiyasa a kullum tsanarta tske kara ruruwa a zuciyata. Se shegen iya kissa dan
inta na wuri sarki mantawa ma yake da akwai wani a wujen ko a'a..shiyasa take mata
lakabin makirar mace..dan gani SWEETBABY ma renonta ce kafin Accident shi ya sama
Murad ya Makalkale mata ya kasa yakiceta daga rayuwarshi..(jifa wani sharri )
Sarki yace ina sauraronki
Fulani tace dama cewa nayi in baka zabi wanda zaka sa a matsayin wazirin ka mi ze
hana a nada Malam Musa mahaifin Maysam ...
Sarki yace kamar kin shiga zuciyata kin gani nima haka nayi wannan tunanin ..
Fulani tace to ai dama ni cikin zuciyarka nake shi yasa na gani . tanayi tana wani
sakin sharme...a tare suka saki ma juna murmushi..
Kutttttt wani malolon bakin ciki ya ziyarci zuciyar Madina ..ta daure de tayi
gyaran murya dan ta hago wanni abun ..
Itama cike da irin tata kissar tace wannan shawara tayi ..ina goyon bayan
hakann.......
Washe gari kam Madina ta sanarwa da Murza cewa sun kusa dawo wa nan dan haka sesu
ci karansu ba babbaka..
3 jours(days)da yin maganar Sarki ya tura sakon san ganin Musa ...
Babu bata lokaci ya ansa kiran ..Murza kan se murna ake za'a kaura birni..
Bayan ya iso sarki yayi mishi bayanin kiranshi ...da farko ya so ya kiya amma se
yaji baze iya cewa sarki a'a ba dan haka ya amince..ba karamar murna sarki yayi
ba..
Kafin sati ya zagayo har sn nadashi sun kauro masarautar....
To fa Murza a masarauta kusa da Madina ..se yaya kenan..
Love you all irin more din nan
Story&Written
by
*FASMA*
*Alherin Allah ya kaiwa masoyan wannan book din a duk inda kuke ..hakika* *ina jin
dadin comment din ku kuma yana bani kwarin guiwa ...daya wa naga sakon ninku..wasu*
*suna cewa ina jan aji da rai ..to bahaka bane muma muna da uzuririka a
gabanmu .....Allah* *ya bar kauna da zumunci ina yinku iri more totaly din nan*
*Pls masu juyamun littafi ku dena bana so . ...kun san kanku base na tona ku cikin
jama'a ba so tun kafin abu yayi nisa ku fasa ....*
Dedicated to all my fans
75__76
```Manzon Allah (SAW) ya