Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Dauɗar Gora Complete Hausa Novel by Bilyn Abdull Ce

Author :  Bilyn Abdull ce Category :  African Stories & Novels

Chapter   6 / 34

15K to 18K   out of 100K words

son yima cikar burina kutse. Na rantse
da ALLAH daya halicceni, koda cikin yankin ahalina ne bana
buƙatar numfashinsa Uwa!!”.
Dariya ta sake ƙyalƙyalewa da shi sai kuma ta gimtse fuska.
Kanta ta shiga girgiza mata da dukkan isa. “Ta-ƙurya wannan
karon akwai banbanci da koyaushe, dama na taɓa faɗa miki
bayan cikar nasararki ta farko akwai ƙalubale dana gani akan
cikar ta biyu, sai dai ba'a buɗe mun komaiba a wancan
lokacin, alamar haka na nuna ƙarfin taurarin mai yunƙurin,
amma a daren jiya dana tsananta bincike akan mafarkinki na
gano wani yanki da ƙyar. Ƴar shilar suda na ƙoƙarin yin cara
irin ta gawurtattun zakaru a kunnen bututu da taimakon wata
zuciya mai son kusantar tata.”
“A taimakeni a kawar mun dasu gaba ɗayansu Uwa. Ko a
bani damar kawar da su da kaina”.
“Hhhhhhh!!!! Ƙaddarar ƴar shilar bata mutuwa bace cikin
sauƙi. Tana kuma da ƙarfin taurarin da zata iya cin nasarar
dusashe naki”.
Bugawar da ƙirjinta yayi ta zata zuciyarta ce zata fito ta
bakinta dan tsabar razana. Ta kafeta da idanu cikin wani irin
yanayi mai wahalar fassara. Sai kuma tai saurin maida kanta
ƙasa ta rissinar tana faɗin, “A gafarceni Uwa”.
Wani irin kakkauran numfashi mai cike da gargaɗi
tsohuwar taja, cike da ƙasaita tana yamutse mummunar
fuskarta ta cigaba da faɗin, “Zamu iya samun mafita sai dai
akwai ruɗani a cikinta. Har zuwa yanzu kuma ban samu
buɗewar ruɗanin ba kai tsaye. Dan haka kina da zaɓi biyu.
Kodai ki ƙara yin duk yanda zakiyi igiya ta ƙullu tsakanin
Ajlaan da wannan ƴar shila muyi duk yanda zamuyi tazama
cikamakin aikinmu na biyu, ko kuma ki barta ta cimma
burinta.......”
Idanunta da suka kaɗa jajur tai ƙoƙarin ɗagowa, sai dai
ta maidasu da sauri zuwa ƙasa. “Uwa amma kin faɗamin na
cinye jarabawa ta biyu da zarar ya aura cika makin matansa
shine matakan nasarata, yanzu haka akwai su su biyu da suka
rage ɗauke da aurensa a kansu, zasu miƙasu garesa a karshen
watannin nan kamar yanda na samu tabbaci. Taya zamu
shigo da wata bayan aikin ya cika. A yanzu ya rage kawai
samun cikar burina na ƙarshe ne a kansa. Miye dalilin
shigowar wannan yarinyar abinda bai shafeta ba? Mizai hana
ai mata wani hukuncin daya dace da ita?...”
Hannu ta ɗaga mata cikin tarar numfashi da ƴar hasala-
hasala, da kakkausar murya tana mai nunata da ɗanyatsa
“Amma har yanzu ban sanar dake wadda ta dace ba, kuma
damun san cutarwace na umarninmu gareki bazamu ce ta
shigo ba”.
“Hakane Uwa, a gafarce ni. Sai dai Mahaifiyar Zak.......”.
Ta faɗa da alamun shiga tashin hankali mai girma, amma
kallon da Uwa ta watso amata ya hanata ƙarasawa.
Bata tanka mata ba, sai dai yanayinta ya nuna a hasale
take, dan cikin kaushin murya da zunzurutun jin zafi ta kaɗa
ƙahon hanunta mai kama da kwarkwaron gidan dodon koɗi.
A take haske ya gilma, sai ga farar takarda a hanunta. “Ƴar
shila burinta shine ɗaukar fansa, domin biyu a cikin masu
ɗakin Ajlaan da suka shuɗe jininta ne. Burinta shine bin kadin
jininsu ta hanyar bayyanama duniya ko kawar da shi.
Bayyanawar tata kafin cikar burinki faɗuwarki ne, a yanzu
haka kuma ta haɗu da mai taimaka matan harma sun gama
magana”.
Sosai zuciyarta ta ƙara harzuƙowa. Amma sai batace
komai ba saboda ganin Uwa a hasale take da ita. Cikin yin
ƙara ƙasa da kai tace, “Da ace bayan cikar burina ne kauɗi da
ƙudirin ɗaukar fansar wannan yarinya ya shigo haske ne ga
cikar burina. Dan zata ƙarasamin aikin ƙarshe da zanyi. Amma
tunda ta shigo a tsakkiyar labarina dolene ta fuskanci
hukuncin daya dace da ita. Idan ita bazata mutun ba shi a
kawar min da shi mana Uwa”.
“Hakan mai sauƙi ne, sai dai shima babu buƙatar
mutuwarsa, dan zai iya mana amfani a gaba. Sannan shi
rabata da shi shine mafi ƙololuwar hukuncinsa. Dan haka
daga nan zuwa safiyar kowace juma'a ta ƙarshen shekarar
nan ki tabbatar an zarga igiya tsakaninta da Ajlaan, a dakatar
da kai masa matan da suka rage a kaita garesa bayan tarewa,
dan da ita zamu cigaba da amfani har samuwar cikar burinmu
ga kowa!!.”
Da sauri ta ɗago kai jin muryar nayin nesa da ita, sai dai
kafin ta iya furta wani abu Uwa ta ɓace daga ɗakin tamkar
guntun girgijen hadari a tsakkiyar fararen gizagizai. Zumbur ta
miƙe tana mai dafe kanta dake sara mata, wani irin tuƙuƙi da
ƙaiƙayin mai zafafa ruhi zuciyarta ke mata. Sai dai sanin
wacece Uwa ya sata jin ɗan sassauci kaɗan, amma ruɗani mai
ɗauke da abubuwa masu matuƙar yawan gaske da fassarasu
a ɗauka shekara dubu bisa dubu ba'a kammala ba na neman
danne wancan ƙwarin gwiwar. Taya ruhin ƴaƴan sarakunan
ƙasar Ruman basu bata matsala ba sai ƴar talakawa
ƙasƙantattu? Dolene yarinyar nan ta ɗanɗana kuɗarta na
hukuncin shiga gonar daba tata ba ƙwarai da gaske, sai tayi
wasa da ita a tsakkiyar titi wasa irin na ɓera a hanun mage,
dan ko ita Malikat bata isaba.....

(Tofa masu karatu, ita kuma wannan wacece ita? Iffah fa
ta taro match ɗin da babu players. Kumuje zuwa dai muga
yaya wasan zai kaya🚴🏼...)

★__________________★

*_IFFAH_*

A ɗan firgice ta buɗe idanunta tare da tura hannu
ƙarƙashin filon data tada kai ta sake danne wayar dake faman
ɓurari cike da tsoron kar Ummu ta jiyo, dan tasan Babiy da
Hanash basa gidan. Ajiyar zuciya ta sauke mai matuƙar ƙarfi
da zaro wayar, cikin rawar jiki ta dannata a silent. Tamkar jira
kiran ya sake shigowa kuwa. Idanunta masu matuƙar girma
da haske ta waro sosai ganin mai kiran, ai batama bari tayi
ring na biyu ba taa ɗaga tare da kaiwa kunnenta tana direwa
a gadon.
“Kina jina?”.
Aka faɗa daga can. Kanta ta jinjina masa tamkar tana gabansa
dai-dai tana leƙawa tsakar gidansu. Daga can gefen da Babiy
ke kiwon tsuntsaye ta hango Ummu, dan haka ta sauke ajiyar
numfashi da fara magana cikin raɗa.
“Ina jinka Sir! Ta samu ne?”.
“Babu lokacin dogon magana Iffah, kiyi ƙoƙari daga nan zuwa
awa ɗaya ki sameni, dan kuwa mun tsinta dami a kala Ajmal
ya shigo Ruman, kuma a yanzu haka mun gama magana da
shi sai dai ban sanar masa ainahin zancen ba, ya kuma buƙaci
haɗuwa dake.....”
“Ya ALLAH! Alhmdllhi. Naji daɗi matuƙa wlhy Sir. Insha
ALLAHU duk yanda zanyi kuwa zan fito ka saurare ni”.
“Okay”.
Kawai ya faɗa yana mai yanke wayar. Itama shiri ta shiga
faman yi a gaggauce, tare da tattare takardun dukkan
bayanai data tattara waje ɗaya. Bakinta ɗauke da addu'ar
samun nasarar amincewar Ummu abisa ƙaryar data shirya
akan fitar ta fito. Daga inda Ummu take tako zubomata ido
na alamar tuhuma. Gareta ta ƙarasa cikin danne komai da
karsashin data aro. “Ummu kiran gaggawa na samu daga
Ikram. Inaga dai abinda muka jima muna jirane ya fito”.
“Amma Iffah....”
“Ummu dan ALLAH kar kice a'a”. Iffah tai saurin tarar
numfashinta cike da marairaicewa. “Ni ba hanaki zanyiba, sai
dai wannan yawan fitar taki a kwanakin nan bana zuwa
makaranta ba ya fara damuna Iffah. Shin kin manta halin da
muka shiga da wanda zamu iya shiga a yanzu? Ina jin tsoro
wlhy, matuƙar tsoro a duk sanda kika fita koda makaranta
ne”.
Sosai tausayin Ummu ya sake mamaye zuciyar Iffah, ta
haɗiye hawayen da suka taru mata a ido tana ƙaƙaro
murmushi. “Insha ALLAHU Ummu babu abinda zai faru,
wanda ya farun ma a baya bazamu taɓa mu yafe ba. Fita ta
kuma ta daina baki tsoro, tunda kinga duk sanda zan fitan ina
suturta dukkan jikina”.
“Shike nan ALLAH ya tsareki, dan ALLAH kiyi maza ki dawo
kafin Abbin ku ya dawo gidan nan ko ɗan uwanki”.
“Insha ALLAHU Ummuna”. Iffah ta faɗa tana rungumeta.
Shafa kanta Ummu tai tana murmushin ƙarfin hali itama, dan
ba wani zuciyarta ta samu nutsuwa bane ita dai, ta bartane
kawai saboda tace fitar ta shafi karatunta. Amma zata cigaba
da rakata da addu'a harta dawo.........✍
9


...........Kasancewar wajene daba kowa ke shiga ba anyhow
yasa sai da Iffah tai kiran Sir Fawzan bayan saukarta a bakin
gate. Umarnin bama security ɗin wajen wayar ya bata. Bayan
yayi magana da security ɗin suka bata damar shigewa batare
data san miya faɗa musu ba. Tafiya take a nutse tana ɗan
kallon wajen da tsarinsa. Dan babban garden ne mai cike da
ababen kallo da ni'imtattun korayen ciyayi da ƙawatatun
filawoyi. Ta taɓa shiga sau biyu a dalilin taron makarantarsu
ta Islamiyya da aka gudanar a wajen. Ya riga ya faɗa mata
inda zata samesa, dan haka kanta tsaye take nufar wajen
ranta fes da nishaɗi tamkar ance mata ga wuƙa ga maƙoshin
Tajwar Eshaan ta yanka.
Sai da taje kusan ƙarshen garden ɗin ta tsaya, sai kuma ta
shiga canki in canka na number wajen daya bata kasancewar
akwai rukuni-rukuni na ɓoyayyun wajen hutawa da manyan
mutane sukafi tu'ammali da su idan basa buƙatar wata
hayaniya. Cikin ɗan ɗage kafaɗa ta nufi na farkon da zuciyarta
tafi karkata. Ƙawatuwar wajen takai mai kallo shagala harya
iya manta abinda ya kawoshi, kamshin firanni da wani iska
mai busawa a hankali kaɗai na dabanne. Jitai kamar da
shakku na shigowarta wajen, amma sai ta dannesa a ƙasan
zuciya ta cigaba da takawa tamkar mai sanɗa tana leƙe-leƙe.
Ta isa kusan tsakkiya zuciyarta ta shiga gargaɗinta ganin babu
alamar akwai mutum mai numfashi a wajen, cak ta tsaya tare
da ciro wayarta domin neman sir Fawzan.
“Ya ALLAHU”.
Ta faɗa jin ana sanar mata bata da kati kona sisi a wayar.
Kamar zatai kuka ta sauketa daga kunenta tana ɗan ƙara
danne-danne da cigaba da takawa a hankali batare data san
mike a gabanta ba. Kaɗowar iska da sassanyan ƙamshin
turare mai daɗin gaske ya sakata tsayawa cak ƙirjinta na
harbawa da ƙarfi. Fararen idanunta ta janye daga kan wayar
tare da ɗago kanta gaba ɗaya, a kan mutumin dake kishingiɗe
bisa wani lallausan jan darduma daya haɗu da kalar korayen
ciyayi ya bada ƙyaƙyƙyawan tsari ta sauke. Rabin jikinsa akan
tum-tum yake. Kansa a risine yana kallon lap-top ƙirar
kamfanin apple dake akan wani ƙaramin tum-tum ɗin itama.
Gefensa kaɗan wani ƙyaƙyƙyawan bowl ne fari na tangaran,
sai butar shayi kalar golden akan tray dake tabbatar da set ne
dan harda ƙananun cups nashan shayi. Sanye yake da
ƙananun kaya farare tas da suka fidda ainahin suffarsa ta
masu ta'amalli da ƙarafuna, gashi sun sake fidda ainahin
hasken fatarsa da sheƙinta irin na masu jin daɗi. Duk da tana
a gab da shi aikinsa yake hankali kwance baiko nuna alamar
yasan da zuwanta ba.
“Mi kake buƙata?”.
Sassaanyar muryarsa mai zurfi da kamewa ta daki kunenta
da alamar akwai wanda yay tsammani ba ita ba. Ƙirjinta ne ya
sake harbawa har tanaji kamar jininta daya tsinke na neman
biyo hudojin gashin fatarta ya fito. Bata da niyyar cewa
komai, gata tsaye tamkar an dasata ta gagara ɗaga ko ƙafa
ɗaya tabar wajen duk da haka zuciyarta tafi buƙatar da tayi.
Jin shiru ba'a amsa masa ba, ga tsaiwar mutum yanaji har
yanzu a gabansa ya sashi ɗago lulu idanunsa masu haske da
baiwar bakin ƙwayar tsakkiyarsu ya sauke a kanta. Komai
tsayawa yay daga garesa, kamar yanda Iffah ma hatta
kaɗawar iskar wajen ta tsaya mata cak... Fuskarsa dake a
kame da kwarjini ya sake tsumewa yana sassauta girman
idanunsa tamkar mai son lumshesu da gayya.
A fisge, tamkar an jawo furucin daga bakin Iffah ta
yamutsa fuskarta da ƙanƙance manyan fararen idanunta da
tun a kallon farko ta kaudasu da ga kansa alamar kunya irin ta
mace, “Idan ma kai aljanine wlhy nafi ƙarfinka. Wace irin
jaraba ce duk inda nai saina ganka”. Ta ƙare maganar da hura
bakinta.
Kamar yanda bai motsa daga yanda yake ba haka bai ce
mata komai ba, bai kuma janye idanunsa a kanta ba har
yanzu. A zuciyar Iffah fa ta fara tsorata dajin tabbacin
mutumin nan fa ƙila aljani ne. Amma sai taga idan ta nuna
tsoronsa fa zai ma iya kasheta, saboda a yanzu haka ma
ƙarfin hali take, tana matuƙar jin kaifi da tasirin idanunsa a
dukkan ɓargon jikinta da jijiyoyi da gudanar jini. Amma sai ta
dake a ƙasan ranta tana karanto addu'ar neman tsari da
aljanu.
Kusan tunani iri ɗaya ne a zukatansu. Dan shima dai
zuciyarsa ta ƙara yarda wannan abar aljana ce kawai, yana
ganin kuma ya kamata yasan miyasa take bibiyarsa ne?.
Nisan data fara masa a idonsa ya fahimci tabar wajen, ilai
kuwa can ya hangota tana tafiya cikin sassarfa ta nufi ƙofa.
Cin karo data kusan yi da mutum ya sata ja gefe da sauri.
Ɗaya daga cikin matasan datai masa gani biyu da su ne, cikin
nuna alamar mamaki da tsuke fuska yake kallonta. Harara ta
balla masa ta ƙyaɓe fuska da raɓashi ta wuce, danji take
ƙafafunta tamkar ba'a kansu take takun ba.....
“Fareedah!”.
Da sauri ta juyo jin muryar Sir Fawzan daya sauke numfashi
da dafe kansa na tabbacin ya jima yana nemanta. “Ina kika
shigane wai? Tun ɗazun sai faman zagaye garden ɗin nan
nake ni da securitys nemanki, ga wayarki ma taƙi shiga sam”.
Maimakon ta bashi amsa sai ta zube a kujerar dake a kusa da
ita ragwaf. A wahale tace “Sir ka bani ruwa nasha Please”.
Sosai yanayinta ya sake neman firgitashi, amma fahimtar
ruwan tafi buƙata ba tambaya ba ya sashi barin wajen da ɗan
hanzari. Mintuna ƙalilan ya dawo da robar ruwa. Miƙa mata
yay bayan ya ɓalle murfin. Tunda ta kafa kai bata koja
numfashi ba sai da ta sha fin rabi, ta sauke robar tare da dafe
goshinta tana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Lokaci ya bata
sosai ta samu nutsuwa kafin ya kai zaune a kujerar dake
facing ɗinta.
“Fareedah miya faru wai? Ina kika shiga? Duk kin tadamin
hankali saboda security sun tabbatar min kin shigo”.
A hankali ta ɗago manyan idanunta da launin farinsu ya
sirka ta zuba masa. Sai kuma ta janye da sauri tana girgiza
kanta dan fuskar mutumin nan kawai ta gani a tare da shi
saboda ta sakama ranta aljani ne. Idanunta rumtse tare da
yakice tunanin ta sake buɗesu akansa. “Sir lokaci ya ƙure ina
abokin naka?”.
Ya fahimci bata son bashi amsa, sai kawai ya girgiza
mata kai. “Rashin ganinki ya sakani a ruɗanin da har ya kira
waya ban sani ba, sai daga baya na lura na kirashi shima
kuma bai ɗaga ba”.
“Ya ALLAH, shike nan itama wannan damar ta kufce min!”.
“Bazamuce haka ba sai munji ta bakinsa, a yau ne dai
kawai nake ganin bazai yuwu ba gaskiya, kodan ke a karan
kanki ma. Kinga saura baifi mintuna arba'in ayi magrib ba.
Kije gida, insha ALLAHU zanbi duk hanyar data dace domin
ganin kin haɗu da shi”.
Kallonsa take kamar zatai kuka. Sai dai saka zantukansa a
ma'aunin hankali ya sata kasa cewa komai.
“Kiyi haƙuri”.
Ya faɗa cikin sake sanyaya murya yana mata wani lallausan
kallo. Kauda nata idon tai daga kansa, taja iska ta fesar da
jinjina masa kanta kawai. Dan ta tabbatar inhar tai magana
kuka ne zai iya ƙwace mata ma.....


*_MASARAUTA_*

Gurfane take a gaban Uwa kamar yanda dokar take ga duk
wanda ke binta. Duk da matsayinta da girmanta a cikin daular
ruman a gaban uwa ita ba komai bace face mai neman biyan
buƙata (Wa'iyazubillah). Kamar ko yaushe tsohuwar da suke
kira uwa sanye take cikin jajayen kaya, sai dai saɓanin waccan
ranar yau inuwarta kawai ake iya gani a jikin bangon ɗakin.
Amma abin mamaki babu tsoro ko wata shakkar hakan a
idanun hamshaƙiyar matar. Inuwar uwa ta kece da mumunar
dariyarta mara daɗin saurare, kai kace za'a iya jinta a duk
faɗin masarautar, sai dai abin mamaki iya ita ɗin kawai take
jinta. Sai da tayi mai isarta kafin ta tsagaita tamkar ba'ita
tayin ba.
“Ta-ƙurya alƙawarina ya cika, zaku iya tunkarar kowa a
yanzu da maganar auren Ajlaan babu mai musa miki hatta
Malikat da shi a karan kansa balle duk wani mai faɗa masa
yaji. Sai dai akwai banbanci a wannan karon da baya.
Hhhhhhhh!!”.
“Umarninki shine abin jira Uwa mai share kukan mai
kuka”.
“Hhhhh Ta-ƙurya shiyyasa bana baƙin cikin taimakonki, zan
kuma cigaba da taimakonki kiyita na sara keda duk
mabiyanki. Ragamar kasancewar gida a hanun wasunki
bashine zai sa su zama masu ƙarfin ikoba sama da naki. Ki
shiga ki fita a haɗa gagarumin aure na bajinta tsakanin
wannan yarinya da Ajlaan. Hakan zaisa su shagaltu da
tunanin komai ya canja musamman shafe watanni tara da
Zawjata-almilki da suka rage suka kwashe gidan nan batare
da ko ciwon kai ba. Ina son ki nuna bajinta irin wadda ko
Malikat bazata yiba, Daular ruman zata cigaba da kasancewa
a tafin hanunki a baɗini koda a zahiri kinada wanda suke
nuna sunfi ƙarfinki. Ranar mako zata zama ranar sa'a
Hhhhhhhh!!!”.
Sautin dariyar ya cigaba da nesa da kunuwanta har inuwar
uwa ta ɓace. Nannauyan numfashi ta sauke tare da
murmushi mai nuna tsantsar farin ciki. Ta dubi ƙyaƙyƙyawan
farin tafin hanunta da jini keta kaikawo tana sake maimaita
kasantuwar daular ruman a tafin hanunta da uwa ta ambata
mata. Tabbas ita ɗin mai sa'a ce, sa'ar da zata iya nunata a
gaban duk wasu sa'ointa koma wanda suka ɗarata. Fatanta
kawai ALLAH ya kaita ranar cikar burinta gaba ɗaya domin
tabbatarma kowa dake cikin Ruman ma ba daular ruman
kawai ba *Saka ƙwan kaza bashi ke nufin mallakar akurki ita
ɗaya ba* sannan zuwan *mai guri bashi ke tabbatarda
naɗewar mai tabarma ba*.......

★★_______★
Kwanaki biyu kenan Iffah bata sake neman sir Fawzan
ɗinta ba, ta kuma kashe wayarta ta yanda shima koya nemeta
bazai sametan ba. Ita tasan dalilin zaɓar yin hakan, duk da
yanayinta ya nuna tana da damuwa dan babu walwala tattare
da ita sam tun baro garden ɗin da tayi. Yau ma data kasance
bazataje makaranta ba kamar yanda ta saba ta tashi taya
Ummu aiki, sai dai yanda take komai kamar mara laka a jiki
yasa Ummu nutsuwa a nazartar ta..
“Wai lafiyarki kuwa Iffah? Tun dawowar fitar da kikai
shekaran jiya duk kin wani canja. Ko jikin naki ne?”.
“A'a Ummu, kawai dai kaina na ɗan mun ciwo ne ƙasa-
ƙasa. Amma na san barci ne da bai isheni ba”.
“Barci kuma? To miya hanaki barcin?”.
In'ina ta fara na rashin sanin abinda zata faɗa. Sai kuma tai
ƙasa da kanta ganin yanda Ummu ta kafeta da idanu. Ummu
mace ce mai yawan tsantseni wajen tarbiyyar ƴaƴanta. Komai
tana binsa a sannu babu garaje ko gaggawar akan tafida
yaranta tun kafin sukai haka, shiyyasa cikin sauki take iya
sanin matsalolinsu da saurin fahimtar sabuwar hanya da suka
ɗauka saɓanin wadda ta sansu da shi.

6 / 34