Author : Bilyn Abdull ce Category : African Stories & Novels
cikinmu”.
Zantukan nasu ya saka zuciyar Iffah dinga tsalle-tsalle a
kan dalilai biyu.......✍️
28
........Na farko ji a ranta UBANGIJI ya amsa mata addu'ar ta
akan burin data shigo da shi Daular ruman. Na biyu minene
dalilin waɗan nan mutane na buɗe mata cikinsu?. Na ƙarshe
da yafi kowanne razani da ban mamaki a ƙwaƙwalwarta
dama suma sun san shike aikata kisan kenan? Amma suka
zaɓi yin shiru saboda ba ƴaƴansu ake halakawa ba kokuwa
suma tsoronsa sukeji? A ɗan ƙaramin tunaninta tanaga zasu
iya yin amfani da ƙwanji wajen sanin mi Shahan-shan ɗin ke
aikatawa musamman Malikat Haseena da Malikat Bushirat.
Amma miyasa suka zaɓi yin amfani da ita? Kodai sun gama
gane manufarta ne a kansa.....?
“Ibnati!”.
Daneen Ammarah ta katseta daga nisan da tai a tunani ta
hanyar kiran sunanta da taɓata. Firgigit kuwa ta kawo ajiyar
zuciya. “Karki kasance a dogon nazari, manufarmu ta sakaki a
wannan sabgar tana da nasaba ne da dalilai biyu. Na farko
juriyarki ta bamu ƙwarin gwiwar kallonki a jaruma. Na biyu
jinki wata abu mai muhimmanci da muke fatan nasara ta
dalilinta kodan tsallake tarkon masu aikata wannan ɓarna da
kika tsallake a harin farko da muke jin shine lagon da aka
dinga ɗanawa a farko wajen salwantar da rayukan da suka
gabata....”
“Mamy nima zata yuwu bana tsallake bane dan nafi
ƙarfinsu, maybe na tsallake ne saboda tsayawarku da fatanku
akan ganin na tsallake ɗin. Amma tabbas zan iya sadaukarwa,
zan kuma iya bin umarninku badan inajin ƙarfina ya kai ba sai
dan kun isa ku bani umarni”.
Su dukansu kalamanta sunyi wani tasiri na musamman
a zukatansu tare da ƙawatata a cikin idanunsu. A wani gefen
sunyi amanna irinta ɗansu ya dace ya samu tun farko, dan
ƙarfin gwiwarta sunyi dai-dai da Zawjata-almilk da akafi
buƙata ga kowane Shahan-shan. Sannan Malikat da sukema
kansu fata.
“ALLAH yay miki albarka”.
Suka faɗa kusan a tare su duka huɗun. A kan laɓɓanta ta
amsa da amin.
Sun cigaba da tattaunawar da gaba ɗaya ta saka Iffah cikin
ƙagara, ƙagara mai nasaba da shiga ruɗanin wani furici daga
Daneen Ammarah. Wai jiya Shahan-shan ne wanda ya
ziyarcesu a wannan falon, tana buƙatar samun filin tunani
dan zuciyarta da ƙwaƙwalwarta fa gaba ɗaya sun kulle, ruɗani
ya gama mamaye duk wani hangenta da dama bai wuce iya
tsayin ƙafafunta da shekarunta ba....
★★....
A hankali ta maida ƙofar ta rufe tare da jingina a jikinta ta
lumshe ido da sauke numfashi tamkar mai kokawar jawosa.
Shin murna zatayi a wannan gaɓar ko kuwa shiga ruɗani?.
Idan ance Shahan-shan ne a jiya ta yarda, shi kuma wanda tai
gamo da shi a mabanbanta wajeje kafin shigowarta
masarauta wanene shi?. Wannan tambaya tafi kowace
tambaya girma da girgiza zuciyarta a duk abubuwan dake cin
ranta. “Kai nifa nama ruɗe wlhy”.
Ta faɗa a zahiri tana zamewa cikin sarewa ta zube ƙasa. Ta
jima a wajen cikin halin shiru da ambaton hasbinallahu wa
ni'imal wakil ko zata samu dai-daiton komawa cikin hankali
dan da gaske komai na halittarta mai motsi ya raunana da
rauni mafi ban tsoro da shiga ruɗani. Tsahon lokaci ta kwashe
a wajen tana kokawa da raunin zuciyarta da rashin ƙarfin
gudanar jini. Fahimtar wancan tunanin na buƙatar lokaci ya
sata turesa ta maida hankali akan tattaunawarsu da su
Malikat. Tabbas wannan shine babban ƙudirinta dayin
ƙundunbalar juriya na tunkarar rayuwar da bata da tabbacin
tsallakewa. Duk da tasan anfi ƙarfinta, dama duk wani mai
ƙarfi da take kallon ƙarfinta ta zaɓi fuskantar mutum mafi
girman iko da tsaro domin ɗaukar fansa. A kwanakin da suka
gabata na kasancewarta cikin wannan daula ta fara fidda ran
samun cikar burinta saboda dalilai masu yawa. Ciki harda
rashin samun koda ƙanƙanuwar ƙofar sanin minene ma
daular ruman ɗin ta ƙunsa balle Shahan-shan da kansa. Sai
gashi a yau cikin sauƙi an buƙaci kaita inda zuciyarta ta fara
raya mata zuwansa ba ƙaramin tsalle bane da ba'a da
tabbacin fita idan an shiga, aka kuma sanar mata wani yanki
na sirrin daular ruman mai girman gaske da ko na ciki basu
san da shi ba ƙila. “Anya babu wani abu a ran mutanen nan
saɓanin abinda suka faɗa?” bakinta ya furta a zahiri cikin sake
dulmiya a ruɗani. (Koda akwaisa yardar ki dasu ce zata baki
ilimin sanin hakan) zuciyarta ta faɗa cikin ƙarfafata da ture
raunin dake neman rinjayarta....
Knoking ƙofar daya wanzu a dai-dai lokacin ya sata jan
numfashi a sauƙaƙe. Da ƙyar ta iya miƙewa daga zaman
daɓaron da tayi ta buɗe. Daneen Ammarah ta sakar mata
murmushi. Cikin yaƙe ta mayar mata da murtani da matsawa
ta bata hanya. Rissinawa hadimar da suke tare tai ta gaisheta,
hannu kawai ta ɗaga mata alamar amsawa tana bin ledar
hanunta da kallo......
★★.... ★.... ★★.....
Kamar yanda aka sanar da Barrister kai tsaye station ɗin da
akace su Babiy suke suka nufa. Kasancewarsa babba kuma
sananne basusha wahalar ganin ogan station ɗin ba kai tsaye.
Sunyi gaisuwa irin tasu ta manyan ma'aikata, su kai kuma
gaisuwar girmama juna da su Kaka.
Barrister ya gabatar da kansa, ya kuma gabatar da abinda
suke tafe da shi harda hoton su Babiy domin sauƙaƙawa.
Jami'in yay shiru yana kallon hotunan kamar mai hasashe, sai
kuma ya ɗago ya kalla Barrister “Gaskiya banajin akwai
waɗan nan mutanen a wannan station ɗin Barrister”.
Barrister daya fahimci matsala ce ke neman shigowa yay
ɗan murmushi da muskuta zamansa. “Yallaɓai adai sake
dubawa, zata iya yuwuwa ko akwaisu ɗin baka da labarin
hakan. Amma tabbas suna a wannan station ɗin. A matsayina
na Barrister ba nazo nan dan a bani belinsu bane ba, duk da
nasan basu da hannu a abinda ake zarginsu. Nazo ne dan na
gana da su, sannan a miƙasu kotu saboda nasan dai ita matar
data saka aka kawosu nan burinta a kwatar mata hakkin
mijinta”.
“Iya gaskiyata nake faɗa maka Barrister babu waɗan nan
mutanen a wannan station ɗin. Amma mizai hana ku sami ita
matar na tabbata tunda tare da ita akaje tasan wane station
ne”.
Barrister yay shiru yana kallonsa cike da nazari. Hakama
Kaka da Abu Zainab. Kusan minti biyu shiru babu wanda ya
motsa, kafin Barrister ya miƙe yana ɗan murmushi ya bashi
hannu. Suma su Abu Zainab miƙewar sukai...
Da kallo ya bisu har suka gama ficewa, ya kai hannu kan
wayarsa dake saman desk ɗin sa yana wani murmushi. A
bugu biyu aka ɗauka wayar daya kira. Sallama kawai yay da
faɗin, “Kamar yanda kai hasashe ranka ya daɗe yanzu suka
bar office ɗina”.
Shiru yana sauraren mi'ake faɗa daga can, sai kuma yay
murmushi da amsawa da “Angama ranka ya daɗe”. Daga
haka ya ajiye wayar yana wata ƴar iskar dariya...
Abu Zainab daya kasa fahimtar komai saɓanin Kaka da
Barrister dake hangen wani abu dalilin kashedi da akai musu
kafin zuwansu nan dama ya katse shirun da motar ta ɗauka ta
hanyar nisawa. “Anya kuwa wannan jami'in akwai gaskiya a
maganarsa Barrister. Kagafa yanda yake ƙyaf-ƙyaf da idanu
kamar tsohon ɗan jari hujja. Nifa wannan al'amari ya fara
bani tsoro wlhy”.
Barrister da zuciyarsa ke kai kawo ya fesar da huci,
“Kana tunanin yaƙi faɗa mana gaskiya ne Zakariyya?”.
“Fuskarsa ta nuna hakan ai Barrister, ko kuwa Kaka?”.
Kaka da shima dai yake aune-aunensa a rai ya girgiza kansa.
“Zata iya yuwuwa gaskiyar ya faɗa, sai dai kumin wani
taimako ɗaya dazai warware mana gaskiyar tasa ko
saɓaninta, bayan nan zan sanar muku abinda ya faru kafin
zuwanmu nan”.
Barrister da shima abinda ke'a ransa kenan ya ɗan juyo
ya kalla kaka ta madubi, “Muna jinka Baba”.
“Muyi gaggawar isa gidan Dawood”.
“Shawara mai ƙyau Baba”.
Barrister ya faɗa yana juya motar hanyar da zata kaisa gidan
Abu Moosa.
★★... ★★... ★★...
“Mamy kuma duka wayar da lap-top ɗinne nawa?”.
Iffah ta faɗa da mamaki. Murmushi Daneen Ammarah tayi,
“Ibnati wannan ai ba komai bane ba, sannan ko baki faɗa ba
kina buƙatar su tare da ke kodan ki dinga jin motsin gida. Na
biyu kuma wannan aikin da zaki fara kowa yasan mai haɗari
ne, dolene ki kasance da waya a duk inda kike a masarautar
nan. Da zarar Kinga abinda zuciyarki bata kwanta da shi ba a
cikin mu huɗun zaki iya kiran kowa ki sanar masa. Lap-top
kuwa ni naga ya dace na kawo miki ita domin ɗebe kewa.
Amma kiyi taka tsantsan ki kuma kula sosai, dan samun
waɗan nan na nufin zaki iya mu'amula da kowa musamman a
yanar gizo batare da kin samu tabbacin wanene ɗin ba”.
“Haka ne Mamy, insha ALLAH zan kiyaye. Nagode sosai
ALLAH ya saka da alkairi”.
“Karki damu kin cancanta ne ai”.
★Iffah ta daka tsallen murna bayan ficewar Daneen
Ammarah, harda ƴar rawarta. Duk wani tunani da kaikawon
da zuciyarta ke mata akan Shahan-shan zuwan wannan waya
da lap-top ya kauda mata shi. Domin a ganinta dama biyu ce
tazo mata a lokaci guda kuma zata damata ta yanda dole sai
Shahan-shan ya shata. Yanzu dai abu na farko da zata fara
shine malam Fawzan. Ta tura masa saƙo bayan nemansa da
tai shi da abokinsa wayar Arfa dake hanunta ta mutu ba caji,
tana buƙatar tasan ko yaga saƙon? Ya kuma iyayenta suke?.
Samun wayar da caji yasa tun a daren ta haɗata, duk da
taga akwai sim card batai amfani da shi ba ta cire na Arfa ta
sanya. Tamkar jira saƙon Malam Fawzan ne ya fara shigowa,
jikinta har tsuma yake wajen buɗewa. Batako kai ƙarshen
karantawa ba kira ya shigo. Gabanta ne ya faɗi ganin
baƙuwar lamba, amma tsabar ƙarfin hali sai ta ɗaga.
“Sir!”.
Ta faɗa cikin gwalalo idanu da nufar ƙofa da sauri ta saka
key. Daga can aka amsa mata da “Na'am Fareedah. Ina kika
shiga haka? Tun bayan ganin saƙonki na kasa samunki, har
zuciyata ta karaya da ko wani ya gano ki ne?”.
“Babu wanda ya gano ni Sir, akasi aka samu wayar ta
mutu, na kuma rasa ta yanda zanyi cajinta dan na manta da
cajan a gida”.
“Ayya. Kin ganni akoda yaushe cikin gwada wayarki nake
koza'a dace. Saboda ke na samar da wannan layin na sirri.
Yanzu ma gwadawa kawai nake amma banyi tunanin samunki
ba sam”.
Iffah ta share hawayen da suka silalo mata tana ɗan
murmushi. “Nagode Sir, koda banyi nasara ba bazan taɓa
mantawa da kai ba. Ina fatan ka bincika min su Ummu. Dan
sam na kasa samun kwanciyar hankali na rashin jin su”.
Ɗan jimm yay kamar mai tattaro abin faɗa, sai kuma yay
ɗan murmushin basarwa. “Suna lafiya dan har gida naje, sai
dai ban samu shiga ba kasancewar suna tare da tsaron
dakarun masarautar har yanzu. Amma nayi ƙoƙari mun haɗu
da Hanash....”
“Amma miyasa wayoyinsu basayi?”.
Ta katsesa a ƙagauce. Da ƙyar ya iya tattaro abin faɗa a
wannan gaɓar ma. “Shi Babiy wayarsa ta samu matsala ne.
Hanash kuwa network ne dan yace min shima yasha nemanki
amma baya samunki”.
“Bani da lafiya ne, ba koyaushe kuma wayar ke kunne ba.
Amma yanzu zan sake nemansa insha ALLAHU dan ina
matuƙar bukatar son naji muryoyinsu kozan samu nutsuwa”.
“Hakan yana da ƙyau. ALLAH kuma ya ƙara lafiya. Kinyi
waya da abokina kuwa?”..
“Eh nayi, amma kamar yanda na sanar maka a text message
an ɗaga amma ana mun wani shirmen banza. Daga ƙarshe ma
akace wai na saɓa lamba”.
Karan farko malam Fawzan yay ƴar dariya. “Taku ne
kawai irin na masu iyawa. Amma a yanzu na tabbatar zai
saurareki”.
Iffah ta ɗan taɓe baki kamar tana gabansa. “Ni ALLAH
harna ɗauka ko ka yaudareni ne ka bani number daba itaba
ma”.
“Iffah koda abin wasa kikazo da shi bazan masa riƙon
banza ba balle wannan mai matuƙar muhimmanci da ma'ana.
Yanzu dai ina fatan wayar taki akwai caji?”.
“Ai bama waccan bace, sabuwa fil aka bani a kwali yau
harda lap-top”.
Jimm yay na wasu ƴan sakkani. Sai kuma ya cire wayar a
kunnensa ya duba. Tuna ashema shine ya kirata ya sashi sake
maidawa. “Amma baƙya zargin akwai wani dalili a baki
wayar? Mutanen nan fa sunada haɗari sosai Iffah. Bazan
ɓoye miki ba inajin tsoron ƙarfin ikonsu”.
“Nice zan baka wannan labarin Sir kasancewata a cikinsu
yanzu. Sai dai kuma wanda suka bani wayar yanki ne na
mutanen kirkin cikinsu. Kasan a ko ina akwai ƙyakykyawa
akwai kuma mummuna”. Tsaf ta kwashe yanda sukai ta sanar
masa saboda ta matuƙar yarda da shi. Shine kuma takema
kallon wanda zai taimaka mata a wannan yaƙin kamar yanda
tai fata. Ya jimanta al'amarin matuƙa, ta wata fuskar kuma
yayi murnar ganin hanyar samun nasararsu ce tazo.
“Lallai mun samu hanya ta jifan tsuntsu biyu da dutse
ɗaya Iffah. Sai dai dole kiyi taka tsantsan da waɗan nan
wayoyin. Ki buɗe account da duk kike ɓuƙata da layin da suka
sanya miki, shi kuma wannan nakin watsap kawai zaki buɗe
da shi, sai dai karki barsa akan wayar, da kuma kinyi magana
da Ajmaal da shi ki goge watsap ɗin ki cire layin sai zaku ƙara
ki maida. Akoda yaushe wayarki ta kasance da security na
idanunki bana wayar ba. Dan inada tabbacin suma zasu saka
ido a kanki. A daren nan ki buɗe watsap ɗin ki sake ma
Ajmaal magana”.
“Nahode Sir, insha ALLAHU zan yi duk yanda kace”.........✍️
29
.........Barrister na ƙoƙarin shiga layin gidan Abu Moosa wata
baƙar mota na ficewa. Babu wanda ya damu da ganinta a
cikinsu, suka ƙarasa kutsa kai har ƙofar gidansa. Ganin gidan
rufe daga nesa baisa sun kawo wani abu a ransu ba duk suka
fita. Abu Zainab ne ya ƙarasa har jikin ƙofar. Kansa tsaye ya
kai hannu ya fara knoking, amma har tsahon mintuna biyu
babu alamar motsin mutum.
Juyowa yay ya ɗan kalli su Kaka dake kallonsa. Cikin
sarewa ya girgiza musu kai. “Banajin fa akwai mutum a gidan
nan, dan babu wani motsi”.
“Kara dai bugawa”.
Cewar Barrister cikin bashi ƙwarin gwiwa. Kai Abu Zainab ya
kaɗa ya cigaba da bugawa, maimakon a buɗe nan sai ƙofar
makwaftansu ce ta buɗe. Wani matashin saurayi ya fito. Abu
Zainab ya maida hankalinsa garesa suka gaisa. Kafinma ya
tambaya saurayin ya bashi amsa.
“Ai banajin akwai kowa gidan nan. Saboda yanzu babu
jimawa matar gidan aka ɗauke a mota harda ƙaton akwati”.
Da mamaki Abu Zainab ya ce, “Kana nufin yanzun?”.
“Eh, dan banajin sunma rufa minti goma. Ta kuma yima
mahaifiyata sallama akan zata koma garinsu ne. Harma
mukayi mamakin hakan ganin duka rasuwar mijinta bai wuce
kwanaki goma sha biyar ba”.
Godiya Abu Zainab yay masa jiki a saɓule ya koma gasu
Kaka. “Waifa kunji babu jimawa tabar anguwar nan. A yanda
tacema makwaftansu ma ta koma garinsu ne”.
“Garinsu kuma?”.
“Haka dai yace. Nifa na fara tsorata da lamarin nan, dan
tabbas akwai abinda ke ɓoye da bamu sanshi ba”.
Tsakanin Kaka da Barrister babu wanda ya iya cewa
komai....
*_MASARAUTA (JASRAH)_*
“Wai ni naga sai faman moso kike, kinma kasa bani labarin
yanda kukai da Akia akan zancenmu na jiya. Kuma naga
wucewarku ke da ita ɗazun zuwa sashin Mamma (Malikat
Haseena)”.
Cike da zolaya ta ɗan hararesa. “Ko kuma dai ƴan leƙen
asirinku sun sanar maka ba”.
“Leƙen asiri kuma? Haba sai kace dai ku. Kudai matan
masarautar nan ne dai da baƙwa iya rayuwa sai dai ƴan leƙen
asiri. Amma mu maza miya haɗamu da wani leƙen asiri kamar
marasa aikin yi”.
Ta ɗan dara kaɗan da taɓe baki. “Muma ɗin ba kowa ne
yake hakan ba kamar yanda kuke zargi. Niko waya dameni a
daular nan dahar zan damu da saka wani bibiyarsa. Ko
lamarin Zaki addu'a ce tamu a garesa kawai”.
“To ALLAH yasa hakan. Yaya zaman naku ya kasance?”.
“Zama an samu nasara. Dan inama Akia bayani a take ta
amince, ta kumace muje sashen Mamma itama muji ta
bakinta. Alhamdullah sai aka dace itama zancen ya ƙayatar da
ita. Na taƙaice maka zance a yanzu haka ma mun zauna da ita
yarinyar. Insha ALLAHU zuwa gobe ma zata koma sashenta.
Sai dai abu ɗaya ne fa Mamma bata amince da shi ba”.
“Minene shi?”.
“Sake kai wata Zawjata-almilk turakarsa. Acewarta za'a ƙara
jinkirtawa aga abinda yarinyar zata samo. Sannan za'a
sakema duka Zawjata-almilk ɗin sabon horo akan kasancewar
su Zawjata-almilk a wannan karon”.
(Wata sabuwa kenan, wannan tsinanniyar tsohuwar ko)
ya ambata a zuciyarsa. A fili kam fuskarsa ya kawata da sabon
murmushi da faɗin, “Woow wannan tsarin yayi, shiyyasa
Mamma ke daɗa birgeni. Hakan ma wani mataki ne da zai
taimakemu matuƙa. ALLAH kuma yasa mu dace”.
“Amin dai Abu Harith. Dan gaskiya a wannan gaɓar ina
tsoron a ce abinda ya faru ya sake maimaita kansa. Saboda
zuwa yanzu hankalin manyan ƙasashen duniya ya fara
dawowa kan ƙasar ruman. Dan ma ana shakkarmu ne da tuni
wani zancen ake ba wannan ɗin ba. ALLAH dai ka bayyana
gaskiya ka kuma wanke wanda ake neman disashewa saboda
son zuciya”.
“Amin Meera. Amma ko yanzu ɗin ma akwai abinda
baku sani ba. Shahan-shan na ɓoyewa ne kawai dan karya
tashi hankalin kowa. A wata mai kamawa shugabannin
manyan ƙasashe bakwai na africa zasu kawo ziyara ƙasar
ruman. Bisa jagorancin shugaban ƙasar Nijeriya, bama raba
ɗayan biyu akan wannan al'amarin ne kuma”.
“Ya Arrahaman”.
Jasrah ta faɗa a tsorace.
“Ki kwantar da hankalinki, dan ALLAH kuma kar kowa yasan
wannan, dan na sanar miki ne kema saboda na yarda da ke”.
Badan hankalin nata ya kwanta ba ta jin jina masa
kanta kawai. Cigaba da kwantar mata da hankali yay cikin
kwantar da murya har barci ɓarawo ya kwashe ta. Sai da ya
tabbatar barcinta yayi nisa sannan ya zare jikinsa cikin sanɗa
ya fice zuwa ɗayan ɗakin dake jikin wanda suke kwance da
waya a hannunsa......
*_ZAWJATA-ALMILK_*
Dukan matakin shawarar da Sir Fawzan ya bata shi tabi, dan
tunda sukai bankwana da Daneen Ammarah tai shirin barci ta
sakama ƙofarta key. Ta fara da buɗe Watsap, sannan ta
lalubo number Ajmaal. Cikin sa'a kuwa yana online, wani
farin ciki ne ya ratsata. Taja kakkauran numfashi da godema
ALLAH.
_Assalamu alaikum_
Ta fara turawa da fatan samun amsa zuciyarta na harbawa
da sauri-sauri. Tsahon mintuna kusan goma babu alamar
zama a buɗe saƙon. Sake tura sallamar tayi a karo na biyu. Ta
dasama wayar ido kamar mai irgan fitan numfashinta. Kamar
a mafarki taga an buɗe, tai kasare tana jiran taga an amsa sai
dai shiru har kusan